Sheikh Ibrahimul Khaleel Ɗandume Foundation And Media

Sheikh Ibrahimul Khaleel Ɗandume Foundation And Media Khalilawa Family Bazasu Taba Tabewa Ba Sabida Sun Rike Allah
(1)

A Cikin Wannan Dare Mai Tsananin Fari, A Kuma Wannan Rana Mai Tsananin Haske, Ku Mu Yi Salati Ga Wanda Yake Riƙe Da Tuta...
23/10/2025

A Cikin Wannan Dare Mai Tsananin Fari, A Kuma Wannan Rana Mai Tsananin Haske, Ku Mu Yi Salati Ga Wanda Yake Riƙe Da Tutar لواء الحمد Kuma Mamallakin Alkausara Sayyiduna Muhammad ﷺ

اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى سَيِّدِنَا مُحَمَّدٍ الفَاتِحِ لِمَا أُغْلِقَ وَالخَاتِمِ لِمَا سَبَقَ نَاصِرِ الحَقِّ بِالحَقِّ و الهَادِي إلى صِرَاطِكَ المُسْتَقِيمِ و عَلَى آلِهِ حَقَّ قَدْرِهِ و مِقْدَارِهِ الْعَظِيمِ ٠ صلاة تفتح لنا بها ابواب الخير والتيسير وتغلق بها عنا ابواب الشر والتعسير وتكون لنا بها ولياً ونصير يا نعم المولى ونعم النصير. آمين يا رب 🤲

Allah Ya Ƙara Mana Son Annabi ﷺ 🤲🥰

MANZON ALLAH ﷺ Ya Kasance A Lokacin Damuwa (Baƙin Ciki) Yana Cewa: «لاَ إِلَهَ إِلَّا اللَّهُ العَظِيمُ الحَلِيمُ، لاَ إ...
23/10/2025

MANZON ALLAH ﷺ Ya Kasance A Lokacin Damuwa (Baƙin Ciki) Yana Cewa:

«لاَ إِلَهَ إِلَّا اللَّهُ العَظِيمُ الحَلِيمُ، لاَ إِلَهَ إِلَّا اللَّهُ رَبُّ العَرْشِ العَظِيمِ، لاَ إِلَهَ إِلَّا اللَّهُ رَبُّ السَّمَوَاتِ وَرَبُّ الأَرْضِ، وَرَبُّ العَرْشِ الكَرِيمِ»

Wannan Addu'ar Idan Bawa Yana Cikin Damuwa Yana Karanta Ta Zai Samu Mafita Da Kuma Yayewa.

Alfarmar Wannan Addu'a, Da Annabin Da Aka Aiko Da Alƙur'ani Ya Isar Kuma Ya Yi Umurni Ga Duk Wanda Ya Ji Cewa Ya Isar, Allah Ka Yaye Mana Damuwar Mu Da Dukkan Baƙƙan Cikin Mu 🤲 Allah Ka Bamu Mafita Cikin Dukkan Al’amuran Mu 🤲

Allah Ya Ƙara Mana Son Annabi ﷺ 🤲💞

MANZON ALLAH ﷺ YA CE:Wanda Ya Bi Ni, To Haƙiƙa Ya Bi Allah. Wanda Kuma Ya Saɓa Mani, Haƙiƙa Ya Saɓa Ma Allah. Wanda Ya B...
22/10/2025

MANZON ALLAH ﷺ YA CE:

Wanda Ya Bi Ni, To Haƙiƙa Ya Bi Allah. Wanda Kuma Ya Saɓa Mani, Haƙiƙa Ya Saɓa Ma Allah. Wanda Ya Bi Ameery Na (Dukkan Wani Mai Jiɓintar Al'amuran Musulmai Kuma Yake Musu Aiki Da Abin Da Annabi ﷺ Ya Shar'anta) To Haƙiƙa Ya Bi Ni. Wanda Kuma Ya Saɓa Wa Ameeny Na To Haƙiƙa Ya Saɓa Mani.

صدق رسول الله صلى الله عليه وسلم.

Allah Ka Bamu Cikakkiyar Damar Yi Wa Magadan Annabin Ka ﷺ Biyayya Don Risƙuwa Da Shi Yana Mai Yi Mana Bishara Da Gamuwa Da Kai Muna Masu Dacewa 🤲

Allah Ya Ƙara Mana Son Annabi ﷺ 🤲

Faɗin cewa Salatul Fatih tafi Al-Qur’an daraja, magana ce da babu wani Musulmi da zai faɗa. Salatul Fatih ma ba ta kai h...
15/10/2025

Faɗin cewa Salatul Fatih tafi Al-Qur’an daraja, magana ce da babu wani Musulmi da zai faɗa. Salatul Fatih ma ba ta kai harafi guda daga cikin Al-Qur’an ba.

