Maigora social media hausa TV

  • Home
  • Maigora social media hausa TV

Maigora social media hausa TV Kiwon lafiya ga mutanen Maigora

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bai wa babban bankin ƙasar umurnin sake fito da tsofaffin takardun naira 200 domin...
16/02/2023

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bai wa babban bankin ƙasar umurnin sake fito da tsofaffin takardun naira 200 domin a ci gaba da mu'amala da su a ƙasar har nan da kwana 60.

BREAKING NEWS....Kotun Ƙolin Najeriya ta ɗage zaman sauraren shari'ar da wasu gwamnonin jihohin kasar s**a shigar zuwa r...
15/02/2023

BREAKING NEWS....Kotun Ƙolin Najeriya ta ɗage zaman sauraren shari'ar da wasu gwamnonin jihohin kasar s**a shigar zuwa ranar Laraba 22 ga watan Fabarairu.

Allah kabamu sa,a darabo Mai amfani

Daga yau Laraba Zuwa Ranar Juma'a CBN Za Ta Fara Karbar Tsoffin Kudi Tana Turawa Mutane Zuwa Ga BankinsuDaga Comr Abba S...
15/02/2023

Daga yau Laraba Zuwa Ranar Juma'a CBN Za Ta Fara Karbar Tsoffin Kudi Tana Turawa Mutane Zuwa Ga Bankinsu

Daga Comr Abba Sani Pantami

Bayan umurnin rufe karbar tsoffin kudi da CBN tayi ta fitar da sabon tsarin da duk wani mai tsoffin kudi zai shigar da kudinshi ba tare da yayi asararsu ba.

Ga tsarin kamar haka; Da farko mutum zaije CBN na garin su tare da Cash din kudinshi sai yayi generating din Reference Code a Portal din CBN din.

Na biyu ya tabbata yana da Account Number a daya cikin bankunan Najeriya.

Na uku ya tabbata yana da BVN number.

Na Hudu ya tabbata ya tafi da katin dan kasa NIN ko Voter's Card ko daya daga cikin manyan ID da ake amfani dasu a Najeriya.

Duk abunda mutum bai Gane ba Insha'Allah idan yaje CBN zai samu cikakken bayani.

CBN ya sanar da cewa za ta karbi tsoffin kudaden ne na tsawon kwanaki uku daga gobe Laraba 15 ga wata zuwa ranar Jumma'a 17 ga wata.

Ina mai bawa al-umma shawara kowa ya daure yaje yakai kudin shi CBN kada mutum yace ai kotu zata tirsasa bankuna su cigaba da karba, abunda ya kamata mu sani shine kotu fa ba ta ajiyan kudi.

In kunne yaji, jiki ya tsira.

A zaman su na jiya, dukkan tsofin shugabannin kasar Najeriya, Gomnoni Shugabannin majalisa da alkalan alkalai na kasar s...
11/02/2023

A zaman su na jiya, dukkan tsofin shugabannin kasar Najeriya, Gomnoni Shugabannin majalisa da alkalan alkalai na kasar sun baiwa shugaba Muhammadu Buhari shawara cewa ya kamataya sauya tsarin chanza Naira; in ma ya tilasta CBN su buga wadatattun kudade, ko su saki tsofin kudaden da s**a amshe daga hannun talakawa.

Ina fata Shugaba Buhari zai ji wannan shawarar, domin ta fi dacewa da halin da muke ciki a yanzu haka. Domi yanzu haka ma su kananan sana'o'i da dama sun riga sun karye sai dai dori.

KA JI RABO:Yayin Da Wasu 'Yan Uwansa Bakaken Fata Ke Auren Tsoffin Matan Turawa, Shi Kuma Wannan Matashi Dake Aikin Gadi...
04/02/2023

KA JI RABO:Yayin Da Wasu 'Yan Uwansa Bakaken Fata Ke Auren Tsoffin Matan Turawa, Shi Kuma Wannan Matashi Dake Aikin Gadi A Kasar Amurka Ya Auri Tsaleliyar Baturiya

Shugaba Múhammadú Buharí Ya Roƙì Ƴan Nájerìya Da Sú Rínƙa Godewa AllahShúgaban Yace A Ƙasashe Masú Maƙwabtaka Da Nájeriy...
31/01/2023

Shugaba Múhammadú Buharí Ya Roƙì Ƴan Nájerìya Da Sú Rínƙa Godewa Allah

Shúgaban Yace A Ƙasashe Masú Maƙwabtaka Da Nájeriya, Saú Ɗaya Aké Cín Abincí.

