Popular News Hausa

  • Home
  • Popular News Hausa

Popular News Hausa we are giving consultancy services on media activities and other matters arise

Jam’iyyar SDP ta nesanta kanta da tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai, kuma ta ja masa kunne
25/07/2025

Jam’iyyar SDP ta nesanta kanta da tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai, kuma ta ja masa kunne

Bangarori Daban-daban na Al'ummar Karamar Hukumar Bindawa Sun Yabama Shugaban Karamar Hukumar Bisa Aiwatar Da  Ayyukan C...
25/07/2025

Bangarori Daban-daban na Al'ummar Karamar Hukumar Bindawa Sun Yabama Shugaban Karamar Hukumar Bisa Aiwatar Da Ayyukan Cigaba A Cikin Kwanaki 100 Na Mulkinshi.

Mataimakin Shugaban Jam'iyyar APC na karamar Hukumar Alhaji Amadu Nasiru Maikifi Doro yayi yabon A yayin wata ganawa da manema labarai A Doro.

Alhaji Amadu Nasiru Doro, ya ce aiwatar da ayyukan raya kasa da ake gudanarwa a halin yanzu ta wannan gwamnatin karamar hukumar na nuna damuwa shi wajen citar da yan'kin gaban.

Ya bayyana cewa, gwamnatin Badaru Giremawa ta samar da ayyukan gina ababen more rayuwa daban-daban bisa daidaito da shirin gwamnatin jiha na inganta rayuwar al’umma tun daga tushe.

Alhaji Amadu Maikifi Doro ya lura cewa waɗannan ayyuka zasu taimakawa Gwamna Radda na samar da damar samun ci gaban ababen more rayuwa a ƙauyuka.

Ya jaddada cewa ayyukan sun haɗa da gina masallatai a wasu mazabu da kuma magudanar ruwa domin kare al’umma daga ambaliya.

Ya ƙara da cewa, karamar hukumar ta gyara da kuma gina rijiyoyin burtsatse a fadin yankin domin inganta damar samun ruwan sha mai tsafta ga al’umma.

An tuna cewa gwamnatin Badaru Musa Giremawa kwanan nan ta kaddamar da gyaran rijiyoyin burtsatse da sauran ayyukan raya kasa a fadin karamar hukumar.

Alhaji Amadu Maikifi Doro ya yi amfani da wannan dama wajen kira ga jama’a da su ci gaba da mara wa gwamnatin karamar hukuma baya domin cimma burinta.

ya kuma yi alkawarin bayar da cikakken goyon baya ga manufofi da shirye-shiryen gwamnatin Gwamna Radda na inganta jin daɗin rayuwar al’ummar jihar.

Ma'aikatar Ilimin Bai Ɗaya da na Sikandare ta jihar Katsina ta ƙaddamar da kwamitin da zai tsara yadda za a aiwatar da S...
25/07/2025

Ma'aikatar Ilimin Bai Ɗaya da na Sikandare ta jihar Katsina ta ƙaddamar da kwamitin da zai tsara yadda za a aiwatar da Shirin haɗin gwiwa na Bunƙasa Ilimi da Tallafama Matasa kashi na 2 na Ƙungiyar Tarayyar Turai wanda ofishin kula da ilimi da al'adu na majalisar dinkin duniya ke yi.

Kwamishinar ma'aikatar Hajiya Zainab Musa Musawa ce ta ƙaddamar da ƙaddamar da kwamitin a lokacin wani zama da ya gudana a ɗakin taron ma'aikatar 24/07/2025.

Kamar yadda ta bayyana, aiwatar da wannan aikin ba na mutum ɗaya ba ne, saboda haka ta yi kira ga membobin kwamitin su bada gudunmawarsu.

Kwamitin ya ƙunshi wakilai daga kwalejin koyarwa ta gwamnatin tarayya da ke Katsina (FCE), Hukumar Bayar da Ilmin Bai Ɗaya ta jihar Katsina (SUBEB), Hukumar Kula da Malamai, (TSB), Kwalejin Ilimi ta Isah Kaita da ke Dutsinma, da dai sauransu.

