Popular News Hausa

Popular News Hausa we are giving consultancy services on media activities and other matters arise

Rokon Mu Ga Gwamnatin karamar Hukumar Katsina Da masarautar Katsina Shine Su Baiwa Abu Dayyabu Magaji Dannabaso, ~ Al'um...
06/11/2025

Rokon Mu Ga Gwamnatin karamar Hukumar Katsina Da masarautar Katsina Shine Su Baiwa Abu Dayyabu Magaji Dannabaso, ~ Al'ummar Yan'kin Dannabaso

Al’ummar Dannabaso dake Karamar Hukumar katsina Sun Roki Gwamnatin Karamar da Masarautar Katsina Su yi La’akari da bukatunsu Wajen Nadawa Magaji Dannabaso Ta Guddumar Shinkafi.

Al’ummar Dannabaso sun yi tattaki zuwa sakatariyar karamar hukumar Katsina da kuma fadar Sarkin Katsina domin nuna goyon bayansu ga jagoran al’ummar Abubakar Umar Abu Dayyabu.

Da suke magana a madadin al’ummar yankin, , Umaru Abdullahi, Turare Dannabaso da Aisha Muhammad Sun bayyana cewa sun je sakatariyar karamar hukumar da fadar Sarkin Katsina ne domin isar da bukatar su ga hukumomi, da su duba muradin al’ummar wajen nadin sabon Magaji Dannabaso ta gundumar shinkafi dake a karamar hukumar Katsina.

Malam Umaru Abdullahi Turare Dannabaso da Aisha Muhammad sun bayyana cewa al’ummar yankin na son a nada Abubakar Umar (Abu Dayyabu) a matsayin Hakimi saboda gudunmawar da yake bayarwa wajen cigaban yankin.

" Mala Abu Dayyabu ya taka muhimmiyar rawa wajen gyaran makarantar sakandare da asibitin yankin, tare da taimakawa wajen daukar nauyin biyan ma'aikatan wucin gadi a wadannan wurare da Samar da abubawan more rayuwa, Wannan ne ya sa al’umma s**a amince da goyon bayansa a matsayin Magajin Dannabaso"~ kamar yadda al'ummar s**a bayyana.

Da yake mayar da jawabi, Shugaban karamar hukumar Katsina, Alhaji Isah Mikidad A.D. Saude, ya yaba wa al’ummar bisa nuna hankalin da s**a yi wajen isar da bukatunsu ta hanya ta gari ga hukumomin da s**a dace.

Shugaban, wanda mataimakinsa Usman Yusuf Saulawa ya wakilta, ya bayyana cewa gwamnatin karamar hukumar za ta ci gaba da baiwa muradun jama’a fifiko, tare da kira ga al’umma da su ci gaba da raya zaman lafiya, hadin kai da fahimtar juna.

’Yan bindiga sun sace Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, Honarabul Samaila Bagudu, a garinsu da ke ƙaram...
01/11/2025

’Yan bindiga sun sace Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, Honarabul Samaila Bagudu, a garinsu da ke ƙaramar hukumar Bagudu.

Rahotanni sun bayyana cewa ’yan bindigar sun mamaye garin ne da yammacin ranar Juma’a suna harbe-harbe don tsoratar da al’umma.

Maharan sun yi awon gaba da ɗan majalisar ne a kan hanyarsa ta dawowa daga masallaci bayan ya an idar da sallah.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Babban Sakataren Yaɗa Labarai na gwamnatin jihar Kebbi, Ahmed Idris, ya ce an sanar da hukumomin tsaro, kuma ana ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da kuɓutar da Mataimakin Shugaban Majalisar.

Majiya: Aminiya

Kotu ta sauke Ɗan Majalisar tarayya da ya canza sheƙa daga PDP zuwa APC a jihar Zamfara Babbar kotun tarayya da ke Abuja...
31/10/2025

Kotu ta sauke Ɗan Majalisar tarayya da ya canza sheƙa daga PDP zuwa APC a jihar Zamfara

Babbar kotun tarayya da ke Abuja ƙarƙashin mai sharia Obiora Egwuatu, ta kori dan majalisar tarayya mai wakiltar Gummi da Bukuyyum Hon. Abubakar Gummi.

