Accuracy News Hausa

Accuracy News Hausa Media Services and more

Zanga-Zanga Ta Barke A Birnin Douala Na Kasar Kamaru, Bayan Ayyana Sakamakon Zaben Shugaban Kasar Da Ya Baiwa Shugaba Pa...
27/10/2025

Zanga-Zanga Ta Barke A Birnin Douala Na Kasar Kamaru, Bayan Ayyana Sakamakon Zaben Shugaban Kasar Da Ya Baiwa Shugaba Paul Biya Nasara.

Hoto: 📸: Aljazeera

Lamido Zai Maka PDP Kotu Saboda Kin Sayar Mashi Da Form Din Takarar Shugabancin Jam'iyyar Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa Al...
27/10/2025

Lamido Zai Maka PDP Kotu Saboda Kin Sayar Mashi Da Form Din Takarar Shugabancin Jam'iyyar

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa Alhaji Sule Lamido, ya lashi takobin garzayawa kotu idan har babbar Jam'iyyar adawa ta PDP ta ki sayar mashi da form din neman takarar Shugabancin Jam'iyyar.

Haka dai na zuwa ne gabanin gudanar da babban taron Jam'iyyar da ke tafe a wata mai kamawa, inda za'a zabi sababbin shuwagabannin jam'iyyar.

Zamu Himmatu Wurin Inganta Rayuwar Ku Da Izinin Allah - Shugaban Karamar Hukumar Rimi Ga Masu Bukata Ta MusammanShugaban...
27/10/2025

Zamu Himmatu Wurin Inganta Rayuwar Ku Da Izinin Allah - Shugaban Karamar Hukumar Rimi Ga Masu Bukata Ta Musamman

Shugaban Karamar Hukumar Rimi Honorabul Muhammad Ali Rimi, ya bayyana aniyar shugabancin shi na yin duk mai yiyuwa ta fuskar inganta rayuwa da jin dadin masu bukata ta musamman a yankin.

Honorabul Muhammad Ali Rimi ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin Kungiyar Masu Bukata ta Musamman da ke Karamar Hukumar.

A cewar shi, shugabancin shi yana da kyakkyawan tsari na kyautata rayuwar su, ta hanyar koyar da su sana'oi da basu fifikon da ya kamata a dukkan shirye-shirye da tsare-tsaren Gwamnati.

Honorabul Muhammad Ali Rimi ya magantu akan dumbin shirye-shirye da Gwamnatin Dikko Radda ta bullo da su domin inganta rayuwar masu bukata ta musamman.

Wakilin tawwagar ya bayyana jin dadi akan kyakkyawar tarba da Karamar Hukumar ta yi masu, sai s**a bayyana cewa, suna sane da irin kokarin Shugaban Karamar Hukumar Honorabul Muhammad Ali Rimi ta fuskar kawo cigaban yankin.

Sun jaddada goyon bayan su ga gwamnatin Malam Dikko Umaru Radda da Shugaban Karamar Hukumar Honorabul Muhammad Ali Rimi.

Paul Biya Mai Shekaru 92 A Duniya, Ya Lashe Zaben Shugaban Kasa Na Kamaru Karo Na 8Shugaban Kasar Kamaru  Paul Biya Mai ...
27/10/2025

Paul Biya Mai Shekaru 92 A Duniya, Ya Lashe Zaben Shugaban Kasa Na Kamaru Karo Na 8

Shugaban Kasar Kamaru Paul Biya Mai shekara 92, Ya Sake Lashe Zaben Shugaban Kasar, Domin Fara Wa'adin Sa Na Takwas, Wanda Zai Kammala Yana Da Shekaru 99 A Duniya.

Paul Biya Dai Ya Shekara Hamsin Yana Shugabantar Kasar Ta Kamaru, Kafin Lashe Wannan Zaben.

Mu'assasatul Khairiyya Hajiya Hauwa Radda Ta Samu Lambar Yabo Ta Digirin Digirgir Akan Ayyukan Jin Kan Al'umma Tsohuwar ...
26/10/2025

Mu'assasatul Khairiyya Hajiya Hauwa Radda Ta Samu Lambar Yabo Ta Digirin Digirgir Akan Ayyukan Jin Kan Al'umma

Tsohuwar mai dakin tsohon Shugaban Kasa marigayi Umaru Musa Yar'adua, kuma yayar Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda, wato Hajiya Hauwa Radda, ta samu lambar yabo ta digirin digirgir akan ayyukan jin kan al'umma.