A lokacin zaman sun yi masayar fahimta a kan yadda za a aiwatar da aiki.

Taken shirin shi ne bunƙasa ilimin malamai a ɓangaren fasahar zamani daga shekarar 2024 zuwa 2028.

Karfafa dangantaka tsakanin Sashen Shari'ar Musulunci Da Kungiyar Lauyoyi Shine Jigon Zaman Lafiya Da Ci gaba a Tsakanin...
22/07/2025

Karfafa dangantaka tsakanin Sashen Shari'ar Musulunci Da Kungiyar Lauyoyi Shine Jigon Zaman Lafiya Da Ci gaba a Tsakanin Al'umma, Cewar Alkalin Alkalan Jihar Katisna.

Alkalin Alkan jihar Katsina Ya jaddada cewa karfafa alaka tsakanin Bangaren Shari'ar Musulunci da kungiyar lauyoyi shine mashinfidar Zaman lafiya da cigaba acikin al'umma.

Farfesa Muhammad Kabir Abubakar ya bayyana haka a lokacin da ya karbi bakuncin kungiyar lauyoyi ta kasa reshen karamar hukunar Funtua.

Kamar yadda ya ce ziyarar kungiyar zata samar da wata kafa ta dorewar dangantakar dake tsakanin bangarorin guda biyu a kokarinsu na tabbatar da adalci a jihar Katsina.

Farfesa Muhammad Kabir Abubakar ya bayyana ziyarar a matsayin wadda tazo kan lokaci, ganin cewa ƙungiyar a Jihar Katsina ta kan nuna ƙarancin rashin kula ga ofishin Alkalin alkalai da Kotun Daukaka Kara ta Shari’a, kamar yadda ake gani.

Ya bayyana fata cewa wannan ziyara za ta buɗe ƙofa ga haɗin gwiwa mafi ƙarfi tsakanin Lauyoyi da Alƙalai, inda ya lura cewa ƙungiyar ta kasance a sahun gaba wajen tsayawa kan ƙa’idodin adalci da gaskiya, bin dokoki, da kuma kare hakkin bil’adama.

Saboda haka Alkalin alkalan ya tabbatar wa ƙungiyar da shirin sa na yin duk gyare-gyaren da s**a dace ga dokokin Kotun Shari’a ko umarni kamar yadda Lauyoyi s**a nema.

Tunda farko da yake jawabi, Shugaban Ƙungiyar Lauyoyin Najeriya reshen karamar hukumar Funtua, Barista Ibrahim Korau, ya ce manufar ziyarar su ita ce ƙarfafa zumunci da kyakkyawar alaƙa tsakanin Kotun Shari’a ta Jihar da ƙungiyar Lauyoyi.

Barista Ibrahim Korau ya kuma jaddada buƙatar a yi gyare-gyare ga dokokin Kotun Shari’a, yana mai lura cewa gyaran karshe an yi shi tun a shekarar 2008.

Ta'aziyya: Tsohon Shugaban kasa Margayi Muhammad Buhari Mutum ne Mai Kaunar Cigaba Kasa da Talakkawa,~ Badamasi Ya'u Yan...
21/07/2025

Ta'aziyya: Tsohon Shugaban kasa Margayi Muhammad Buhari Mutum ne Mai Kaunar Cigaba Kasa da Talakkawa,~ Badamasi Ya'u Yan'tumaki.

Shugaban Hukumar Kula da bayar da kwangila da sayar da kadarorin gwamnatin ta jiha Alhaji Badamasi Ya'u Yantumaki ya bayyana rasuwar tsohon shugaban Nigeria Margayi Muhammadu Buhari amatsayin babban rashi baga Nigeria kadai ba gabaki dayan nahiyar Afirika wanda za'a dade ba'a cike gibin shi ba.

Shugaban hukumar ya bayyana haka ne a yayinda yake mika sakon ta’aziyya shi ga iyalai, Gwamnati Jiha dama masarautar Daura bisa rasuwar tsohon shugaban kasa margayi Muhammadu Buhari.

