Sen. Muntari Dandutse Media Reporters

Sen. Muntari Dandutse Media Reporters Chairman Senate Committee on Tertiary
Institutions and TetFund | Senator
representing Katsina South Senatorial
District, Katsina State.

Sanatan shiyar Funtua na cigaba da Samun Goyon Bayan Al'umma Kungiyoyin masu sana'ar hannu na 'yan asalin shiyyar Funtua...
26/06/2026

Sanatan shiyar Funtua na cigaba da Samun Goyon Bayan Al'umma

Kungiyoyin masu sana'ar hannu na 'yan asalin shiyyar Funtua mazauna Abuja sun bayyana cikakken goyon bayansu ga Sanatan Katsina ta Kudu, Muntari Mohammed Dandutse, tare da yabawa irin gudunmawar da yake ci gaba da bayarwa wajen tallafawa al'umma.

An bayyana hakan ne yayin wani taro da wakilan kungiyoyin s**a gudanar tare da wakilin Sanatan, Malam Tasi'u Begon, wanda ya wakilce shi a wajen zaman.

Da yake jawabi a madadin kungiyoyin, Alhaji Sirajo Kankara, ya ce suna matuƙar jin daɗin yadda Sanata Dandutse ke kula da mambobinsu, musamman a lokutan da suke fuskantar ƙalubale kamar rashin lafiya da haɗurran ababen hawa.

Ya ƙara da cewa Sanatan ya kasance mai tausayi da taimakon al'ummar shiyyar Funtua ba tare da nuna bambanci ba, abin da ya sa kungiyoyin s**a yanke shawarar fitowa fili domin bayyana goyon bayansu da kuma nuna godiyarsu gare shi.

A nasa jawabin, Malam Tasi'u Begon ya miƙa godiyar Sanatan ga shugabanni da mambobin kungiyoyin bisa irin amincewa da goyon bayan da s**a nuna masa.

Ya bayyana cewa Sanata Dandutse na ɗaukar dukkan al'ummar shiyyar Funtua a matsayin iyalansa, kuma zai ci gaba da tallafawa jama'a tare da aiwatar da ayyukan ci gaba da za su inganta rayuwar al'umma ba tare da nuna bambanci ba.

A ƙarshe, ya yi kira ga mambobin kungiyoyin da su ci gaba da kasancewa cikin haɗin kai, zaman lafiya da kuma bayar da gudunmawa wajen bunƙasa ci gaban shiyyar Funtua da Jihar Katsina baki ɗaya.

Dandutse Media Reporter

CIKAKKEN RAHOTON AIKIN SHEKARU UKU NA SANATA MUNTARI DANDUTSE,_____DANDUTSE YA BAR TARIHI A KATSINA TA KUDU.A cikin shek...
26/06/2026

CIKAKKEN RAHOTON AIKIN SHEKARU UKU NA SANATA MUNTARI DANDUTSE,

_____DANDUTSE YA BAR TARIHI A KATSINA TA KUDU.

A cikin shekaru uku da s**a gabata, al'ummar Mazabar Katsina ta Kudu sun shaida gagarumin sauyi a fannoni daban-daban karkashin jagorancin Sanata Muntari Mohammed Dandutse, mai wakiltarsu a Majalisar Dattawan Tarayyar Najeriya.

Tun bayan hawansa kujerar wakilci, Sanata Dandutse ya mayar da hankali wajen inganta rayuwar jama'a ta hanyar samar da tsaro, ayyukan more rayuwa, ƙarfafa matasa da mata, tallafin jinƙai, samar da ayyukan yi da kuma gabatar da muhimman kudurori da s**a shafi ci gaban yankin.

ƁANGAREN TSARO DA MAIDO DA ZAMAN LAFIYA.

Da yake yankin Katsina ta Kudu na daga cikin wuraren da s**a fuskanci matsalar rashin tsaro, Sanata Dandutse ya nuna jajircewa ta musamman wajen amfani da damar da yake da ita a Majalisar Dattawa domin kare rayuka da dukiyoyin al'umma.

(1) A zauren Majalisar Dattawa, Sanatan ya yi amfani da Dokar Tsari ta 42 (Order 42) domin jawo hankalin majalisa kan tabarbarewar matsalar tsaro a yankin tare da neman daukar matakan gaggawa.