Wata jami'ar Kasar Turkiyya mai suna Franco-Arab University hadin guiwa da Cibiyar Franco- Arab African Council for Scientific Promotion ne s**a bayar da digirin na digirgir ga tsohuwar mai dakin tsohon Shugaban Kasar.

Accuracy News Hausa ta kalato cewar, an karrama Mu'assasatul Khairiyya din ne a lokacin taron Kimiyya da jami'ar ta shirya na shekarar 2025.

Hajiya Hauwa Radda dai na daga cikin mutane 12 da jami'ar ta zabo kuma aka karrama daga kasashe 14, wadanda an zabe su ne bisa ga gudummuwar da suke bayarwa ga yada Addinin Musulunci da zaman lafiya da tsaro da kuma tabbatar da cigaban al'umma.

Kamar yadda Accuracy News Hausa ta samu, an zabi Hajiya Hauwa Radda ne bisa ayyukan jin kai da take gudanarwa da s**a hada da:

Her pet Project, Mu'assasatul Khairiyya Foundation has been recognized for its humanitarian activities, including:

*Ciyar da mabukata da sauran masu karamin karfi.

*Tallafawa Yan Gudun Hijira da masu bukata ta musamman.

*Gina makarantun islamiyya da masallatai.

*Tallafawa dalibai da kayan karatu.

*Hada hannu da Hukumar Hisbah, domin gyaran akidar mutane da ke aikata laifuka.

*Gudanar da gangamin kula da lafiyar al'umma na kyauta, da ciyar da marayu a kullum.

Shugaban Cibiyar ta Franco-Arab Farfesa Mohammed Abdul Jara ne ya gabatar da lambar yabon ga Hajiya Hauwa Radda, sai ya yaba mata akan jajircewa da take yi wurin yada Addinin Musulunci da tallafawa mabukata.

Wannan karramawa da aka yi wa Hajiya Hauwa Radda wata yar manuniya ce ta kokarin ta wurin taimakon al'umma, a matsayin ta na tsohuwar mai dakin tsohon Shugaban Kasar Najeriya Marigayi Yar'adua da kuma kasancewar ta yaya ga Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda.

Ku Kasance Jakadu Na Kwarai Ga Karamar Hukumar Katsina - Mai Raba Alkairi Ga Sababbin Yan Sanda Da Ya Samar Wa AikiSabab...
26/10/2025

Ku Kasance Jakadu Na Kwarai Ga Karamar Hukumar Katsina - Mai Raba Alkairi Ga Sababbin Yan Sanda Da Ya Samar Wa Aiki

Sababbin jami'an yan sanda da Dan Majalissar Tarayya na Mazabar Karamar Hukumar Katsina Honorabul Sani Aliyu Danlami ya samar wa aiki sun bayyana cewa, zasu kasance masu aiki da gaskiya da rikon amana, tare kasancewa abin alfahari ga Karamar Hukumar Katsina da kasa Baki daya.

Sabbin jami'an yan sandan yan asalin Karamar Hukumar Katsina su 13 sun bayyana haka ne a lokacin da s**a kai wa Dan Majalissar Tarayyar ziyara a gidan sa da ke Katsina.

Ziyarar na da nufin nuna farin cikin su da godiyar su a gareshi, dangane da sama masu aikin yan sanda da ya yi daga cikin kokarin sa na sama wa matasa ayyukan dogaro da Kai.

Dan Majalissar Tarayyar Honorabul Sani Aliyu Danlami (Garkuwan Arewan Arewan Katsina) ya bayyana jin dadin sa dangane da wannan ziyara, inda ya yi kira ga sabbin jami'an yan sanda da su kasance masu sanya gaskiya da rikon amana a cikin harkokin aikin su.

Duk da cewa wannan ba shine na farko ba, Honorabul Sani Danlami Mai Raba Alkairi ya bayyana cewa, wakilcin shi zai cigaba da bada fifiko wurin ganin an sama wa matasa ayyukan yi da inganta harkar kiwon lafiya da bunkasa bangaren ilimi da aiwatar da ayyukan raya kasa da ci gaban al'umma da sauran su.

26/10/2025
26/10/2025

Rohoton Gidan Talabijin Na Jihar Katsina KTTV, Akan Yadda Shugaban Majalissar Kansilolin Karamar Hukumar Rimi, Kuma Shugaban Kansilolin Jihar Katsina Honorabul Abdullahi Haruna Eka Ya Raba Tallafin Kudi Kusan Naira Miliyan 2 Ga Al'ummar Mazabar Shi.