Alhaji Badamasi Ya'u yan'tumaki wanda ya bayyana margayi Muhammadu Buhari amatsayin jajirtaccen mutum mai tsayuwa akan gaskiya, ya bayyana cewa mutum ne wanda Allah ya horeshi da dukkan nagartar shugabancin nagari da ake bukata.

Yayi amfani da damar wajen kira ga al'umma dasu dauki dabi'ar kare abubuwan da gwamnati ke samarwa don cin moriyar abubuwan da tsohon shugaban kasar ya bari.

Shugaban hukumar ya kuma Mika sakon godiya ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu bisa irin soyayya da karramawa da yayima margayi muhammadu buhari.

Daga nan sai ya mika sakon ta’aziyya ga iyalan margayi muhammadu Buhari da gwamnatin jihar katsina dama masarautar Daura.

Wane tasiri bada muƙamin da shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu zai ga ɗan tsohon shugaban ƙasa Muhammad Babangida zai yi a ...
19/07/2025

Wane tasiri bada muƙamin da shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu zai ga ɗan tsohon shugaban ƙasa Muhammad Babangida zai yi a siyasar arewacin Nijeriya?

Ku bayyana mana ra'ayin ku

Tsohon ɗan majalisar tarayya wanda ya wakilci Katsina ta tsakiya Hon. Aminu Ahmad Chindo ya ziyarci shugaban majalisar t...
19/07/2025

Tsohon ɗan majalisar tarayya wanda ya wakilci Katsina ta tsakiya Hon. Aminu Ahmad Chindo ya ziyarci shugaban majalisar tarayya ta ƙasa Hon. Tajudeeb Abbas a ofishin sa da ke Abuja

Sirajo Yazid Abukur Na Neman Masu Haka Kabarin Buhari Yayi Musu KyautaBiyo bayan faifan bidiyo da ya karaɗe kafafen sada...
17/07/2025

Sirajo Yazid Abukur Na Neman Masu Haka Kabarin Buhari Yayi Musu Kyauta

Biyo bayan faifan bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta, na wani mazaunin garin Daura, Muhammad Ali, wanda ya jagoranci wadanda s**a haka kabarin marigayi tsohon shugaban kasar Najeriya Muhammadu Buhari, masoyan Buhari sun fara mayar da biki.

A halin yanzu dai, tuni shugaban Hukumar Kula da Gyaran Hanyoyi ta Jihar Katsina (KASSROMA), Engr. Sirajo Yazid Abukur, ya bada cigiyar wannan bawan Allahn, da alkawari ba shi kyautar Naira miliyon daya su raba, shi da mataimakansa.

Ya ce mataimakan Muhammad Ali, su biyu, kowannensu zai dauki Naira dubu dari biyu da hamsin domin su ja jari.

Shugaban na KASSROMA ya yaba wa gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, bisa irin damuwar da ya nuna da tabbatar da cewa an birne tsohon shugaban kasar cikin mutunci.

Ya ce Gwamna Radda ya shiga cikin hidimar dumu-dumu tun daga dauko gawar tsohon shugaban kasar har zuwa kai ta Daura, har zuwa yi mata sutura .

Abukur ya ce abin da ya fi burge shi shine yadda gwamnan ya cire babbar rigarsa ya shiga cikin masu aikin birne tsohon shugaban kasar, ya ce hakan ya nuna amanarsa da tawalu'u da kuma dabi'u na jagoranci.

NBTE Ta Ziyarci Kwalejin Nexus College of  Nursing Science Katsina Hukumar Ilimin Fasaha Ta Ƙasa NBTE sun ziyarci kwalej...
15/07/2025

NBTE Ta Ziyarci Kwalejin Nexus College of Nursing Science Katsina

Hukumar Ilimin Fasaha Ta Ƙasa NBTE sun ziyarci kwalejin Nexus College of Nursing Science Katsina domin tantance kayayyakin aikin su kafin fara karatu.

Tawagar ƙarƙashin jagorancin injiniya Hamidu Isah Abba sun isa kwalejin domin duba irin shirin da kwalejin ta yi na fara karatun aikin jinya da unguwar zoma.

Tunda farko a jawabin sa, mamallakin kwalejin ya yi lale marhabin da tawagar wanda ya bayyana a matsayin wani mataki na samun kafuwar kwalejin Nexus College of Nursing Science da ke Katsina.

