06/11/2025
Rokon Mu Ga Gwamnatin karamar Hukumar Katsina Da masarautar Katsina Shine Su Baiwa Abu Dayyabu Magaji Dannabaso, ~ Al'ummar Yan'kin Dannabaso
Al’ummar Dannabaso dake Karamar Hukumar katsina Sun Roki Gwamnatin Karamar da Masarautar Katsina Su yi La’akari da bukatunsu Wajen Nadawa Magaji Dannabaso Ta Guddumar Shinkafi.
Al’ummar Dannabaso sun yi tattaki zuwa sakatariyar karamar hukumar Katsina da kuma fadar Sarkin Katsina domin nuna goyon bayansu ga jagoran al’ummar Abubakar Umar Abu Dayyabu.
Da suke magana a madadin al’ummar yankin, , Umaru Abdullahi, Turare Dannabaso da Aisha Muhammad Sun bayyana cewa sun je sakatariyar karamar hukumar da fadar Sarkin Katsina ne domin isar da bukatar su ga hukumomi, da su duba muradin al’ummar wajen nadin sabon Magaji Dannabaso ta gundumar shinkafi dake a karamar hukumar Katsina.
Malam Umaru Abdullahi Turare Dannabaso da Aisha Muhammad sun bayyana cewa al’ummar yankin na son a nada Abubakar Umar (Abu Dayyabu) a matsayin Hakimi saboda gudunmawar da yake bayarwa wajen cigaban yankin.
" Mala Abu Dayyabu ya taka muhimmiyar rawa wajen gyaran makarantar sakandare da asibitin yankin, tare da taimakawa wajen daukar nauyin biyan ma'aikatan wucin gadi a wadannan wurare da Samar da abubawan more rayuwa, Wannan ne ya sa al’umma s**a amince da goyon bayansa a matsayin Magajin Dannabaso"~ kamar yadda al'ummar s**a bayyana.
Da yake mayar da jawabi, Shugaban karamar hukumar Katsina, Alhaji Isah Mikidad A.D. Saude, ya yaba wa al’ummar bisa nuna hankalin da s**a yi wajen isar da bukatunsu ta hanya ta gari ga hukumomin da s**a dace.
Shugaban, wanda mataimakinsa Usman Yusuf Saulawa ya wakilta, ya bayyana cewa gwamnatin karamar hukumar za ta ci gaba da baiwa muradun jama’a fifiko, tare da kira ga al’umma da su ci gaba da raya zaman lafiya, hadin kai da fahimtar juna.