(2) Haka kuma, ya gabatar da muhimman kudurori da dama domin matsa lamba ga gwamnati da hukumomin tsaro su kara kaimi wajen dakile ayyukan 'yan bindiga da sauran masu aikata laifuka.

(B) Sakamakon wadannan kudurori:

(1) An kara tura jami'an tsaro zuwa yankunan da ke fama da hare-hare.

(2) An samar da kayan tallafi ga al'ummomin da matsalar tsaro ta shafa.

(3) An samu ingantaccen hadin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro, sarakunan gargajiya da shugabannin al'umma.

(4) An samu raguwar hare-hare a wasu yankuna tare da dawo da kwarin gwiwa ga jama'a.

TALLAFI DA ƘARFAFA TATTALIN ARZIKIN AL'UMMA.

A bangaren tallafawa jama'a da bunkasa tattalin arziki, Sanata Dandutse ya aiwatar da shirye-shirye masu dimbin tasiri.

Tallafin Kai Tsaye:-

(1) An raba babura guda 117 ga shugabannin rumfunan jam'iyyar APC.

(2) Ya baiwa Mata 248 injinan niƙa.

(3) Ya baiwa Mata 539 keken ɗinki. Domin su taimaka mazajensu

(4) Ya bayar da tallafin Naira Miliyan 10 ga Ƙungiyar Daliban Jihar Katsina ta Jami'ar Ahmadu Bello domin kafa cibiyar kasuwanci.

(4) Ya bayar da Naira Miliyan 2 ga Ƙungiyar ALLOPN.

(6) Ya raba na'urorin hasken rana guda 300 ga masallatai da makarantun Tsangaya.

(7) Yayi Shirye-shiryen Samar da Sana'o'i
Matasa 400 sun samu horo kan harkar POS tare da jari na Naira 50,000 ga kowane mutum.

(8) Ya horos Da Matasa 300 sun samu horo da jari kan kiwon kifi.
Matasa 100 sun samu horo kan sarrafa fata da takalma tare da jari.

(9) Ya Sanya fitilun tituna masu amfani da hasken rana akalla guda 50 a kowace ƙaramar hukuma 11 da ke shiyyar Funtua domin inganta tsaro da harkokin kasuwanci.

MANYAN AYYUKAN MORE RAYUWA:-

A bangaren ayyukan raya kasa kuwa, Sanata Dandutse ya aiwatar da muhimman ayyuka da dama.

(A) Ayyukan Da Aka Kammala:-

(1) Ya Gina rijiyoyin burtsatse guda uku a Gundumar Garagi ta Kankara.

(2) Ya Sayi fili, anyi katanga da rijiyar burtsatse ga Makarantar Maijalalaini da ke Malumfashi.

(3) Ya Gina cibiyar koyon sana'o'i a Musawa.

(4) Ya Gina dakin karatu na al'umma a Malumfashi.

(5) Ya Gina sabon Hedikwatar Area Command ta zamani a Malumfashi.

(6) Ya Katange Hedikwatar 'Yan Sanda a Funtua.

(7) Ya Gyara ofishin 'yan sanda na Kankara.

(8) Ya Kammala mataki na farko na Madatsar Ruwan Bakori.

(9) Ya Gina ajujuwa a Matazu da Danja.

(B) Ayyukan Da Ake Gudanarwa yanzu, ba'a kammala ba:-

(1) Yana Gina makarantar sakandare a Jikamshi, Musawa.

(2) Yana Gina mataki na biyu na Madatsar Ruwan Bakori.

(3) Yana Gina karin ajujuwa a makarantu daban-daban a Bakori, Dandume, Kankara, Malumfashi da Musawa.

(C) Ayyukan Da Ke Tafe Yanzu Haka;-

(1) Gina Madatsun Ruwa na Dankanjiba, Unguwar Barkono da Sayaya.

(2) Gina cibiyoyin ICT a ƙananan hukumomi takwas na mazabar..

SAMAR DA AYYUKAN YI DA MUHIMMAN KUDURORI:-

A cikin shekaru ukun da s**a gabata, Sanata Dandutse ya taimaka wajen samar da sama da ayyukan yi na dindindin 90 a hukumomi da ma'aikatun gwamnatin tarayya daban-daban.

Haka kuma, ya gabatar da muhimman kudurori masu amfani ga yankin, ciki har da:

(1) Yakai Kudirin Kafa Jami'a.

