TAFI KWABO TV

TAFI KWABO TV SHAFIN YA KUNSHI: LABARAI (NEWS), WAJARMA JAMAA DAKAI, SIYASA (POLITIES), SUPPORT (WASANNI), RAAYOYI, BUSINESS, ADDINI. MATUKAR BABU ZAGI KO CIN MUTUNCHI

Tafi kwabo tv

ADC Aspirants and Candidates Forum Katsina Ya Shiga Mako na Uku na Rangadin Haɗin Kai, Ya Ziyarci Zango, Baure, Sandamu,...
27/07/2026

ADC Aspirants and Candidates Forum Katsina Ya Shiga Mako na Uku na Rangadin Haɗin Kai, Ya Ziyarci Zango, Baure, Sandamu, Daura da Mai’adua.

Katsina Times

Tawagar 'ADC Aspirants and Candidates Forum Katsina' sun shiga mako na uku na rangadin haɗin kai da suke gudanarwa a faɗin ƙananan hukumomin Jihar Katsina, domin ƙarfafa zumunci da haɗin kai tsakanin masu neman takara, waɗanda s**a samu tikitin takara da kuma waɗanda ba su samu ba, shugabannin jam'iyya da sauran masu ruwa da tsaki na jam'iyyar ADC, gabanin babban zaɓen shekarar 2027.

A ranar Lahadi, tawagar Forum ɗin ta kai ziyara tare da gudanar da taro a garin Daura wanda ya haɗa ƙananan hukumomi biyar: Zango, Baure, Sandamu, Daura da Mai’adua. Rangadi na daga cikin shirin zagaya dukkan ƙananan hukumomi 34 na jihar domin tabbatar da haɗin kan ‘ya’yan jam’iyyar, tattauna makomar jam’iyyar tare da kuma dabarun tunkarar zaɓen 2027.

Da yake jawabi, shugaban Forum din, Hon. Abdurrazaq Dahiru Kaita, ya bayyana cewa manufar rangadin ita ce haɗa kan duk masu neman takarar Majalisar Dokoki ta Jiha da sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar, ba tare da la’akari da wanda ya samu tikitin takara ko wanda bai samu ba.

Ya ce abin da ya faru a zaɓen fidda gwani ya riga ya zama tarihi, don haka lokaci ya yi da za a binne duk wani saɓani tare da mayar da hankali wajen ganin jam’iyyar ADC ta samu nasara a zaɓen 2027.

"Mun fito ne domin ceton al'umma. Ba kujerar takara kaɗai ce za ta kawo canji ba. Idan muka haɗa kai muka kafa gwamnati, za mu iya yi wa al'umma cikakkiyar hidimar da ta ce. Don haka ina kira ga kowa da ya zo mu yi aiki tare domin fitar da talakawa daga halin matsin rayuwar da suke ciki."

Hon. Kaita ya ƙara da cewa tun da farko an kafa Forum ɗin ne domin kawar da duk wata baraka da ka iya tasowa bayan zaɓen fidda gwani, tare da tabbatar da cewa duk masu neman takara suna tafiya a matsayin ahali guda, ya bayyana cewar Forum ɗin na kare muradun rukuni huɗu, da s**a haɗa da: na masu neman takara da ba su samu tikiti ba kuma suna da ƙorafi; na na waɗanda s**a samu tikitin takara; da na waɗanda ba su samu tikiti ba amma s**a amince da sakamakon zaɓen; da ku?a Jam’iyyar ADC baki ɗaya.

A nasa jawabin, Jami’in Hulɗa da Jama’a na Forum ɗin, Aliyu Abdulkadir Dan Hawwa, ya buƙaci duk masu ruwa da tsaki su ci gaba da mara wa waɗanda s**a samu tikitin takara baya.

Ya ce: "Kowa ya yi ƙoƙarinsa wajen neman takara, amma Allah ne ke ba wanda ya so, ga shi yanzu ya ba su. Mu fifita ci gaban jam’iyya a kan son zuciya, domin idan muka haɗa kai, da yardar Allah za mu samu nasara." In ji shi

Shi ma ɗantakarar Majalisar Wakilai ta Tarayya na mazabar Sandamu/Daura/Mai’adua a ƙarƙashin jam’iyyar ADC, Hon. Abdulrashid Nasir, PhD, ya yabawa shugabannin Forum ɗin bisa ƙoƙarin da suke yi na haɗa kan ‘ya’yan jam’iyya.

Ya bayyana cewa ayyukan Forum ɗin na haifar da sakamako mai kyau, yana mai misalta cewa a Ƙaramar Hukumar Baure sama da mambobin APC 20 masu riƙe da muƙaman Exco sun sauya sheƙa zuwa jam’iyyar ADC.

