21/02/2025
Shugaban Hukumar Hisbah ta Jihar Katsina ya sanar da haramta dukkan gidajen rawar dare (Night Clubs) a faɗin jihar, yana mai cewa an ɗauki wannan mataki ne domin kare tarbiyya da kyawawan dabi’u a cikin al’umma.
A cewar shugaban Hisbah, wannan dokar ta zo ne sakamakon yawaitar rahotannin dake nuna yadda gidajen rawar dare ke zama matsala ga matasa, tare da haifar da munanan dabi’u kamar shaye-shaye, fasadi, da aikata miyagun laifuka.
“Mun haramta yin rawar dare gaba ɗaya a Jihar Katsina, kuma ba za mu lamunci duk wani abu da zai lalata tarbiyyar jama’a ba,” in ji shugaban Hisbah.
Ya ƙara da cewa hukumar za ta yi aiki tare da sauran hukumomin tsaro don tabbatar da cewa wannan umarni ya kasance, tare da hukunta duk wanda ya saba wannan doka. Wannan mataki ya nuna ƙudurinsu na ceto al’umma daga abubuwan da ke barazana ga kyawawan dabi’u da zaman lafiya.