Honorabul Abdullahi Haruna Eka, Shugaban Kansilolin Jihar Katsina Ya Gwangwaje Al'ummar Mazabar Shi Da Tallafin Kudi Shu...
25/10/2025

Honorabul Abdullahi Haruna Eka, Shugaban Kansilolin Jihar Katsina Ya Gwangwaje Al'ummar Mazabar Shi Da Tallafin Kudi

Shugaban Majalissar Kansilolin Karamar Hukumar Rimi Kuma Shugaban Zauren Kansiloli Na Jihar Katsina Honorabul Abdullahi Haruna Eka, ya bayar da tallafin kudi sama da naira miliyan daya ga al'umma daban-daban da s**a fito daga mazabar shi.

Honorabul Abdullahi Haruna Eka ya mika tallafin kudin ne a lokacin wani taro da ya gudana a Ofishin Jam'iyyar APC na Mazabar Sabon Gari/Allaraini.

Tallafin kudin dai ya samar da shi ne ga kananan yan kasuwa da s**a hada da masu saida shayi da biredi da masu chefane da masu saida kaji da masu saida kifi da mata masu kananan sana'oi da matasa.

Haka zalika, su ma Shuwagabannin Jam'iyyar APC na yankin da Limamai da dattawan jam'iyya da sauran masu hidima ga Jam'iyya, na daga cikin wadanda s**a amfana da tallafin kudin na Honorabul Abdullahi Haruna Eka.

Kamar yadda aka tsara, wadanda s**a karbi tallafin wasu sun amfana da naira 20,000 wasu kuma 10,000 a yayin da wasu kuma s**a karbi naira 5000.

Da yake kaddamar da rarraba tallafin, Shugaban Majalissar Kansilolin ta Karamar Hukumar Rimi ya bayyana cewa, samar da gudummuwar kudin wani yunkuri ne na marawa kokarin Gwamna Radda baya akan yadda yake kyautatawa Kansilolin Jihar Katsina.

A cewar Eka, ya samar da tallafin ne bisa alwashin da ya sha ga Gwamna Radda a lokacin wani taro cewa, Kansilolin Jihar Katsina zasu zauna lafiya da al'ummomin su, musamman ta hanyar kyautata masu.

Honorabul Abdullahi Haruna Eka ya yi magana mai tsawo akan kudirin da Gwamna Dikko Radda yake da shi na kyautatwa Kansilolin Jihar Katsina, wanda hakan zai basu sukunin su ma su kyautatawa al'umma.

Ya nuna godiya ga Shugaban Karamar Hukumar Rimi Honorabul Muhammad Ali Rimi da Sakatare na Musamman ga Gwamna Radda Honorabul Abdullahi Aliyu Turaji, akan yadda suke kara masu kwarin guiwa na kyautatwa al'umma.

Shugaban Kansilolin na Jihar Katsina ya kuma godewa al'ummar Mazabar tashi akan goyon baya da hadin kai da suke bashi a koda yaushe, sai ya sha alwashin cewa zai cigaba da yin bakin kokarin shi wurin kawo masu ayyukan cigaba.

Wadanda s**a maganta sun hada da Shugaban Jam'iyyar APC na Mazabar da Dattawan Jam'iyya da Shugabar Mata Ta yankin matasa, gami da Babban Limamin yankin.

Sun yabawa hangen nesan Honorabul Abdullahi Haruna Eka akan samar da wannan tallafi, sai s**a ce hakan ya nuna karara shi dan halal ne, kuma bai manta da jama'ar shi ba.

Al'ummar Mazabar Sabon Gari/Allaraini Sun Nemi Daukin Gwamna Radda Akan Wata Hanya Mai Matukar Muhimmanci.... Sun Gudana...
25/10/2025

Al'ummar Mazabar Sabon Gari/Allaraini Sun Nemi Daukin Gwamna Radda Akan Wata Hanya Mai Matukar Muhimmanci
.... Sun Gudanar Da Aikin Gayya Domin Inganta Yanayin Hanyar

Al'ummar Mazabar Sabon Gari/Allaraini da ke Karamar Hukumar Rimi, sun roki Gwamna Dikko Radda akan ya kawo masu dauki wurin shimfida hanyar Eka-Sabon Gari-Allaraini-Shifdawa-Jibawa-Doro.

