Accuracy News Hausa

Accuracy News Hausa Media Services and more

Innalillahi wa inna IlaiHi Rajiun. Allah ya yiwa Mahaifin Dr Bello Galadanchi (Dan Bello) rasuwa a Yau Alhamis 7 ga wata...
07/08/2025

Innalillahi wa inna IlaiHi Rajiun.

Allah ya yiwa Mahaifin Dr Bello Galadanchi (Dan Bello) rasuwa a Yau Alhamis 7 ga watan Agusta.

Allah ya gafarta masa. Ameen.

Shugaban Karamar Hukumar Rimi Ya Shimfida Ayyuka 79 A Cikin Kwanaki 100Shugaban Karamar Hukumar Rimi Hon.Mihammad Ali Ri...
07/08/2025

Shugaban Karamar Hukumar Rimi Ya Shimfida Ayyuka 79 A Cikin Kwanaki 100

Shugaban Karamar Hukumar Rimi Hon.Mihammad Ali Rimi ya gudanar da ayyukan raya kasa da cigaban al'umma har guda 79 a cikin kwanaki 100 na shugabancin shi.

Hon.Muhammad Ali Rimi ya bayyana hakan ne lokacin bikin cika shekaru 100 da hawan mulkin shi tare da zababbun Kansilolin Karamar Hukumar.

Bikin wanda ya gudana a farfajiyar Karamar Hukumar ya samu shaidawar jiga-jigan jam'iyyar APC na Karamar Hukumar da masu rike da sarautu da malaman addini,da matasa da sauran masu kyakkyawan fata a gareshi.

Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda wanda Mai Bada Shawara Akan Harkokin Siyasa Ya'u Umar Gwajo-Gwajo ya wakilta,ya yabawa Shugaban Karamar Hukumar akan shimfida dumbin ayyuka da s**a taba rayuwar al'umma a cikin kwanaki kalilan.

Gwamna Radda ya ce dandazon jama'a da s**a shaida taron murnar wata yar manuniya ce da ke tabbatar da cewa sun gamsu da salon mulkin Hon.Muhammad Ali Rimi.

A nashi jawabin,Dan Majalissar Tarayyar Akitat Usman Murtala Banye ya ce Hon.Muhammad Ali Rimi ya sha samun shi da bukatun al'umma,maimakon bukatar kashin kanshi,don haka ya taya al'ummar yankin murna akan yin shugaba na gari.

Shugaban Karamar Hukumar Hon.Muhammd Ali Rimi,ya ce ayyukan da ya shimfida a cikin kwanaki 100 basu rasa nasaba da goyon bayan da ya samu daga Gwamna Dikko Radda.

Hon.Muhammad Ali Rimi Ya Kuma yabawa masu ruwa da tsaki da Majalissar Kansiloli da masu rike da sarautu da sauran al'ummar yankin akan shawarwari da addu'oi da suke yi mashi.

Ya nanata kudirin cewa da izinin Allah ba zai ci amanar al'ummar yankin ba bisa damar da s**a bashi na shugabantar su.

Tsofaffin Shuwagabanni Karamar Hukumar Mu'azu Lemamu Tsagero da Nasiru Ala Iyatawa da Bilyaminu Muh'd Rimi,sun bayyana cewa akwai kyakkyawan yakin cewa Shugaban Karamar Hukumar zai ba mara da kunya a shugabancin shi.

Shugaban Masu Ruwa Da Tsaki Salisu Mamman Da Kauran Katsina da sauran Manyan baki suma duk sun maganta.

Sakon Taya Murna Daga Kungiyar Masu Shayi Da Biredi Ta Jihar Katsina.A madadin Shugabannin ƙungiyar Masu Sana'ar Saida S...
06/08/2025

Sakon Taya Murna Daga Kungiyar Masu Shayi Da Biredi Ta Jihar Katsina.