Haka kuma alƙalin Kotun ya umarci Ƙakakin Majalisar tarayya Hon. Tajudeen Abbas da ya ayyana kujerar sa a matsayin babu mai ita

Sannan ya umarci hukumar zaɓe ta ƙasaemai zaman kanta INEC da ta shirya sabon zaɓe nan da kwanaki 30 masu zuwa

Ya kuke ganin wannan mataki na Kotu?

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin TsaroGwamnan Jihar...
29/10/2025

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gargaɗi shugabanni da hukumomin tsaro da su guji tattaunawa da ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai idan har za a bar su da makaman nasu, yana mai cewa irin wannan salon sulhu ba ya kawo zaman lafiya, sai dai ya ƙara tashin hankali tare da raunana ikon gwamnati.

Gwamnan ya yi wannan jawabi ne a matsayin babban baƙo mai gabatar da lacca ga mahalarta taron Executive Intelligence Management Course (EIMC) na 18 a Cibiyar Nazarin Tsaro ta Ƙasa (NISS) da ke Abuja, ranar Laraba.

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, taken laccar shi ne: “Rawar ’Yan Faɗa-da-Gwamnati a Harkokin Tsaro: Ƙalubale da Damar Zaman Lafiya da Ci Gaban Afrika – Salon Zamfara.”

An bayyana cewa mahalartan EIMC 18 sun fito ne daga hukumomin tsaron Nijeriya da kuma ƙasashen Afrika kamar Chadi, Ghana, Rwanda, Somalia, da Gambiya.

A cikin laccarsa, Gwamna Lawal ya bayyana cewa salon Zamfara ta zama abin koyi ga sauran sassan Afrika wajen nazarin yadda ake ƙoƙarin samar da zaman lafiya da ci gaba.

Ya ce, “A cikin shekaru 20 da s**a wuce, tsarin tsaro a Afrika ya sauya sosai. Ra’ayin cewa gwamnati ita kaɗai ke da ikon amfani da ƙarfi yanzu ya fara fuskantar kalubale daga ƙungiyoyi marasa bin tsarin gwamnati – ciki har da ‘yan sa-kai, ƙungiyoyin kare kai, ‘yan ta’adda, barayin daji da kuma cibiyoyin aikata laifuka na ƙasa da ƙasa.”

Gwamnan ya bayyana cewa matsalolin tsaro a Zamfara sun samo asali ne daga rashin aikin yi, taƙaddamar albarkatun ƙasa, da canjin yanayi, tare da yawaitar makamai daga rikice-rikicen yankuna.

Ya ce, tun da s**a hau mulki a 2023, gwamnatinsa ta mayar da hankali wajen kafa tsaro bisa ginshiƙai uku:

1. Haɗin gwiwar hukumomin tsaro ƙarƙashin kwamitin tsaro na jiha da gwamnan kansa ke jagoranta.

2. Ƙirƙirar Rundunar Kare Al'umma ta 'Community Protection Guards' (CPG) domin tallafawa jami’an tsaro.

3. Haɗa kai tsakanin sarakunan gargajiya, ƙananan hukumomi da hukumomin tsaro wajen raba bayanan sirri da saurin ɗaukar mataki kan barazanar tsaro.

Ya ƙara da cewa, an kafa kwamitocin sulhu a kowace ƙaramar hukuma da s**a haɗa da sarakuna, malamai, mata da matasa domin sulhunta rikice-rikice da gina aminci.

Gwamnan ya ce, Zamfara na aiki tare da ofishin mai ba da shawara kan harkokin tsaro na ƙasa da kuma ƙasashen ƙetare kamar Kolombiya wajen shirin Preventing and Countering Violent Extremism (PCVE) — wanda ke mayar da hankali kan shirin gyarawa da dawo da masu tubabbun 'yan ta'adda cikin al’umma.