Ya kuma yi kira ga duk wanda ke da wani ɓacin rai sakamakon zaɓen fidda gwani da ya yi haƙuri, ya haɗa kai da sauran ‘ya’yan jam’iyyar domin ceto al’umma.

Bayan taron, tawagar Forum ɗin ta gudanar da jerin ziyarce-ziyarcen girmamawa da ta’aziyya a garin Daura. Tawagar ta kai ziyarar gaisuwar ta’aziyya gidan Kwamishina Habu Daura, inda ta jajanta masa bisa rasuwar Shehu Abu Daura, tare da addu’ar Allah Ya jikansa da rahama, Ya kuma ba iyalansa haƙurin jure rashin.

Haka kuma, tawagar ta kai ziyarar ta’aziyya gidan Alhaji Adanu Dan Bale, tare da yi wa iyalansa addu’ar Allah Ya gafarta wa mamacin.

Har ila yau, tawagar ta kai ziyarar girmamawa ga Tafidan Daura, Alhaji Sa’idu Abdurrahman, inda ya tarbe su cikin mutuntawa, ya yi musu nasihohi kan shugabanci, rayuwa da hidimtawa al’umma, tare da ƙarfafa musu gwiwar ci gaba da kasancewa matasa masu kishin jama’a.

Rangadin ya ƙare cikin yanayi na fahimtar juna, haɗin kai da farin ciki, inda mahalarta s**a sha alwashin yin aiki tare domin tabbatar da nasarar jam’iyyar ADC a zaɓen shekarar 2027.

ADC Aspirants and Candidates Forum Katsina Na ci Gaba da Ziyarce-Ziyarcen Shugabanninta, Ta Jaddada Goyon Bayanta Ga Shu...
25/07/2026

ADC Aspirants and Candidates Forum Katsina Na ci Gaba da Ziyarce-Ziyarcen Shugabanninta, Ta Jaddada Goyon Bayanta Ga Shugabancin Matan Jam'iyyar.

Katsina Times

Ƙungiyar 'ADC Aspirants and Candidates Forum Katsina' a ranar Asabar ta ci gaba da gudanar da ziyarce-ziyarcen sada zumunci, haɗin kai (solidarity), kyautata alaƙa da kuma ta'aziyya a karamar hukumar Katsina, a wani mataki da ta bayyana a matsayin ci gaba da ƙoƙarinta na ƙarfafa haɗin kan jam'iyyar, gina kyakkyawar alaƙa tsakanin mambobinta da kuma girmama shugabannin jam'iyyar.

A ci gaba da ziyarce-ziyarcen a ranar Asabar, tawagar, ƙarƙashin jagorancin shugabanta, Hon. Abdurrazaq Dahiru, ta fara ne da kai ziyarar haɗin kai ga Shugabar matan Jam'iyyar ADC ta Jihar Katsina, Hajiya Amina Lawal Dauda. A yayin ziyarar, mambobin forum ɗin sun tabbatar mata da cikakken goyon bayansu tare da bayyana cewa suna tare da ita wajen ci gaban jam'iyyar. Sun kuma nemi haɗin kai da shawarwarinta musamman kan yadda za a ƙara bai wa mata damar taka rawar gani a cikin harkokin jam'iyyar, tare da tattauna dabarun da za su ƙarfafa ADC da kuma shirya ta yadda ya kamata domin fuskantar zaɓukan shekarar 2027.

Daga nan tawagar ta kai ziyarar sada zumunci ga Memba a cikinta, kuma Alƙalin Alƙalan ƙungiyar NATO reshen Jihar Katsina, Injiniya Maharazu Sani (Mai Fenti) a Kamfaninsa. A yayin ganawar, bangarorin biyu sun tattauna muhimman batutuwan haɗin gwiwa, kyautata alaƙa da kuma hanyoyin da za su amfani jam'iyyar ta ADC.

A ci gaba da ziyarce-ziyarcen, forum ɗin har wayau ya kai ziyarar girmamawa da dubiya ga mahaifin ɗaya daga cikin mambobinsa kuma abokin gwagwarmayar jam'iyyar, Usman Safiyanu Masari. Tawagar ta yi wa dattijon fatan alheri, tare da addu'ar Allah Ya ƙara masa lafiya da tsawon rai.

A ƙarshe, 'ADC Aspirants and Candidates Forum' ta tuke da kai ziyarar ta'aziyya ga Mataimakin Shugaban Jam'iyyar ADC na karamar hukumar Katsina, Hon. Umar Karoni, bisa rasuwar matarsa. Mambobin tawagar sun miƙa saƙon alhini da jajantawa ga iyalan mamaciyar, tare da yin addu'ar Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta mata kurakuranta, Ya yalwata kabarinta, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarta. Haka kuma sun roƙi Allah Ya ba wa mijinta da sauran iyalanta haƙurin jure wannan babban rashi.