(2) Yakai Kudirin kafa Jami'ar Tarayya ta Kimiyyar Kiwon Lafiya da Lafiyar Jama'a ta Funtua, wanda ke jiran karatu na uku a Majalisar Dattawa.

(3) Yakai Kudirin Kafa Asibitin Tarayya.

(4) Yakai Kudirin kafa Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya a Malumfashi, wanda aka yi masa karatu na farko.

(5) Yakai Kudirin Kafa Yankin Kasuwanci Mai 'Yanci

(6) Yakai Kudirin kafa Funtua Free Trade Zone, wanda zai taimaka wajen bunkasa tattalin arziki da samar da dubban ayyukan yi.

JAJIRCEWA WURIN HIDIMTA WA AL'UMMA

Masu sharhi kan harkokin siyasa da ci gaban al'umma na ganin cewa shekaru ukun farko na Sanata Muntari Mohammed Dandutse sun kasance shekaru na aiki tukuru, tsayawa tsayin daka wajen kare muradun jama'a da kuma samar da ayyukan ci gaba.

Da yake bayyana kudirinsa na ci gaba da yi wa jama'a hidima, Sanata Dandutse ya ce:

"Daga gabatar da muhimman kudurori masu amfani ga al'umma zuwa samar da damammaki ga mazabu, zan ci gaba da bayar da ingantaccen wakilci ga al'ummar Mazabar Sanatan Katsina ta Kudu."

Hakika, shekaru uku na farko sun nuna cewa tafiyar ci gaba, hidima da jajircewa a Mazabar Sanatan Katsina ta Kudu na ci gaba da samun karbuwa da tagomashi a tsakanin al'umma.

"Zaman lafiya ba kawai rashin rikici ba ne, kasancewar adalci da kyakkyawan shugabanci ne"_-Inji- Sanata Muntari Mohammed Dandutse

Rubutawa: Shamsu Wapa Dandume

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UNCikin matuƙar alhini da jimami, Sanatan Shiyyar Funtua kuma ɗan takarar kujerar Sanata...
25/06/2026

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN

Cikin matuƙar alhini da jimami, Sanatan Shiyyar Funtua kuma ɗan takarar kujerar Sanatan Katsina ta Kudu, Sanata Muntari Mohammed Dandutse, ya bayyana baƙin cikinsa bisa mummunan harin da ya yi sanadin rasuwar mutane bakwai da aka yi jana'izarsu a yau Alhamis a garin Sayaya, ƙaramar hukumar Matazu ta Jihar Katsina.

Sanata Dandutse ya bayyana wannan lamari a matsayin abin takaici, mai tayar da hankali da kuma ci gaba da jefa al'ummar yankin cikin baƙin ciki da zaman dar-dar. Ya ce babu wani abu da ya fi raɗaɗi kamar rasa rayukan bayin Allah ba tare da wani laifi ba.

Zuciyarmu na zubar da hawaye tare da iyalan waɗanda s**a rasa rayukansu. Wannan babban rashi ne ba ga iyalansu kaɗai ba, har ma ga al'ummar Katsina ta Kudu da Jihar Katsina baki ɗaya. Muna addu'ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta musu, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarsu, Ya kuma ba iyalansu haƙurin jure wannan babban rashi."

A madadin al'ummar Katsina ta Kudu, Sanata Muntari Mohammed Dandutse ya miƙa saƙon ta'aziyya ga iyalan mamatan, al'ummar garin Sayaya, Masarautar Matazu da gwamnatin Jihar Katsina bisa wannan ibtila'in da ya afku.

Ya kuma yi kira ga Gwamnatin Tarayya da hukumomin tsaro da su ɗauki matakan gaggawa da ƙwararan matakai domin kawo ƙarshen hare-haren 'yan ta'adda da s**a addabi yankunan Katsina da Arewa maso Yamma gaba ɗaya.

Sanatan ya ce lokaci ya yi da za a ƙara kaimi wajen kare rayuka da dukiyoyin al'umma tare da tabbatar da cewa masu hannu a irin waɗannan munanan ayyuka sun fuskanci hukunci mai tsauri.

Rayuwar ɗan Najeriya tana da daraja. Ba za a ci gaba da zubar da jinin bayin Allah ba tare da ɗaukar matakin da ya dace ba. Dole ne gwamnati ta tashi tsaye cikin gaggawa domin dakile wannan annoba ta rashin tsaro da ke ci gaba da salwantar da rayukan al'umma marasa laifi."