A cewarsa, “Tattaunawar sulhu na iya taimaka wajen magance rikici, amma zaman lafiya na gaskiya ba zai samu ba sai an ajiye makamai. Sulhu ba tare da iko ba dai-dai yake da miƙa wuya gare su. Barin masu bindiga da makamai yayin da ake tsara sharuɗɗan zaman lafiya hanya ce ta sake janyo tashin hankali.”

Gwamna Lawal ya jaddada cewa duk wani yunƙurin sulhu dole ne ya zama mai tsari, ƙarƙashin jagorancin gwamnati, tare da cikakken iko na doka. “Zaman lafiya na gaskiya yana samuwa ne idan masu ɗauke da makamai sun amince da mulkin doka, kuma gwamnati ta tabbatar tana da ƙarfin kare jama’arta.”

A nasa jawabin, Kwamandan Cibiyar Tsaro ta Ƙasa, J.O. Odama (FSI+, FDC), ya yaba wa Gwamna Lawal bisa hangen nesan da ya gabatar, yana mai cewa, “Ya kawo mana cikakken haske kan gaskiyar lamura a Zamfara. Na tashi a can, na san irin ƙalubalen da ya fuskanta kafin ya zama gwamna. Amma yanzu ya sauya fasalin jihar daga fuskar rashin tsaro zuwa canjin na gaskiya da kyakkyawan fata ga al'umma.”

SULAIMAN BALA IDRIS
Mai Magana da Yawun Gwamnan Jihar Zamfara
29 ga Oktoba, 2025

Matakin ya biyo bayan korafr-korafen da aka yi tare da sake bin diddigin sunayen waɗanda aka yi wa afuwar a farkon watan...
29/10/2025

Matakin ya biyo bayan korafr-korafen da aka yi tare da sake bin diddigin sunayen waɗanda aka yi wa afuwar a farkon watan wannan na Oktoba, 2025

An kira ga shugaban ƙaramar ƙungiyar Funtua Hon. Abdulmutalib Goya da ya yi koyi da takwaransa na Dutsinma wajen aikin t...
26/10/2025

An kira ga shugaban ƙaramar ƙungiyar Funtua Hon. Abdulmutalib Goya da ya yi koyi da takwaransa na Dutsinma wajen aikin tsaftace muhalli.

Wannan kiran ya fito ne da shugaban gidauniyar hadin kan jama'ar Funtua Kwamarad Mannir Suleiman a lokacin tattaunawar da da manema labarai

Kwamarad Mannir Suleiman ya ce ya nuna buƙatar da ake da ita ga shugaban ƙaramar hukumar Funtua da ya yi koyi da na Dutsinma wajen aiwatar da kyakkyawar ayyuka.

A cewar sa, yin haka zai taimaka wajen rage cututtukan masu yaɗuwa da marasa yaɗuwa a tsakanin al'umma, kuma hakan zai taimaka wajen kawar da cutar maleriya baƙi ɗayan ta

Kwamarad Mannir Suleiman ya karfafa cewa haɗa gwaiwa da sashen kula da tsaftace muhalli na ƙaramar hukuma zai taimaka maka matuƙa gaya

Ita ma gidauniyar hadin kai yankin Funtua zata kasance wajen haɗa hannu domin tsaftace muhalli a garin Funtua.

Ya ce suna fatan shugabancin gidauniyar zai ɗauki mataki kamar yadda sauran ƙananan hukumomi s**a rigar s**a yi nisa wajen tsaftace muhalli.