Yace zagayen Da Aka Yí Da Shí A Jìhar Kanó A Jìrgìn Sama Ya Ga Manyan Ayyukan More Rayúwa Da Súka Tabbatar Da Céwa Ƴan Nájerìya Ná Shan Jar Miya.

Mé za kúce ?

Munyi karo da wani labari na wata mata ta yi matukarmamaki a ranar auren danta, yayin da ta gano cewa asheamaryar ’yarta...
30/01/2023

Munyi karo da wani labari na wata mata ta yi matukar
mamaki a ranar auren danta, yayin da ta gano cewa ashe
amaryar ’yarta ce wacce ta bace tun shekara 20 baya.
Hakan ya sa mahaifiyar amaryar wacce a rashin sani ta kusa
ta zamar mata surika s**a fara zubar da hawaye, ita da
amaryar da angon, tun bayan da s**a gano cewa ita ce
’yarta wacce ta bace da dadewa kuma yanzu take auren
danta.
An dai gudanar da wannan bikin ne a garin Suzhou, da ke
lardin Jiangsu na kasar China a ranar 31 ga watan Maris.Sabuwar surikar ta gano ’yar tata ce a lokacin da ake cikin
tsakiyar biki, inda ta tabbatar da ’yarta ce ta hanyar gano irin
hannunta, kamar yadda kafar yada labarai ta Times Now
News ta ruwaito.
Ita dai wannan matar ta fuskanci wadanda suke ikirarin su
ne iyayen amaryar, sannan ta tambaye su ko su ne masu
rainon amaryar, sai ’yan uwan amaryar s**a yi mamakin
tambayar da mahaifiyar ke yi masu, duk da yake labari ne
mai tsawo.
Daga nan sai s**a fara bayyana abin da ya faru da amaryar
tun tana jaririya kamar haka: “Wadanda s**a raini amaryar
sun ce, sun tsinci jaririya a gefan hanya, sai s**a dauke ta
suna rainonta har ta girma. Kuma sun raine ta kamar ’yar da
s**a haifa.”
Ita dai wannan batacciyar yarinya ta bayyana yadda ta yi
murnar haduwarta da mahaifiyarta fiye da murnar ranar
bikinta.
Bayan ta gano abin da ya faru, sai ta nuna damuwarta game
da auren, duk da yake shi ma angon dan riqo ne, inda ta
karkata ga dan uwan nata.
Angon ya bayyana aniyarsa na auren matarsa kuma ya ce,
ba wani dalili na sauya kudirinsa.
A bangaren mahaifiyar, ta ce ba wata matsala a auren tun
da ba ’yan uwa ba ne na jini domin kuwa shi ma angon dan
riko ne da aka dauko tun yana karami.
kada kumanta kudinga muna share na post inmu zuwa ga
abokaninku domin bamu qwarin guiwar kawomaku
ingantattin sahihun labaran duniya a cikin harshen hausa
dana turanci mungode da ziyartar shafin KuryaLoaded.ng
dakunkayi

Ku kawo mana karin magana uku masu alaƙa da gatari.
25/01/2023

Ku kawo mana karin magana uku masu alaƙa da gatari.

DA DUMIDUMINSA: Sheikh Dahiru Bauchi Ya Goyi Bayan Atiku A Zaben 2023Mai Girma Wazirin Adamawa Alhaji Atiku Abubakar ya ...
24/01/2023

DA DUMIDUMINSA: Sheikh Dahiru Bauchi Ya Goyi Bayan Atiku A Zaben 2023

Mai Girma Wazirin Adamawa Alhaji Atiku Abubakar ya ziyarci Babban Malamin Addinin Musulunci a Nijeriya, Sheikh Dahiru Bauchi da Sheikh Shariff Saleh Ibrahim, a yayin ziyarar sun bayyana goyon bayan su ga Atiku Abubakar, a matsayin shugaban kasar Najeriya da ya kamata 'yan Najeriya su zaba a zabe mai zuwa.

Daga Kungiyar Arewa Bloggers For Atiku.