Ya ƙara da cewa, "Raɗaɗin da iyalan mamatan ke ciki a yau raɗaɗinmu ne baki ɗaya. Muna tare da su cikin wannan lokaci na jarrabawa, kuma muna addu'ar Allah Ya maye musu da mafificin alheri."

Allah Ya jiƙan waɗanda s**a rasu, Ya gafarta musu kura-kuransu, Ya sanya Aljannatul Firdausi ce makomarsu. Allah Ya bai wa iyalansu haƙurin jure wannan babban rashi, Ya kuma dawo da zaman lafiya, tsaro da kwanciyar hankali a Jihar Katsina da Najeriya baki ɗaya. Amin.

Dandutse Media Reporter

Sanata Muntari Dandutse Ya Taya Femi Gbajabiamila Murnar Cika Shekaru 64Sanatan da ke wakiltar Katsina ta Kudu a Majalis...
25/06/2026

Sanata Muntari Dandutse Ya Taya Femi Gbajabiamila Murnar Cika Shekaru 64

Sanatan da ke wakiltar Katsina ta Kudu a Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Muntari Mohammed Dandutse, ya taya Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Rt. Hon. Femi Gbajabiamila, murnar cika shekaru 64 da haihuwa.

A cikin saƙon taya murnar da ya fitar, Dandutse ya bayyana Gbajabiamila a matsayin gogaggen jagora kuma ɗan siyasa mai kishin ƙasa, wanda ya bayar da gagarumar gudunmawa wajen bunƙasa dimokuraɗiyya da harkokin majalisa a Nijeriya.

Ya ce a tsawon shekarun da ya shafe yana hidimar jama'a, musamman a Majalisar Wakilai ta Tarayya inda ya riƙe muƙaman Jagoran Masu Rinjaye da Kakakin Majalisar Wakilai ta Tara, Gbajabiamila ya taka muhimmiyar rawa wajen inganta ayyukan majalisa da samar da dokokin da s**a taimaka wajen ci gaban ƙasa.

Sanatan ya kuma yaba da irin rawar da yake takawa a matsayinsa na Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, yana mai cewa yana ci gaba da nuna ƙwarewa, jajircewa da sadaukarwa wajen gudanar da ayyukan da s**a shafi hidimar ƙasa.

Dandutse ya yi addu’ar Allah Ya ƙara wa Gbajabiamila lafiya, hikima da tsawon rai, tare da yi masa fatan samun ƙarin nasarori a rayuwarsa da ayyukan da yake gudanarwa.

“Ina taya Rt. Hon. Femi Gbajabiamila murnar cika shekaru 64 da haihuwa. Ina roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya ci gaba da ba shi lafiya, hikima da nasara a ƙoƙarinsa na yi wa Nijeriya da al’ummarta hidima,” in ji Dandutse.

Dandutse Media Reporter

25/06/2026

Happy follow-versary to my awesome followers. Thanks for all your support! Rabiu Muhammad Sayaya

Zaman Majalisar Dattawa na Yau Sanata mai wakiltar Katsina ta Kudu a Majalisar Dattawa, Sanata Muntari Mohammed Dandutse...
24/06/2026

Zaman Majalisar Dattawa na Yau

Sanata mai wakiltar Katsina ta Kudu a Majalisar Dattawa, Sanata Muntari Mohammed Dandutse, ya halarci zaman Majalisar Dattawa da aka gudanar a ranar Laraba a harabar Majalisar Tarayya da ke Abuja.

Zaman ya gudana ne ƙarƙashin jagorancin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, inda sanatoci s**a tattauna muhimman batutuwan da s**a shafi tsaro da gyaran kundin tsarin mulkin ƙasa.

Daya daga cikin manyan batutuwan da aka tattauna shi ne kudirin gyaran kundin tsarin mulki da ke neman ba jihohin Nijeriya damar kafa rundunonin ’yan sandansu.

Bayan doguwar muhawara da nazari kan tanade-tanaden kudirin, Majalisar Dattawa ta amince da shi a zaman kwamitin gaba ɗaya.

Kudirin na neman samar da tsarin doka da zai ba jihohi damar kafa rundunonin ’yan sanda na kansu, yayin da Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya ta tarayya za ta ci gaba da aiki kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

Masu goyon bayan kudirin sun ce hakan zai taimaka wajen ƙarfafa tsaro, inganta tattara bayanan sirri, da kuma ba da damar mayar da martani cikin gaggawa ga matsalolin tsaro a matakin jihohi da ƙananan hukumomi.