25/10/2025
25/10/2025

Uwargidan Gwamnan jihar Katsina Hajiya Zulaihat Dikko Umar Raɗɗa ta jagorancin taron ranar 'Polio' ta duniya a Katsina

Taron dai ya haɗa da hukumomin lafiya da masu ruwa da tsaki akan sha'anin lafiya tare da waɗanda s**a nakasa a dalilin cutar 'Polio'

Ku Kalli Bidiyon

Gwamnatin Jihar Katsina Ta Sake Jaddada Aniyarta Ta Ci Gaba Da Bayar Da Gudunmawa Wajen Bunkasa Harkokin Wasanni A Cikin...
24/10/2025

Gwamnatin Jihar Katsina Ta Sake Jaddada Aniyarta Ta Ci Gaba Da Bayar Da Gudunmawa Wajen Bunkasa Harkokin Wasanni A Cikin Jihar.

Kwamishinan matasa da ci gaban wasanni, Alhaji Lawal Aliyu Zakari Shargalle, ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai a shirye-shiryen gudanar da gasar kwallon kafa ta yara ‘yan kasa da shekara goma sha takwas (U-18) karo na biyu ta shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya gudana a dakin taro na filin wasa na Muhamadu Dikko.

Kwamishinan wanda Babban sakataren na ma’aikatar, Muhammad Rabiu Muhammad, ya wakilta, ya bayyana cewa gwamnatin jihar mai ci tana bai wa ci gaban matasa muhimmanci, inda ta kafa makarantar koyon kwallon kafa domin bunkasa harkar wasanni.

Ya yaba da gudunmawar shugaban jihar na kungiyar Youth Sports Federation of Nigeria (YOSFN), Alhaji Aminu Wali, bisa kokarinsa wajen habaka harkokin wasanni a jihar.

A nasa jawabin, daraktan wasanni, Alhaji Abdullahi Bello, ya bayyana cewa an kammala dukkan shirye-shirye domin gudanar da gasar, inda wakilai daga jihohi goma sha biyar (15) sun isa Katsina domin fafatawa a gasar.

Alhaji Abdullahi Bello ya bukaci masu son wasanni a jihar da su marawa kungiyar jihar baya tare da nuna karamci ga baki a lokacin gasar.

A nasa bangaren, mataimakin shugaban kungiyar matasan yan'wasa na yankin Arewa maso Yamma, wanda kuma shine shugaban kungiyar na jihar, Alhaji Aminu Wali, ya bayyana cewa ‘yan wasan jihar sun lashe wasanni daban-daban a matakin kasa.

Alhaji Aminu Wali ya yaba wa gwamnatin jihar bisa karbar bakuncin wannan gasa, yana mai cewa hakan na nuna kudirin gwamnatin jihar wajen bunkasa harkokin wasanni.

An yi kira ga gwamnan jihar Katsina ya yi la'akari da ƴan asalin mazaɓu da ƙananan hukumomi, idan za a sake ɗaukar malam...
24/10/2025

An yi kira ga gwamnan jihar Katsina ya yi la'akari da ƴan asalin mazaɓu da ƙananan hukumomi, idan za a sake ɗaukar malaman makaranta a jihar.

Shugaban ƙungiyar sakatarorin ilimi na jihar Katsina kuma sakataren ilimin ƙaramar hukumar Danmusa Zaharaddeen Umar Danmusa ya yi wannan kiran a lokacin da yake zantawa da manema labarai bayan kammala taron masu ruwa da tsaki a kan ilimi wanda ya gudana a ɗakin taron ma'aikatar ilimi ta jihar Katsina.

Kamar yadda ya bayyana, hakan zai taimaka matuƙa wajen magance sauya wurin aiki da malamai keyi, magance ƙarancin malamai a yankunan karkara da kuma bada damar ɗaukar malamai masu kishin aikin a faɗin jihar.

Malam Zaharaddeen Umar Danmusa ya bayyana cewa, sanya masu kishin ilimi cikin tafiyar zai ƙara taimakawa wajen gyara ilimi a jihar.

Shugaban ƙungiyar sakatarorin ilimi ya yaba ma gwamnan jihar bisa bada damar a kakkaɓe kundi don gyara kwamitin kula da ingancin makarantu na SBMC a jihar Katsina da kuma ƙoƙarin ciyar da ilimi gaba a faɗin jihar.