Dakta Bashir Sani shi ne ya wakilci mamallakin kwalejin ya yi bayanin cewa sha'awar su da bada gudunmawa a ɓangaren kiwon lafiya tasa s**a jingine duk wasu nau'o'i da suke a wannan wuri s**a maida ita makaranta.

A cewar Dakta Bashir Sani suna da kyakkyawar fatan cewa kafa wannan kwalejin zai taimaka wajen kawo saukin ga al'umma musamman a wannan lokaci da harkar kiwon lafiya ta zama wani babban ƙalubale.

Sannan ya yi fatan cewa wannan tawaga ta hukumar ta ilimin kimiyya da fasaha ta ƙasa NBTE zata gudanar da aikin tantance kayayyakin da kwalejin ta samar domin fara zangon karatu.

Da yake nasa jawabi shugaban tawagar NBTE injiniya Hamidu Isah ya nuna jin dadi da irin yadda hukumar gudanarwar kwalejin s**a shirya masu tarba wanda ya ce haka zai taimaka masu wajen gudanar da aikin su ba tare da wani cikas ba.

Injiniya Hamidu Isah ya yaba da ƙoƙarin mahukuntan kwalejin Nexus College of Nursing Science wajen ƙoƙarin samar da yanayi mai kyau na koyo da koyarwa.

Haka kuma bayan kammala zagaye da tantance kayayyakin da kwalejin ta samar domin fara zangon karatu, injiniya Hamidu ya lura da wasu abubuwa da ya bada shawara akan gyara a kuma inganta wasu tare da samar da waɗanda babu.

Ya kawo misalai da dama na yadda abubuwa s**a canza a lokaci na duniya a tafin hannu tare da karfafa gwiwar mahukunta da su ƙara ninka ƙoƙarin su wajen ganin wannan kwalejin ta kai matakin da hukumomi za su amince da ita

Da ya ke ɗan tsokaci shugaban kwalejin (Provost) Ferfesa Adamu Ɗalhatu ya yi na'am da shawarwari da tawagar ta bayar wanda ya bada tabbacin cewa za su gyara domin cikin jerin manyan makarantu masu zaman kansu na lafiya.

Wasu daga cikin wuraren da tawagar ta zagaya domin ganewa idon ta sun haɗa da Ajujuwan karatu da ɗakunan gwaje-gwaje da Ɗakin kwana da asibiti da sauran ɓangarori.

An bayyana karatun Alkur'ani mai girma a matsayin aiki mai kyau nan gidan duniya da lahira.Kwamishinar Ma'aikatar Ilimin...
14/07/2025

An bayyana karatun Alkur'ani mai girma a matsayin aiki mai kyau nan gidan duniya da lahira.

Kwamishinar Ma'aikatar Ilimin Bai Ɗaya da na Sikandare ta bayyana hakan a lokacin rufe gasar karatun Alkur'ani ta Rabida karo na 15 ta matakin jiha ga makarantun da basu Arabiyya wanda ya gudana a cibiyar ERC da ke birnin 14 ga watan Yulin shekarar 2025.

Kamar yadda ta bayyana, Alkur'ani ba littafi bane kawai, umarnin ubangiji na yadda mutane zasu gudanar da rayuwa mai kyau.

Ta ce gasar za ta ƙara ma mutane imani da tsoran Allah.

Hajiya Zainab Musa Musawa ta yaba ma ɗaliban da s**a yi fice wajen karantun Alkur'anin mai girma.

A jawabinshi na maraba, jami'in kula da gasar wanda kuma shi ne daraktan kula da makarantun ƙaramar sikandaren Alhaji Kabir Dodo ya yaba ma Gwamnan Jihar Katsina da Kwamishinar Ma'aikatar Ilimi ta jihar Katsina bisa bada gudunmawa don ganin an samu nasarar gasar.

Gasar wadda aka tsara rukuni daban-daban, Hafsat Saminu daga ƙaramar hukumar Baure ta lashe gasar a matakin Hizib 60.