Yayin muhawarar, Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Dattawa, Sanata Opeyemi Bamidele, ya bayyana kudirin a matsayin wani muhimmin sauyi a tsarin tsaron ƙasa, yana mai cewa zai taimaka wajen magance ƙalubalen tsaro da Nijeriya ke fuskanta.

Haka kuma, wasu sanatoci da s**a haɗa da Enyinnaya Abaribe da Aminu Waziri Tambuwal sun nuna goyon baya ga kudirin, tare da jaddada buƙatar samar da matakan kariya domin hana duk wani amfani da rundunonin ’yan sandan jihohi ta hanyar da ba ta dace ba.

A cewar dokokin gyaran kundin tsarin mulki, mataki na gaba shi ne samun amincewar aƙalla kashi biyu bisa uku na Majalisun Dokokin Jihohi 36 kafin a miƙa kudirin ga Shugaban Ƙasa domin sanya hannu ya zama doka.

Wakilin Katsina ta Kudu na daga cikin sanatocin da s**a halarci zaman da aka gudanar a Abuja. Masu lura da harkokin majalisa na ganin ci gaba da halartarsa a irin waɗannan muhimman zaman yana nuna ƙoƙarinsa na tabbatar da an wakilci muradun al’ummar mazabarsa yadda ya kamata, tare da ba da gudunmawa ga dokoki da manufofin da s**a shafi tsaro da ci gaban ƙasa.

Dandutse Media Reporter

Labara 24 ga watan Jun 2026,

24/06/2026

Video...

The bill to establish an Export Free zone, Funtua came up for first reading. This bill is very critical to the economic prosperity of North West zone and Nigeria at large if passed into law and I am hopeful and very passionate that this bill if passed will be the greatest achievement in the region.

Sen. Muntari Dandutse Media Reporters

Cikin Hotuna..Sanata mai wakiltar Katsina ta Kudu a Majalisar Dattawa, Muntari Mohammed Dandutse, ya halarci zaman da Ma...
23/06/2026

Cikin Hotuna..

Sanata mai wakiltar Katsina ta Kudu a Majalisar Dattawa, Muntari Mohammed Dandutse, ya halarci zaman da Majalisar Dattawa ta gudanar a yau, Talata, 23 ga Yuni, 2026, a harabar Majalisar Tarayya da ke Abuja.

Zaman ya gudana ƙarƙashin jagorancin Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Obot Akpabio, inda aka tattauna muhimman batutuwan da s**a shafi harkokin ƙasa da ayyukan majalisa.

A yayin zaman, Shugaban Majalisar Dattawa ya karanta wasiƙa daga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, wadda ta ƙunshi Kudirin Dokar Kafa ‘Yan Sandan Jihohi (State Police Bill). Ana sa ran kudirin zai kasance cikin manyan batutuwan da Majalisar za ta mayar da hankali a kansu domin ƙarfafa tsaro da samar da mafita ga ƙalubalen rashin tsaro da ake fuskanta a sassa daban-daban na ƙasar nan.

Daga bisani Majalisar dage ci gaba da zaman zuwa gobe, Laraba, 24 ga Yuni, 2026. Dage zaman ya biyo bayan karrama marigayi ɗan Majalisar Wakilai, Hon. Yaya Tongo, wanda ya rasu a kwanakin baya, bisa al'adar majalisa ta nuna alhini ga rasuwar mamba mai ci gaba da zama a majalisa.

Halartar Sanata Muntari Mohammed Dandutse a wannan muhimmin zama na nuna jajircewarsa da ƙudirin ci gaba da wakiltar muradun al'ummar Katsina ta Kudu, tare da ba da gudunmawa wajen samar da dokoki da manufofin da za su inganta rayuwar al'umma da ci gaban ƙasa baki ɗaya.

Dandutse Media Reporter
23 Yuni, 2026

PRESS RELEASEWhy Senator Muntari Dandutse Deserves a Second TermAs the 2027 General Elections approach, there are compel...
23/06/2026

PRESS RELEASE

Why Senator Muntari Dandutse Deserves a Second Term

As the 2027 General Elections approach, there are compelling reasons why the Senator representing Katsina South Senatorial District, Senator Muntari Mohammed Dandutse, deserves the continued support of the people through a second term in office.