A madadin Shugabannin ƙungiyar Masu Sana'ar Saida Shayi Da Biredi ta jihar Katsina, da membobinmu dake lungu da saƙon jihar Katsina, ni Shugabanta ina taya murnar ga babban dan gwamnan jihar Katsina, Malam Muhammadu Dikko Umar Radda, bisa ga sarautar Gwagaren Katsina, Hakimin Raɗɗa da mai Martaba Sarkin Katsina, Alhaji Abdulmuminu Kabir Usman ya tabbatar masa.

Bayanin hakan na kunshe a cikin wata takardar taya murnar da shugaban ƙungiyar Masu Sana'ar Saida Shayi Da Biredi ta jihar Katsina, Malam Dikko Bello Raɗɗa ya sanya wa hannu aka raba wa manema labarai a Katsina, yau Talata.

Malam Dikko Bello Raɗɗa, ya kara da cewa ina da tabbacin sabin hakimin, haziƙin matashi mai hangen nesa, al'ummar za su amfana matuka da wannan baiwar da hakimin. Ina da yakinin zai kawo sauye-sauye masu da al'ummar wannan gunduma za su dunga alfahari da shi.

Daga karshe, muna addu'ar Allah ya kara wa maigirma gwamna, Malam Dikko Umar Radda lafiya da nisan kwana, domin cigaba da ayyukan alheransa, wanda s**a karade lungu da saƙon jihar Katsina.

Kwamishinan Da Aka Zarga Da Belin Dillalin Kwaya A Jihar Kano Ya Yi Murabus Daga Mukamin ShiKwamishinan Harkokin Sufuri ...
06/08/2025

Kwamishinan Da Aka Zarga Da Belin Dillalin Kwaya A Jihar Kano Ya Yi Murabus Daga Mukamin Shi

Kwamishinan Harkokin Sufuri na Jihar Kano da ya yi belin wanda ake zargin dilan miyagun kwayoyi ne a Kano, ya yi murabus

Kwamishinan Alhaji Ibrahim Ali Namadi, ya ajiye mukaminsa ne bayan da aka kammala bincike kan rawar da ya taka wajen bayar da beli ga wani da ake zargi da safarar miyagun kwayoyi, Sulaiman Aminu Danwawu.

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, ta nuna cewa kwamishinan ya yi murabus ne domin kare mutuncin gwamnatin Kano da ke da akidar yaki da fataucin kwayoyi da sauran laifuka.

Abin Burgewa Da Jinjina.....Nadadden Kansila Daga Mazabar Shema  Ta Karamar Hukumar Dutsinma A Jihar Katsina Honarabul D...
05/08/2025

Abin Burgewa Da Jinjina.....

Nadadden Kansila Daga Mazabar Shema Ta Karamar Hukumar Dutsinma A Jihar Katsina Honarabul Darda'u, Ya Tallafawa Masu Sana'ar Shayi Da Biredi Su 16 Da Jarin Biredin Dubu Goma-Goma Domin Kara Habbaka Kasuwar Su.

Wuraren Da Za'a Gudanar Da Taron Sauraron Ra'ayoyin Al'umma Da Ayyukan Da Suke Bukata A Fadin Mazabu 361 Na Jihar Katsin...
05/08/2025

Wuraren Da Za'a Gudanar Da Taron Sauraron Ra'ayoyin Al'umma Da Ayyukan Da Suke Bukata A Fadin Mazabu 361 Na Jihar Katsina.

Photo Credit: Katsina Post.

Yar Asalin Jihar Yobe Rukayya Muhammad Ta Lashe Gasar Muhawara Ta DuniyaGasar Teen Eagle da ta gudana a Birnin Landan ta...
05/08/2025

Yar Asalin Jihar Yobe Rukayya Muhammad Ta Lashe Gasar Muhawara Ta Duniya

Gasar Teen Eagle da ta gudana a Birnin Landan ta samu halartar ɗalibai daga ƙasashen duniya sama da 60, inda ɗalibar ’yar shekara 15 daga jihar Yobe, Rukayya Muhammad Fema, ta zama gwarzuwar shekarar 2025 a Gasar Muhawara.