Kansilan Mazabar kuma Shugaban Majalissar Kansilolin Karamar Hukumar Rimi Honorabul Abdullahi Haruna Eka tare da masu magana da yawun al'ummar yankin ne s**a yi wannan kira, a sa'ilin da wakilin Accuracy News Hausa ya ziyarci yankin.

Honorabul Abdullahi Haruna Eka wanda kuma shi ne Shugaban Kungiyar Kansiloli ta Jihar Katsina ya bayyana cewa, wannan hanya tana da matukar muhimmanci ta fuskar bunkasa tattalin arzikin al'ummomin da ta shafa.

Wannan hanya dai ta shafi garuruwa sama da 40, wadanda suke karkashin Kananan Hukumomin Rimi da Charanchi da Bindawa da Ingawa da kuma karamar Hukumar Dutsi.

Rashin kyawon hanyar ya samo asali ne tun daga kan wata babbar korama da ta ratsa bayan Garin Sabon Gari, Wanda hakan ke kawo ma al'ummar tarnakin gudanar da zirga-zirgar yau da kullum akan hanyar.

A sabili da rashin kyawon hanyar, an samu mace-macen mata masu juna biyu a lokutan damina, baya ga wahalhalun da al'ummar ke fuskanta wurin zuwa gonakin su, da kuma safarar amfanin gonar zuwa gida.

Kamar yadda masu magana da yawun al'ummar s**a bayyana, sun dade suna neman gwamnatocin da s**a gabata su gudanar masu da wannan aiki, to sai dai har yanzu hakar su bata cimma ruwa ba.

A cewar su, Gwamna Dikko Umaru Radda ya yi alkawarin aiwatar da aikin hanyar a lokacin da ya ziyarci yankin a lokacin yakin neman zaben shi, sai s**a yi tuni ga Gwamnan akan bukatar yin aikin.

Masu magana da yawun al'ummar sun nuna godiya akan dumbin ayyukan cigaba da Gwamnatin ta Dikko Umaru Radda ta shimfida masu a yankin, sai s**a kara jaddada goyon bayan su ga gwamnatin tashi.

Sun yi amfani da damar inda s**a yabawa Shugaban Karamar Hukumar Rimi Honorabul Muhammad Ali Rimi, da Kansilan Mazabar Honorabul Abdullahi Haruna Eka, akan yadda suke kokarin kawo cigaba ga yankin.

Daga karshe Kansilan Mazabar kuma Shugaban Majalissar Kansilolin Karamar Hukumar Rimi Honorabul Abdullahi Haruna Eka ya yabawa wasu yan kasuwa a yankin, Alhaji Sabitu da Alhaji Kado, akan gudummuwar da s**a bada wurin gudanar da aikin gayyar.

Kansilolin Karamar Hukumar Katsina Sun Zama Yan Lelen Honorabul Isah Miqdad .... Zai Gina Majalissar Kansiloli Ta Zamani...
25/10/2025

Kansilolin Karamar Hukumar Katsina Sun Zama Yan Lelen Honorabul Isah Miqdad
.... Zai Gina Majalissar Kansiloli Ta Zamani Ga Kansilolin Karamar Hukumar

Karamar Hukumar Katsina a karkashin jagorancin Shugaban Karamar Hukumar Honorabul Isah Miqdad AD Saude, zata fara aikin ginin Majalissar Kansiloli ta zamani a karo na farko a tarihi Jihar Katsina.

Wannan yunkuri dai na da nufin tabbatar da hadin guiwa tsakanin bangaren zartaswa na Karamar Hukumar da Majalissar Dokokin, gami da inganta yanayin gudanar da aikin su.

Sabon ginin zai kasance da na’urorin fasahar zamani da kuma wutar lantarki na awa 24, don samar da ingantaccen wurin gudanar da harkokin Majalissa da ɗaukar muhimman shawarwari na cigaban al’umma.

Tune Ya Zama Sabon Shugaban Hukumar Hukumar Daukar Ma'aikata Ta Jihar KatsinaGwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umaru Rad...
24/10/2025

Tune Ya Zama Sabon Shugaban Hukumar Hukumar Daukar Ma'aikata Ta Jihar Katsina

Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda, Ya Amince Da Nadin Alhaji Idris Usman Tune A Matsayin Sabon Shugaban Hukumar Kula Da Ma'aikata Ta Jihar Katsina.

Allah Ya Sanya Albarka!

Address

Batsari Road
Katsina

Telephone

+17033444156

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Accuracy News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Accuracy News Hausa:

Share