Accuracy News Hausa

Accuracy News Hausa Accuracy News Hausa shafi ne na yada sahihan labarai a cikin harshen Hausa.

Muna kawo maku labarai ne na gaskiya cikin sauri da inganci daga Najeriya da duniya baki daya.

Ma'aikatar Raya Karkara Da Walwalar Jama'a Ta Shirya Walimar Sallah Ga Yara Da Ke Gidan Gyaran Hali Na Katsina .... Gwam...
27/05/2026

Ma'aikatar Raya Karkara Da Walwalar Jama'a Ta Shirya Walimar Sallah Ga Yara Da Ke Gidan Gyaran Hali Na Katsina
.... Gwamnatin Dikko Radda Ta Basu Gudummuwar Babbar Saniya Domin Shagalin Sallah

Ma'aikatar Raya Karkara Da Walwalar Jama'a ta Jihar Katsina, a karkashin jagorancin Farfesa Abdulhamid Ahmad, ta shirya walimar cin abincin Sallah ga yaran da ke gidan gyaran hali na Katsina.

Kwamishinan Ma'aikatar Farfesa Abdulhamid Ahmad, tare da Babban Sakataren Ma'aikatar da Darkatoci da sauran ma'aikata sun shaida wannan gagarumar walimar Sallah.

Da yake magantawa a yayin walimar cin abincin, Kwamishinan ya ce tun lokacin da Gwamna Radda ya hawo karagar mulki Gwamnatin shi ke shirya irin wannan walima ga yaran, domin su san cewa an kula da su.

A cewar shi, Gwamna Radda yana bayar da duk kulawar da ta kamata ga wadannan yara da ake kawowa a gidan, domin su fahimci rayuwa su zama mutane masu kyawawan halaye.

Daga nan sai ya yabawa Gwamna akan goyon baya da hadin kai da yake baiwa ma'aikatar a koda yaushe, tare da yin kira ga yaran akan su kasance masu hali na gari bayan fitar su gidan.

Babban Sakataren Ma’aikatar, Alhaji Muntari Kado Kurfi, ya magantu akan irin yadda Gwamna Radda ke nuna matukar damuwa da tabarbarewar tarbiyar yara masu tasowa.

Ya godewa Kwamishinan ma’aikatar Farfesa Abdulhamid Ahmad da gwamnatin Jihar Katsina, bisa irin jajircewa da ayyukan alkhairi da suke gudanarwa domin taimakon al’umma.

Haka kuma, ya yi nasiha ga yaran da ke gidan tare da ma’aikatan wajen tabbatar da ɗa’a, biyayya da kuma kyakkyawar mu’amala a tsakanin su.

Sauran wadanda s**a maganta a yayin taron sun hada da Daraktan Walwalar Jama'a Alhaji Jibrin Mukhtar da wasu daga cikin jami'an da ke kula da yaran.

Daga karshe an gudanar da addu'oi na musamman ga Gwamna Dikko Umaru Radda, akan Allah SWT ya kara yi mashi jagoranci a Gwamnatin shi.

Hoto: Katsina Post/Facebook

Sakon Barka Da Sallah Daga Mai Dakin Gwamnan Jihar Katsina Hajiya Fatima Dikko Radda A wannan lokaci na farin ciki na Ei...
27/05/2026

Sakon Barka Da Sallah Daga Mai Dakin Gwamnan Jihar Katsina Hajiya Fatima Dikko Radda

A wannan lokaci na farin ciki na Eid-el-Kabir, ina amfani da wannan dama wajen miƙa sakon taya murna da fatan alheri ga daukacin al’ummar Jihar Katsina da kuma al’ummar Musulmi baki ɗaya.

Wannan lokaci yana tunatar da mu muhimmancin sadaukarwa da biyayya da tausayi da kuma ibada ga Allah Maɗaukakin Sarki.

A yayin da muke gudanar da wannan biki mai albarka, ina kira ga daukacin al’umma da su cigaba da inganta zaman lafiya da haɗin kai da soyayya da fahimtar juna a cikin al’ummominmu.

Haka kuma, ina amfani da wannan dama wajen kira ga Alhazanmu da su roƙi Allah SWT ya kawo ƙarshen ƙalubalen da wasu sassan Jihar nan da ƙasa baki ɗaya ke fuskanta.

Ina kuma roƙonsu da su yi addu’ar Allah ya cigaba da yi wa mijina, Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, CON, jagora da taimako wajen kai jihar nan ga tudun mun tsira.