Forum ɗin ya jaddada wa Katsina Times cewar irin waɗannan ziyarce-ziyarcen na daga cikin manufofinsa na ƙarfafa zumunci, gina haɗin kai, kyautata alaƙa tsakanin shugabanni da mambobin jam'iyyar, tare da tabbatar da cewa ADC ta kasance jam'iyya mai haɗin kai da shirin tunkarar zaɓukan 2027 cikin ƙarfi da tsari.

Adc Katsina State House of Assembly Aspirant at malunfashi
22/07/2026

Adc Katsina State House of Assembly Aspirant at malunfashi

19/07/2026

Available

11/07/2026

Kungiyar A.B.K SUPPORT AND MOBILIZATION FORUM kungiyace mai hoyan bayan dan takarar Gwamnan jam’iyyar ADC Sen. Ahmed Babba, ta kaima Dr zayyana Shehu ziyara

07/07/2026

HON. ABDULRASHEED EL-KASIM unity cup

Jam'iyyar ADC a Katsina Ta Rufe Baraka Shafin Zaben 2027*TAFI KWABO TV**Katsina, Nigeria*A ci gaba da yunƙurin ƙarfafa h...
06/07/2026

Jam'iyyar ADC a Katsina Ta Rufe Baraka Shafin Zaben 2027

*TAFI KWABO TV*

*Katsina, Nigeria*
A ci gaba da yunƙurin ƙarfafa haɗin kai da kuma daƙile duk wata baraka da ka iya shafar shirye-shiryen jam'iyyar gabanin zaɓen 2027, Ƙungiyar masu neman tikitin takarar kujerun Majalisar Dokokin Jihar Katsina a ADC (**Aspirants and Candidates Forum**) ta kai ziyarar girmamawa ga ɗaya daga cikin fitattun jiga-jigan jam'iyyar, **Sanata Sadiq 'Yar'adua.

Manufar Wannan Ziyara

Ziyarar dai na daga cikin jerin ganawa da shugabanni da masu ruwa da tsaki da ƙungiyar ke gudanarwa domin:
* Neman shawarwari da gina fahimtar juna.
* Samar da ingantaccen yanayin siyasa gabanin 2027.

* Tabbatar da an shiga zaɓe cikin haɗin kai da ƙarfi guda.

> **Sakataren Ƙungiyar, Muhsin Gambo Lawal Dutsin-Ma:**
> "Mun yanke matsayar cewa duk wanda ya samu tikiti za mu mara masa baya. Waɗanda ba su samu ba kuma za mu ci gaba da bada gudummuwar aiki domin tabbatar da nasarar jam'iyyar a kowane mataki. An kafa forum ɗin ne domin ƙarfafa wa mambobi gwiwar rungumar sakamakon zaɓen fidda gwani cikin lumana."
>
> **Shugaban Ƙungiyar, Hon. Abdurrazaq Dahiru Kaita:**
> "Babban manufar forum ɗin ita ce kare martaba da mutuncin jam'iyyar, da kuma magance rikice-rikicen da s**a kunno kai musamman bayan zaɓen fidda gwani. Za mu riƙa lallashin waɗanda ba su samu tikiti ba domin su zauna a jam'iyya."
>
# # # 🏛️ Jawabin Sanata Sadiq 'Yar'adua
A nasa ɓangaren, Sanata Sadiq 'Yar'adua ya yaba da wannan yunƙuri, yana mai jaddada cewa **haɗin kai shi ne ginshiƙin samun nasara** a kowace jam'iyya.
* **Kan Rikice-rikice:** Ya nuna damuwarsa kan yadda rashin jituwa ke raunana jam'iyya, kuma ya yi alƙawarin bayar da goyon baya don daidaita kowane sabani.
* **Adalci da Gaskiya:** Ya jaddada cewa zai ci gaba da tsayawa tsayin daka wajen kare gaskiya a jam'iyyar.
* **Kiran Gari:** Ya yi kira da a guji siyasar rarrabuwar kai, yana mai cewa kowane mamba yana da muhimmanci a ADC.
> *"Kowane mutum yana da rawar da zai taka a wannan jam'iyya. Nasara ba ta samuwa da rarrabuwar kai, sai da haɗin kai, girmama juna da kuma ba kowa damar bayar da gudummawarsa. ADC tamu ce gaba ɗaya."* – Sanata Sadiq 'Yar'adua.

Ziyarar ta kammala cikin yanayi na fahimtar juna, inda ɓangarorin biyu s**a jaddada aniyarsu ta gina ingantaccen tsari da zai kai jam'iyyar ADC ga gagarumar nasara a babban zaɓen shekarar 2027 a Jihar Katsina.

04/07/2026

unity cup babanta

Address

GRA
Katsina
82L77

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when TAFI KWABO TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share

Category