27/07/2026
ADC Aspirants and Candidates Forum Katsina Ya Shiga Mako na Uku na Rangadin Haɗin Kai, Ya Ziyarci Zango, Baure, Sandamu, Daura da Mai’adua.
Katsina Times
Tawagar 'ADC Aspirants and Candidates Forum Katsina' sun shiga mako na uku na rangadin haɗin kai da suke gudanarwa a faɗin ƙananan hukumomin Jihar Katsina, domin ƙarfafa zumunci da haɗin kai tsakanin masu neman takara, waɗanda s**a samu tikitin takara da kuma waɗanda ba su samu ba, shugabannin jam'iyya da sauran masu ruwa da tsaki na jam'iyyar ADC, gabanin babban zaɓen shekarar 2027.
A ranar Lahadi, tawagar Forum ɗin ta kai ziyara tare da gudanar da taro a garin Daura wanda ya haɗa ƙananan hukumomi biyar: Zango, Baure, Sandamu, Daura da Mai’adua. Rangadi na daga cikin shirin zagaya dukkan ƙananan hukumomi 34 na jihar domin tabbatar da haɗin kan ‘ya’yan jam’iyyar, tattauna makomar jam’iyyar tare da kuma dabarun tunkarar zaɓen 2027.
Da yake jawabi, shugaban Forum din, Hon. Abdurrazaq Dahiru Kaita, ya bayyana cewa manufar rangadin ita ce haɗa kan duk masu neman takarar Majalisar Dokoki ta Jiha da sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar, ba tare da la’akari da wanda ya samu tikitin takara ko wanda bai samu ba.
Ya ce abin da ya faru a zaɓen fidda gwani ya riga ya zama tarihi, don haka lokaci ya yi da za a binne duk wani saɓani tare da mayar da hankali wajen ganin jam’iyyar ADC ta samu nasara a zaɓen 2027.
"Mun fito ne domin ceton al'umma. Ba kujerar takara kaɗai ce za ta kawo canji ba. Idan muka haɗa kai muka kafa gwamnati, za mu iya yi wa al'umma cikakkiyar hidimar da ta ce. Don haka ina kira ga kowa da ya zo mu yi aiki tare domin fitar da talakawa daga halin matsin rayuwar da suke ciki."
Hon. Kaita ya ƙara da cewa tun da farko an kafa Forum ɗin ne domin kawar da duk wata baraka da ka iya tasowa bayan zaɓen fidda gwani, tare da tabbatar da cewa duk masu neman takara suna tafiya a matsayin ahali guda, ya bayyana cewar Forum ɗin na kare muradun rukuni huɗu, da s**a haɗa da: na masu neman takara da ba su samu tikiti ba kuma suna da ƙorafi; na na waɗanda s**a samu tikitin takara; da na waɗanda ba su samu tikiti ba amma s**a amince da sakamakon zaɓen; da ku?a Jam’iyyar ADC baki ɗaya.
A nasa jawabin, Jami’in Hulɗa da Jama’a na Forum ɗin, Aliyu Abdulkadir Dan Hawwa, ya buƙaci duk masu ruwa da tsaki su ci gaba da mara wa waɗanda s**a samu tikitin takara baya.
Ya ce: "Kowa ya yi ƙoƙarinsa wajen neman takara, amma Allah ne ke ba wanda ya so, ga shi yanzu ya ba su. Mu fifita ci gaban jam’iyya a kan son zuciya, domin idan muka haɗa kai, da yardar Allah za mu samu nasara." In ji shi
Shi ma ɗantakarar Majalisar Wakilai ta Tarayya na mazabar Sandamu/Daura/Mai’adua a ƙarƙashin jam’iyyar ADC, Hon. Abdulrashid Nasir, PhD, ya yabawa shugabannin Forum ɗin bisa ƙoƙarin da suke yi na haɗa kan ‘ya’yan jam’iyya.
Ya bayyana cewa ayyukan Forum ɗin na haifar da sakamako mai kyau, yana mai misalta cewa a Ƙaramar Hukumar Baure sama da mambobin APC 20 masu riƙe da muƙaman Exco sun sauya sheƙa zuwa jam’iyyar ADC.
Ya kuma yi kira ga duk wanda ke da wani ɓacin rai sakamakon zaɓen fidda gwani da ya yi haƙuri, ya haɗa kai da sauran ‘ya’yan jam’iyyar domin ceto al’umma.
Bayan taron, tawagar Forum ɗin ta gudanar da jerin ziyarce-ziyarcen girmamawa da ta’aziyya a garin Daura. Tawagar ta kai ziyarar gaisuwar ta’aziyya gidan Kwamishina Habu Daura, inda ta jajanta masa bisa rasuwar Shehu Abu Daura, tare da addu’ar Allah Ya jikansa da rahama, Ya kuma ba iyalansa haƙurin jure rashin.
Haka kuma, tawagar ta kai ziyarar ta’aziyya gidan Alhaji Adanu Dan Bale, tare da yi wa iyalansa addu’ar Allah Ya gafarta wa mamacin.
Har ila yau, tawagar ta kai ziyarar girmamawa ga Tafidan Daura, Alhaji Sa’idu Abdurrahman, inda ya tarbe su cikin mutuntawa, ya yi musu nasihohi kan shugabanci, rayuwa da hidimtawa al’umma, tare da ƙarfafa musu gwiwar ci gaba da kasancewa matasa masu kishin jama’a.
Rangadin ya ƙare cikin yanayi na fahimtar juna, haɗin kai da farin ciki, inda mahalarta s**a sha alwashin yin aiki tare domin tabbatar da nasarar jam’iyyar ADC a zaɓen shekarar 2027.