28/05/2026
Ƙungiyar Tsaffin Ɗalibai ta Makaranta Sakandiren Jeka-Dawo ta gwamnati da ke Kofar Yandaka (Government Day Secondary School) a cikin birnin Katsina ta karrama tsaffin ɗalibanta 4 da s**a samu muƙamai.
Ƙungiyar ta karrama su ne a lokacin taronta na Sallah, wanda ya gudana a ɗakin taron makarantar.
Mutanen da aka karrama sun haɗa da Ministan Gidaje da Raya Birane, Dr. Muttaka Rabe Darma; ɗan majalisar dokokin jihar Katsina mai wakiltar ƙaramar hukumar Katsina, Ali Abu Albaba; Kwamishinan Ma'aikatar Ruwa, Mannir Ayuba Sulluɓawa; da kuma shugaban jam'iyyar APC na ƙaramar hukumar Katsina, Bishir Gambo Saulawa.
Da suke jawabi kafin karrama su, shugaban ƙungiyar Haruna Sada Kofar Sauri da uban ƙungiyar Haruna Dalhatu sun yi bayani mai tsawo game da ƴaƴan ƙungiyar huɗu da s**a samu muƙamai.
Sun bayyana su a matsayin mutanen kirki, kuma masu ƙoƙarin kawo ma ƙungiyar da ma al'umma cigaba.
A nashi ɓangaren, sauran membobin ƙungiyar sun bada shawarwari yadda za a ƙara kawo ma ƙungiyar cigaba, tallafa ma membobin da ke da ƙaramin ƙarfi, da dai sauransu.
Abubuwan da s**a gudana a wurin sun haɗa da bada lambobin karramawa, gudunmuwar kudi, da dai sauransu.