29/10/2025
Ziyarar Duba Ayyukan Magudanen Ruwa Waɗanda Shugaban Karamar Hukumar Malumfashi Hon. Mukhtar Abdullahi City, Yake Gudanarwa
Kwamitin duba ayyuka da tabbatar da ingancinsu a karamar hukumar Malumfashi, karkashin jagorancin Shugaban Kwamitin kuma Supervisory Councilor na Ma’aikatar Ayyuka, Hon. Abdullahi Yahaya Karfi, ya kai ziyarar duba ayyuka a wasu sassa na karamar hukumar a ranar Talata, 28 ga Oktoba, 2025.
wuraren da aka ziyarta sun haɗa da Gangarawa Gandu, Unguwar Mata, da kuma Agagiwa, inda ake aiwatar da ayyukan magudanan ruwa domin sauƙaƙa wa al’umma.
A yayin ziyarar, Hon. Abdullahi Yahaya Karfi ya yaba da yadda ‘yan kwangila s**a nuna jajircewa da himma wajen aiwatar da ayyukan da aka basu. Ya kuma yi kira ga sauran ‘yan kwangila da su gaggauta komawa wuraren ayyukan da aka basu domin tabbatar da ci gaban aikin da aka basu.
Ya ƙara da cewa, kwamitin zai ci gaba da bin diddigin ayyukan domin tabbatar da an yi su cikin nagarta da inganci, kamar yadda Mai Girma Shugaban Karamar Hukumar Malumfashi, Hon. Alhaji Mukhtar Abdullahi City, ya umarta.
“Zamu tsaya tsayin daka wajen ganin an yi aiki mai inganci. Duk wani ɗan kwangila da ya yi aiki mara kyau zai fuskanci hukuncin gwamnati,” in ji Hon. Abdullahi Yahaya Karfi.
Kwamitin ya bayyana cewa ziyarar duba ayyuka za ta kasance ta kai-tsaye daga farkon fara aiki har zuwa ƙarshe, ba tare da sanarwa ga ‘yan kwangila kafin zuwan kwamitin ba, domin tabbatar da gaskiya da inganci a duk matakin aiwatar da ayyuka.
Buhari Lawal Mlf.
SSA to the Executive Chairman Malumfashi Local Government.
29/10/2025.