25/10/2025
Honorabul Abdullahi Haruna Eka, Shugaban Kansilolin Jihar Katsina Ya Gwangwaje Al'ummar Mazabar Shi Da Tallafin Kudi
Shugaban Majalissar Kansilolin Karamar Hukumar Rimi Kuma Shugaban Zauren Kansiloli Na Jihar Katsina Honorabul Abdullahi Haruna Eka, ya bayar da tallafin kudi sama da naira miliyan daya ga al'umma daban-daban da s**a fito daga mazabar shi.
Honorabul Abdullahi Haruna Eka ya mika tallafin kudin ne a lokacin wani taro da ya gudana a Ofishin Jam'iyyar APC na Mazabar Sabon Gari/Allaraini.
Tallafin kudin dai ya samar da shi ne ga kananan yan kasuwa da s**a hada da masu saida shayi da biredi da masu chefane da masu saida kaji da masu saida kifi da mata masu kananan sana'oi da matasa.
Haka zalika, su ma Shuwagabannin Jam'iyyar APC na yankin da Limamai da dattawan jam'iyya da sauran masu hidima ga Jam'iyya, na daga cikin wadanda s**a amfana da tallafin kudin na Honorabul Abdullahi Haruna Eka.
Kamar yadda aka tsara, wadanda s**a karbi tallafin wasu sun amfana da naira 20,000 wasu kuma 10,000 a yayin da wasu kuma s**a karbi naira 5000.
Da yake kaddamar da rarraba tallafin, Shugaban Majalissar Kansilolin ta Karamar Hukumar Rimi ya bayyana cewa, samar da gudummuwar kudin wani yunkuri ne na marawa kokarin Gwamna Radda baya akan yadda yake kyautatawa Kansilolin Jihar Katsina.
A cewar Eka, ya samar da tallafin ne bisa alwashin da ya sha ga Gwamna Radda a lokacin wani taro cewa, Kansilolin Jihar Katsina zasu zauna lafiya da al'ummomin su, musamman ta hanyar kyautata masu.
Honorabul Abdullahi Haruna Eka ya yi magana mai tsawo akan kudirin da Gwamna Dikko Radda yake da shi na kyautatwa Kansilolin Jihar Katsina, wanda hakan zai basu sukunin su ma su kyautatawa al'umma.
Ya nuna godiya ga Shugaban Karamar Hukumar Rimi Honorabul Muhammad Ali Rimi da Sakatare na Musamman ga Gwamna Radda Honorabul Abdullahi Aliyu Turaji, akan yadda suke kara masu kwarin guiwa na kyautatwa al'umma.
Shugaban Kansilolin na Jihar Katsina ya kuma godewa al'ummar Mazabar tashi akan goyon baya da hadin kai da suke bashi a koda yaushe, sai ya sha alwashin cewa zai cigaba da yin bakin kokarin shi wurin kawo masu ayyukan cigaba.
Wadanda s**a maganta sun hada da Shugaban Jam'iyyar APC na Mazabar da Dattawan Jam'iyya da Shugabar Mata Ta yankin matasa, gami da Babban Limamin yankin.
Sun yabawa hangen nesan Honorabul Abdullahi Haruna Eka akan samar da wannan tallafi, sai s**a ce hakan ya nuna karara shi dan halal ne, kuma bai manta da jama'ar shi ba.