Mu kuma tuna da marasa galihu da zawarawa da marayu da sauran masu buƙata ta musamman, ta hanyar nuna musu kulawa da tallafi a wannan lokaci mai tsarki.

Ina addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki ya karɓi ibadunmu, ya yalwata mana albarka, kuma ya cigaba da kare Jihar Katsina da Najeriya baki ɗaya.

Allah ya sanya wannan Sallah ta zo mana da zaman lafiya, ci gaba, farin ciki ga kowanne gida.

Barka da Sallah!
Hajiya Fatima Dikko Radda,
Uwargidan Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina,
Malam Dikko Umaru Radda, PhD, CON.

Mawakin Kwankwasiyya Tijjani Gandu Ya Samu Takara A Karkashin Jam'iyyar NDCJam'iyyar NDC A Jihar Kano, Ta Tsayar Da Shah...
26/05/2026

Mawakin Kwankwasiyya Tijjani Gandu Ya Samu Takara A Karkashin Jam'iyyar NDC

Jam'iyyar NDC A Jihar Kano, Ta Tsayar Da Shahararren Mawakin Kwankwasiyya Tijjani Gandu, A Matsayin Dan Takarar Kujerar Dan Majalissar Dokokin Jiha Mai Wakiltar Birnin Kano, A Zaben Shekarar 2027.

Wane Fata Kuke Yi Mashi?

Subhanallah..... Wutar Lantarki Mai Amfani Da Hasken Rana Ta Yi Sanadiyar Haddasa Gobara A Wasu Shaguna Na Babbar Kasuwa...
26/05/2026

Subhanallah.....

Wutar Lantarki Mai Amfani Da Hasken Rana Ta Yi Sanadiyar Haddasa Gobara A Wasu Shaguna Na Babbar Kasuwar Katsina.

Allah Ya Kyauta Gaba Ya Kuma Maida Da Alkairi.

#𝗸𝗮𝘁𝘀𝗶𝗻𝗮𝘀𝘁𝗮𝘁𝗲

Saƙon Taya Murna Ga Gwamna Dikko Radda Daga Kungiyar Masu Shayi Da Biredi Ta Jihar KatsinaKungiyar Masu Shayi Da Biredi ...
24/05/2026

Saƙon Taya Murna Ga Gwamna Dikko Radda Daga Kungiyar Masu Shayi Da Biredi Ta Jihar Katsina

Kungiyar Masu Shayi Da Biredi Ta Jihar Katsina a karkashin jagorancin Alhaji Dikko Bello Radda, na taya murna ga Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda, akan samun tikitin takarar kujerar karo na biyu a zaben shekarar 2027.

Kungiyar ta masu shayi da biredi na kuma taya murna ga Gwamnan akan kammala zabukan fitar da gwani na yan takarkari da aka yi a cikin kwanciyar hankali da lumana.

Shugaban Kungiyar Alhaji Dikko Bello Radda, ya bayyana sake samun tikitin takarar na Gwamna Dikko Radda akan wani gagarumin cigaba ga Jihar Katsina da kuma kasa baki daya.

A cewar shi, Jihar Katsina ta samu gagarumin cigaba na ayyukan raya kasa, a karkashin jagorancin Gwamna Dikko Radda, saboda haka sake bashi dama zai tabbatar da dorewar wadannan ayyukan cigaba.

Daga nan sai ya yi fatan cewa, za'a kammala zabukan shekarar 2027 a cikin kwanciyar hankali da lumana, tare da yin kira ga al'ummar Jihar Katsina, akan su kasance sun zabi yan takarkari da suke da yakinin zasu kawo masu cigaba.

Alhaji Dikko Bello Radda ya kuma bukaci ya'yan kungiyar tasu akan su kasance masu bin doka da oda a lokacin yakin neman zabe da kuma kowane lokaci.

Daga karshe ya yi fatan alkhairi ga Gwamna Dikko Radda, tare da yi mashi addu'ar cigaba da samun jagorancin Allah SWT ta fuskar tafiyar da al'amurran Jihar Katsina.

Dan Soja Autan Rarara Mawakin Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD, CON, A Kasa Mai Tsarki, Yayin Gudanar D...
22/05/2026

Dan Soja Autan Rarara Mawakin Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD, CON, A Kasa Mai Tsarki, Yayin Gudanar Da Ibadar Aikin Hajji.