Wallahi na kusa zama Dan bindiga ~ Dan Hausa,Wani matashi a kafar Tik-tok mai suna Real Dan hausa ya bayyana  a cikin wa...
23/01/2023

Wallahi na kusa zama Dan bindiga ~ Dan Hausa,

Wani matashi a kafar Tik-tok mai suna Real Dan hausa ya bayyana a cikin wani matsakaicin faifayin video inda a jiyo shi yana cewa, naje banki ba sau daya ba, ba sau biyu ba, amma sun hana mutane Sanya kudi,

Ga ni da kudi na har naira dubu dari uku, wallahi matukar nayi asarar wannan kudin har lokacin dena karbon su yayi, toh wallahi zan koma Dan fashin daji, Zan tattara kayana na zama Dan Garkuwa da mutane,

Ya bayyana yadda gwamnati bata son Alumma su zama masu neman halal, ya bada wa'adin lokaci, matukar yayi asarar kudinsa ya bayyana cewa zai hada kai da masu garkuwa da mutane,

Jama'a ina mafita ?

Masha Allah,, Masha Allah
20/01/2023

Masha Allah,, Masha Allah

19/01/2023

*SANARWA ! SANARWA !!*

Kai Tsaye Dan Uwa ko Yar uwa Kuyi kokari ku sanarda Yan uwa na Kyauye A Fadarkarda kowa yaro da Babba Tsofaffi da Sukeyin Asusu( Dan Banki) A sanar dasu suyi kokari Sukai kudinsu Bank ko Kuma Sukai wajen Yan kasuwa kusa dasu su Sayi Wani Abu

Abinnan Ana kallonsa wasa-wasa Walh Mutane zasusha Mamaki zaka wayi safiya kawai kaje sayen Wani Abu Sai ace Ba'a karbar wannan

Mafi yawan Yan kasuwa Zasu Dena Karba 20 zuwa 25/01/2023

Mu Fadakarda Yan uwanmu Na kyauye

Falau Gwada-bawa

18/01/2023
Akwai wata tsohuwar dabara da gurbatattun yan siyasa da yan koren su ke amfani da ita domin kauda hankalin mutane daga b...
18/01/2023

Akwai wata tsohuwar dabara da gurbatattun yan siyasa da yan koren su ke amfani da ita domin kauda hankalin mutane daga barnar su. A falsafa ana kiran wannan dabara da “false equivalence”.

Ta’arifin wannan dabara shine; idan dan siyasa ya tafka barna wadda yake ganin ba shida mafita a cikin ta, to sai ta danne tashi barnar sai ya koma nuni ga barbar da wanin sa yayi.

Kuma kasancewar ba kowa ne zai iya halarto cewa “two wrongs don’t make a right” ba, ma’ana, laifi biyu basa zama dai-dai , sai hakan ya zama ya rage tasirin barnar wannan dan siyasa domin hankalin mutane baya kai.

Misali, idan nace maka Ganduje yayi ba dai-dai ba, kai kuma a kokarin bani amsa sai kace min ai Kwankwaso ma yayi barna, to me kayi kenan? Wannan shi ake kira “false equivalence”. Idan Kwankwaso yayi laifi ya kare kansa. Kai ma ka kare kan ka ba tare da nuni ga laifin Kwankwaso ba. Saboda laifi biyu basa zama dai-dai.

Magana ake yi ta wanda ke mulkin Kano yanzu, da kuma zabi tsakanin ci gaba da irin wannan mulkin, ko kuma samun canji. Saboda haka mu kano ce a gaban mu ba mutane ba.

DA DUMI DUMIN SA jarumin barkwanci Wanda akafi sani da suna hudu mazaje ne yace yadainayin harkar film daga yanzu insha ...
18/01/2023

DA DUMI DUMIN SA jarumin barkwanci Wanda akafi sani da suna hudu mazaje ne yace yadainayin harkar film daga yanzu insha allahu

Wane fata zakuyi masa

17/01/2023

Haryanzu jihar katsina
Yankin karamar hukumar faskari
matsalar tsaro sai Kara ta,azzara take Allah ka kawo Mana sauki

Innanillahi wa,inna,ilaihirraju,unAllah Ya Yiwa Fitaccen Ɗan Wasan Barkwanci Maisuna Kamal Aboki Rasuwa Sakamakon Hatsar...
16/01/2023

Innanillahi wa,inna,ilaihirraju,un

Allah Ya Yiwa Fitaccen Ɗan Wasan Barkwanci Maisuna Kamal Aboki Rasuwa Sakamakon Hatsarin Mota.

Allah yajikansa da rahama yasa aljanna ce makomar sa Ameen

16/01/2023

Masoya kuzo muyi salati tare da Ambaton Annabi Muhammadu ﷺ

Address


Telephone

+2348121422558

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Maigora social media hausa TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share