Taron ya samu halartar manyan mutane daban-daban da s**a haɗa da mai taimakawa Gwamnan Jihar Katsina akan harkokin ɗalibai Muhammad Nuhu Nagaske, Babbar Sakatariyar Ma'aikatar Ilimi Hajiya umulkhairi Ahmad Bawa, wakilin babban alkalin gasar karatun Malan Yakubu Abdulkadir, da dai sauransu.

Abubuwan da s**a gudana a wurin sun haɗa da bada kyauta daban-daban ga waɗanda s**a lashe gasar a mataki daban-daban, raba tallafin kuɗi da kwamishinar ilimi ta bada daga cikin aljihunta ga waɗanda s**a lashe gasar, gabatar da lambar karramawa ga uwar taron kuma mai ɗakin Gwamnan Jihar Katsina da kwamishinar ilimin.

Gidauniyar Gwagware Ta Miƙa Sakon Ta'aziyyar Rasuwa tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari Hukumar Gudanarwa ta gidauniya...
14/07/2025

Gidauniyar Gwagware Ta Miƙa Sakon Ta'aziyyar Rasuwa tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari

Hukumar Gudanarwa ta gidauniyar gwagware na Miƙa sakon ta'aziyyar ga iyalan tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari wanda Allah ya yi rasuwa jiya Lahdi, a wata asibiti da ke Landon a ƙasar Birtaniya

Wannan yana kunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban gidauniyar Alhaji Yusuf Aliyu Musawa ya sanyawa hannu a ka rabawa manema labarai a Katsina

A cewar sanarwar tsohon shugaban Nijeriya mutum ne mai gaskiya da jajircewa tare da ƙima wanda ya shugabanci Nijeriya bisa gaskiya da rikon amana tare da jajircewa.

Haka kuma sanarwar ta ce abubuwan shugabanci da shugaban ya bari sun kasance na sadaukarwa wanda ya dukufa don ganin an samu haɗin kan kasa da yi wa al'umma aiki, wanda za a dade ana tunawa da shi akan haka

"A matsayin wannan gidauniya ta taimakon al'umma da san cigaban al'umma, ta lura da irin cigaba da gudunmawa da marigayi Muhammadu Buhari ya bada wajen gina ƙasa da yakar cin hanci da rashawa da samar da ayyukan yi" inji sanawar

A irin wannan lokaci na juyayi, muna miƙa sakon ta'aziyyar mu ga Mai girma gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Raɗɗa da gwamnatin sa da masarautun Katsina da Daura

Wannan rashi da ƙasa ta yi na babban jigo abu ne da za a dade ba a manta da shi ba, musamman mutanen Katsina da suke alfahari da shi a matsayin wakili.

"Muna rokon Allah (S.W.T) ya yafe masa kura-kuransa sannan ya karbi kyakkyawan ayyukan sa sannan ya yi masa sakamako da gidan aljanna firdausi.

Haƙika Nijeriya ta yi rashin wani jigo, wanda ya bar abubuwan da za a cigaba da tunawa da su musamman ayyukan jin kai da aka yi wa al'umma.

Sai Gobe Talata Za a yi Jana'izar Tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari A garin Daura. - Gwamna Raɗɗa Gwamnan jihar Kats...
14/07/2025

Sai Gobe Talata Za a yi Jana'izar Tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari A garin Daura. - Gwamna Raɗɗa

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umar Raɗɗa ya bayyana cewa sai gobe talata idan Allah ya kaimu za a yi jana'izar tsohon shugaban kasar Muhammadu Buhari wandavya rasu jiya a wata asibiti da ke Landan.

Malam Dikko Raɗɗa ya bayyana haka jim kaɗan bayan dawowarsa Nijeriya daga ƙasar Birtaniya inda ya je duba tsohon shugaban kasar kafin Allah ya yi masa wa'adi.

A wata ganawa da manema labarai da gwamnan ya yi ya bayyana a hukumance cewa ana sa ran isowar gawar Muhammad Buhari Katsina da misalin karfe 12 00am na safe inda aka bayyana cewa za a yi jana'izar sa da misalin karfe 2:00pm na yamma a garin Daura ta jihar Katsina

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Popular News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Popular News Hausa:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share