The people of Katsina South deserve representation that is accessible, effective, and result-oriented. Senator Dandutse has consistently demonstrated these qualities through his leadership style, legislative contributions, and commitment to grassroots development.

As Chairman of the Senate Committee on TETFund, Senator Dandutse occupies a strategic position that enables him to influence policies affecting Nigeria’s higher education sector. His role was instrumental in providing legislative support for the establishment of the Federal University of Medical and Health Sciences, Funtua, among other educational initiatives across the country.

One of his greatest strengths has been his close relationship with the people. Unlike many politicians who become distant after elections, Senator Dandutse has maintained regular engagement with traditional rulers, youth and women groups, party leaders, and stakeholders across the eleven local government areas of Katsina South. This has ensured that the concerns of ordinary citizens continue to receive attention at the national level.

His commitment to youth and educational development is equally commendable. Through scholarship opportunities, empowerment programmes, skills acquisition initiatives, and support for entrepreneurs, many young people and women have benefited directly from his interventions. A second term would guarantee the continuation and expansion of these programmes.

Senator Dandutse has also brought valuable experience and stability to legislative representation. In a system where influence is built through relationships, seniority, and institutional knowledge, retaining an experienced lawmaker strengthens Katsina South’s ability to attract federal projects and opportunities.

Furthermore, his record of interventions in areas such as security support, healthcare outreach, infrastructure development, and financial assistance to vulnerable constituents reflects a genuine commitment to public service. While no leader can solve every challenge, his responsiveness and dedication have earned him widespread respect.

His loyalty to the party and commitment to the mandate entrusted to him by the people have also helped align federal opportunities with local development needs, translating promises into tangible projects and programmes.

It is therefore not surprising that Senator Muntari Mohammed Dandutse continues to enjoy the support and endorsement of party leaders, stakeholders, traditional and religious leaders, youth groups, student bodies, women organizations, and voters across Katsina South Senatorial District.

As 2027 draws nearer, the people of Katsina South have an opportunity to consolidate the gains already achieved by renewing the mandate of Senator Muntari Mohammed Dandutse for a second term.

Signed, Mubashir Mustapha
Funtua, Katsina State
23 June 2026

PRESS RELEASEA CALL TO KATSINA SOUTH PEOPLE: CHOOSE EXPERIENCE, CHOOSE TRUSTED LEADERSHIPAs the 2027 General Election ap...
22/06/2026

PRESS RELEASE

A CALL TO KATSINA SOUTH PEOPLE: CHOOSE EXPERIENCE, CHOOSE TRUSTED LEADERSHIP

As the 2027 General Election approaches, the people of Katsina South Senatorial District stand at a defining moment in their political journey. The choice before the electorate is clear: to continue with proven leadership and effective representation or to risk uncertainty through experimentation.

Across democratic societies, leadership is entrusted to individuals with demonstrated competence, integrity, and a verifiable record of public service. Governance requires experience, vision, and the ability to deliver tangible results for the people.

Senator Muntari Muhammad Dandutse has consistently exemplified these qualities. As the APC flag bearer for Katsina South Senatorial District, he brings years of legislative experience, public service, and unwavering commitment to the welfare of his constituents. His leadership is founded on three key principles:

1. Experience Over Experimentation
2. Integrity and Reliability
3. Commitment to Sustainable Development and Progress

Throughout his tenure, Senator Dandutse has championed initiatives aimed at improving infrastructure, empowering youths and women, supporting education, enhancing healthcare services, and attracting developmental projects to communities across Katsina South.

The 2027 General Election is not merely a political contest; it is an opportunity for the people to reaffirm their commitment to progress, stability, and effective representation. It is a chance to elect a leader who understands the challenges facing the district and possesses the experience and network required to attract federal opportunities and development programs.

We therefore call upon party faithful, community leaders, women, youths, and all stakeholders across Katsina South Senatorial District to unite and support Senator Muntari Muhammad Dandutse in the forthcoming election.

Together, let us choose experience. Let us choose competence. Let us choose a leader who is prepared to deliver meaningful progress for our people.

For Katsina South. For Progress. For the Future.

Signed:

Dr. Bello Abubakar Annoor
Director General, KADAF Development Forum, President, MAAN, Jagaban Azara Dan-Buran Funtua

Address

Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sen. Muntari Dandutse Media Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share