Barista Abba Mangal Ya Ziyarci Tsohon Gwamnan Jihar Katsina Ibrahim ShemaDan Takarar Kujerar Dan Majalissar Tarayya Mai ...
22/05/2026

Barista Abba Mangal Ya Ziyarci Tsohon Gwamnan Jihar Katsina Ibrahim Shema

Dan Takarar Kujerar Dan Majalissar Tarayya Mai Wakiltar Mazabar Karamar Hukumar Katsina, Barista Abba Dahiru Bara'u Mangal, Ya Ziyarci Tsohon Gwamnan Jihar Katsina Barista Ibrahim Shehu Shema.

Yanzu-Yanzu:Jam'iyyar ADC A Jihar Katsina Ta Tabbatar Da Alhaji Umar Tsauri Tata, A Matsayin Dan Takarar Kujerar Dan Maj...
21/05/2026

Yanzu-Yanzu:

Jam'iyyar ADC A Jihar Katsina Ta Tabbatar Da Alhaji Umar Tsauri Tata, A Matsayin Dan Takarar Kujerar Dan Majalissar Tarayya Mai Wakiltar Kananan Hukumomin Kurfi/Dustinma, A Zaben Shekarar 2027.

Wane Irin Fata Kuke Yi Mashi?

Jarin Shaddodi Na Ya Karye Saboda Kwaikwayon Gwamna Radda - Cewar Young DikkoMai kwaikwayon Gwamnan Jihar Katsina Muhamm...
21/05/2026

Jarin Shaddodi Na Ya Karye Saboda Kwaikwayon Gwamna Radda - Cewar Young Dikko

Mai kwaikwayon Gwamnan Jihar Katsina Muhammad Auwal, wanda aka fi sani da Young Dikko, ya koka akan yadda jarin shi na saida shaddodi ya karye saboda kwaikwayon Gwamnan.

A wata hira da ya yi da Kafar Sadarwa ta Katsina Post, Young Dikko ya ce, "duk na dinke shaddojin da nake siyarwa domin nai koyi da adonsa, ina rokon a taimaka man".

Ya yi fatan cewa, wannan sako zai isa ga Gwamnan, domin ya kawo mashi dauki akan wannan kalubale da yake fuskanta a halin yanzu.

Da Izinin Allah  Zaku Samu Wakilci Na Gari Idan Kuka Bani Dama - Injiniya Nura Khalil Ga Mutanen Shiyyar Funtua Dan taka...
20/05/2026

Da Izinin Allah Zaku Samu Wakilci Na Gari Idan Kuka Bani Dama - Injiniya Nura Khalil Ga Mutanen Shiyyar Funtua

Dan takarar Gwamnan Jihar Katsina a karkashin inuwar jam'iyyar PDP Sanata Yakubu Lado Danmarke, ya kaddamar da Injiniya Nura Khalil a matsayin dan takarar kujerar Sanatan Shiyyar Funtua, a karkashin jam'iyyar PDP.

Danmarke ya kaddamar da takarar Injiniya Nura Khalil ne a lokacin wani taro da ya samu halartar dubban magoya bayan jam'iyyar ta PDP daga Kananan Hukumomi 11 na Shiyyar Funtua.

Da yake magantawa a yayin taron, Sanata Yakubu Lado Danmarke ya bayyana Injiniya Nura Khalil a matsayin mutum mai jajircewa ta fuskar taimakon al'umma, a don haka ya bukaci al'ummar shiyyar akan su mara mashi baya domin samun nasarar lashe zabe.

Sanata Yakubu Lado Danmarke ya jaddada yakinin cewa, Injiniya Nura Khalil ba zai ci amanar al'ummar shiyyar ba idan s**a bashi damar wakiltar su a Majalissar Dattawa.

Daga nan sai ya yi kira ga al'ummar Jihar Katsina akan kada su yi kasa a guiwa wurin yin ruwan kuri'u ga jam'iyyar PDP, a zaben 2027, domin fitar da su daga halin matsin tattalin arziki da suke ciki.

Da yake magantawa, dan takarar kujerar Sanatan Injiniya Nura Khalil, ya bayyana farin ciki akan dandazon jama'a da s**a fito domin nuna soyayyar su gareshi a lokacin taron.

Injiniya Nura Khalil ya lashi takobin cewa, idan al'ummar shiyyar s**a bashi dama, ba zasu yi da na sanin tura shi wakilcin su ba a Majalissar Dattawa ta Kasa.

Daga nan sai ya nuna damuwa akan halin da tsaro yake ciki a shiyyar, sai ya yi fatan cewa da izinin Allah zai kasance mai bada gudummuwar da ta dace domin shawo kan matsalar.

20/05/2026

Address

Batsari Road
Katsina

Telephone

+17033444156

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Accuracy News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Accuracy News Hausa:

Share