Ya yi nuni da cewa, ƙoƙarin gwamnan a ɓangaren ilimi ne ya sa ƙungiyar malamai ta ƙasa ta ba shi lambar girmamawa a lokacin bikin tunawa da ranar malamai.

Ma'aikatar Ilimin Firamare Da Na Sikandire Ta Jihar Katsina Ta Gudanar Taro Na Kwana Ɗaya A Kan Yadda Za A Yi Zaɓen SBMC...
24/10/2025

Ma'aikatar Ilimin Firamare Da Na Sikandire Ta Jihar Katsina Ta Gudanar Taro Na Kwana Ɗaya A Kan Yadda Za A Yi Zaɓen SBMC Da Inganta Kwamitin A Jihar.

Da take jawabi, Kwamishinar ilimi ta jihar Katsina Hajiya Zainab Musa Musawa ta yi bayani mai tsawo a kan abinda taron ya ƙunsa.

Kwamishinar wadda ta samu wakilcin daraktar kula da makarantun babbar sikandire ta ma'aikatar Hajiya Raliya Yusuf; ta ce taron ya ƙunshi jaddada sabbin tsare-tsaren Kwamitin Kula da Ingancin Makarantu (SBMC); ƙarfafa alaƙa tsakanin gwamnati, al'umma da kwamitin SBMC don inganta ilimi; tattauna yadda za a gudanar da zaɓen kwamitin SBMC; da dai sauransu.

A lokacin taron, masu ruwa da tsaki a ɓangaren ilimi (SBMC) sun yi masayar fahimta da bada shawarwari a kan yadda za a gudanar da zaɓen cikin nasara da inganta kwamitin na SBMC.

Taron ya samu halartar daraktocin ilimi daban-daban, shugabannin kwamitin SBMC, jami'an tsaro, da dai sauransu.

Abubuwan da s**a gudana a wurin taron sun haɗa da yi ma Shugaban Kwamitin Kula da Ingancin Makarantu na SBMC na jihar Katsina Alhaji Bello Ciroma Ingawa addu'a bisa rasuwarshi.

An ɗan yamutsa hazo tsakanin Akpabio da Natashaa majalisar dattawa kan ƙudirin zubar da cikiAn samu ɗan rikici a zauren ...
22/10/2025

An ɗan yamutsa hazo tsakanin Akpabio da Natashaa majalisar dattawa kan ƙudirin zubar da ciki

An samu ɗan rikici a zauren majalisar dattawa a ranar Talata yayin da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan mai wakiltar Kogi ta Tsakiya s**a yi sabani yayin muhawara kan kudirin gyaran dokar aikata laifuka da ke neman tsananta hukunci ga masu taimakawa wajen zubar da ciki.

Kudirin da Sanata Opeyemi Bamidele ya gabatar, na neman ƙara hukuncin daga shekaru uku zuwa goma a gidan yari ba tare da zabin biyan tara ba. Sai dai wasu ’yan majalisa sun nuna damuwa cewa hakan na iya hana likitoci taimakon gaggawa a lokutan da rayuka ke cikin haɗari.

Akpabio ya dakatar da tattaunawar, ya kuma umarci kwamitin majalisar kan shari’a da doka da su sake nazarin kudirin cikin makonni biyu.

Sai dai bayan an dakatar da batun, Sanata Natasha ta nemi damar yin magana tana mai cewa batun ya shafi mata kai tsaye, amma Akpabio ya hana ta magana, yana mai cewa an rufe muhawarar gaba ɗaya.

Sanata Adams Oshiomhole ya goyi bayan matakin Akpabio, yana cewa sake buɗe batun zai karya dokokin majalisar.

Bayan zaman, Natasha ta bayyana takaici cewa an hana ta yin magana kan batu da ya shafi haƙƙin mata da lafiyarsu, tana mai cewa za ta bayar da gudunmawa lokacin da kwamitin majalisar zai sake nazarin kudirin.

Daily Nijeriya Hausa

Address

Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Popular News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Popular News Hausa:

Share