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A Cikin Jam'iyyar Hada Ka Ta ADC Wani sabon rikici na neman ya kawo cikas akan yunkurin da jam...
05/08/2025

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A Cikin Jam'iyyar Hada Ka Ta ADC

Wani sabon rikici na neman ya kawo cikas akan yunkurin da jam'iyyar hada ka ta ADC ke yi na kwatar mulki daga jam'iyya mai mulki a zaben shekarar 2027.

Wannan sabon rikici dai na zuwa ne a dai-dai lokacinda Shuwagabannin Jam'iyyar na Jihohi s**a nuna kin amincewar su ga yadda sababbin mambobin su ke neman yin son iyawa a jam'iyyar.

Dama dai a yau Talata Shugaban Jam'iyyar na Jihar Kaduna ya gargadi Tsohon Gwamnan Jihar Malam Nasir El-Rufai,akan ya kiyayi yi masu Katsalanda a cikin harkokin su na yau da kullum.

Majiyar Accuracy News Hausa ta ruwaito cewar,Shuwagabannin Jam'iyyar na Jihohi sun bukaci jami'an tsaro akan su shiga tsakani tare da kame duk wanda ke yunkurin kawo masu rudu a cikin Jam'iyyar.

Jiga-Jigan APC A Jihar Kano Sun Jaddada Goyon Bayan Su Ga Tinubu A 2027Masu Ruwa da Tsaki na Jam'iyyar APC a Jihar Kano ...
05/08/2025

Jiga-Jigan APC A Jihar Kano Sun Jaddada Goyon Bayan Su Ga Tinubu A 2027

Masu Ruwa da Tsaki na Jam'iyyar APC a Jihar Kano sun jaddada goyon bayan su ga sake yin takarar Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu a zaben shekarar 2027.

Jiga-jigan jam'iyyar sun bayyana goyon bayan su ga takarar Shugaban Kasar ne a lokacin wani taro da ya gudana a Jihar ta Kano.

Gwagwaren Katsina Hakimin Gundumar Radda Alhaji Muhammadu Dikko Radda.....Allah Ya Taya Riko.
05/08/2025

Gwagwaren Katsina Hakimin Gundumar Radda Alhaji Muhammadu Dikko Radda.....

Allah Ya Taya Riko.

PDP Na Neman Goodluck Jonathan Ya Yi Mata Takara A Zaben 2027Rohotanni na nuni da cewar,Babbar Jam'iyyar ta PDP a Najeri...
05/08/2025

PDP Na Neman Goodluck Jonathan Ya Yi Mata Takara A Zaben 2027

Rohotanni na nuni da cewar,Babbar Jam'iyyar ta PDP a Najeriya na cigaba da zawarcin Tsohon Shugaban Kasa Goodluck Ebele Jonathan domin ya yi wa jam'iyyar takarar kujerar Shugaban Kasa a zaben 2027.

Majiyoyi da dama sun tabbatar da cewa manyan jiga-jigan jam'iyyar na cigaba da neman ganin sun jawo ra'ayin Tsohon Shugaban Kasar domin ya amince da yin takarar ga PDP.

Ko zaku sake goyon bayan Jonathan a zaben na 2027?.

Jagoran 'yan ta'adda, Bello Turji ya ajiye makamai.Turji ya saki mutanen da ya sace domin jaddada aniyarsa ta neman zama...
05/08/2025

Jagoran 'yan ta'adda, Bello Turji ya ajiye makamai.

Turji ya saki mutanen da ya sace domin jaddada aniyarsa ta neman zaman lafiya.

Rahoto ya nuna cewa an fara komawa gonaki sakamakon sulhun da aka yi da Turji.

Address

Batsari Road
Katsina

Telephone

+17033444156

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Accuracy News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Accuracy News Hausa:

Share