Amma abin da ake kwatanta shi a nan shi ne: Lada ko sakamakon wanda yake karatun Al-Qur’an amma baya kiyaye ladubansa, baya aiki da hukuncinsa, baya tafiya bisa shiryarwarsa, yana zaluntar kansa, da kuma lada na wanda yake yawaita salati ga Annabi ﷺ a kowace irin siga. Ga irin wannan mutum, wannan aiki wato (yin salati ga Annabi ﷺ) yafi karatun Al-Qur’ān wanda baya aiki da shi. Kamar yadda Ibn Mas‘ud ya ce: Yaya masu karatun Al-Qur’ān da yawa, amma Al-Qur’ān yana la’antar su.

Saboda haka, duk wanda yake son danganta wani magana da mutanen hanyar Tijaniyya, ya tabbatar da bincike sosai. Ba a taɓa cewa Shaykh, Allah ya yarda da shi, ya kwatanta Salatul Fātiḥ da Al-Qur’ān kai tsaye ba. Abin da ya kwatanta kawai shi ne lada tsakanin wanda yake karatun Al-Qur’ān ba tare da aiki da shi ba, da kuma wanda yake yin salati ga Annabi ﷺ yana aiki da abin da Al-Qur’ān ya koyar.

Don haka ka koma ga wannan fahimta, ka yi tunani a kai, ya Ɗan’uwa. Amma maganar cewa Salatul Fātiḥ tafi Al-Qur’ān, ko cewa tana cikin Al-Qur’ān, duk waɗannan magana ce ta ƙarya.”

— Sheikh Sharif Ibrahim Saleh.
“Kashf al-Ghumūt wa Iẓālat al-Ilbās”

~Ibrahim Khaleel Sinikom ✍️
__________________________________

Wannan Kenan. Allah Ya Sa Mu Dace 🤲
Allah Ya Ƙara Mana Son Annabi ﷺ 🤲🥰

DAGA ZANTUKAN SHEIKH IBRAHIM NIASSE {RADHIYAL-LAHU ANHU}Wata Rana, Annabi ﷺ Yana Zaune Tare Da Sahabban SaSai Ya Ce Musu...
15/10/2025

DAGA ZANTUKAN SHEIKH IBRAHIM NIASSE {RADHIYAL-LAHU ANHU}

Wata Rana, Annabi ﷺ Yana Zaune Tare Da Sahabban Sa

Sai Ya Ce Musu: Yanzu Wani Zai Zo, Kuma Shi Yana Cikin Ƴan Aljannah.

Sai Abdullahi Bin Sulãmin Ya Zo. Bayan Ya Fita Daga Mazaunin Annabi ﷺ Sai Wasu Daga Cikin Sahabbai S**a Bi Shi Gida Suna Mamakin Shi.

Sai S**a Tambaye Shi: Shin Wane Aiki Kake Yi Da Har Ka Samu Shaidar Annabi ﷺ Cewa Kai Ɗan Aljannah Ne?

Sai Abdullahi Ya Ce Masu: Duk Abin Da Nake Yi Shi Kuke Yi. Sedai Kuma Ni Ina Da Wata Ɗabi’a Guda Ɗaya, A Duk Sanda Rana Ta Hudo (Wayewar Garin Ko Wace Rana) To Wani Mugun Ƙudiri A Kan Wani Muslimi Baya Zamowa A Cikin Zuciyata. (Ma'ana: Bana Wayar Gari Da Mugun Ƙudiri A Kan Wani Muslimi Cikin Zuciyata)

Sai S**a Ce: Saboda Haka Ne Ka Samu Shaidar Annabi ﷺ.

Domin Allah Subhanahu Wa Ta'ala Yana Cewa:
﴿يوم لا ينفع مالٌ ولا بنونٌ إلاّ من أتى الله بقلب سليم﴾
Ma'ana “Ranar Da Dukiya Ko Ƴaƴa Baza Su Amfani Mutum Da Komai Ba, Sai Wanda Ya Zo Ma Allah Da Lafiyayyar Zuciya”

Sheikh Ibrahim Niasse Ya Ce “Irin Wannan Zuciyar Ta Abdullahi Bin Sulãmin Ita Ce Lafiyayyar Zuciya.

Allah Ka Gyara Mana Zukatan Mu Daga Hiƙdu Da Ƙulla Sharri Ko Makirci 🤲

Allah Ka Ɗaure Zuciyar Mu Da Ambaton Ka Da Soyayyar Ka Da Ta Annabin Ka ﷺ

Allah Ka Ƙarawa Annabi ﷺ Daraja 🤲

10/10/2025
Me Ka Sani Game Da Sheikh Ibrahimul Khaleel Ɗandume?
08/10/2025

Me Ka Sani Game Da Sheikh Ibrahimul Khaleel Ɗandume?

*Maulana Mai Gyaran Zuciyata Mai Saita Man Hanya Lokacin Da Duniya Tayi Man Duhu Shike Zamowa Fitllata Mai Haskenda Yake...
08/10/2025

*Maulana Mai Gyaran Zuciyata Mai Saita Man Hanya Lokacin Da Duniya Tayi Man Duhu Shike Zamowa Fitllata Mai Haskenda Yake Haska Man Ko Mai Jagorana A Lokacin Da Na Rasa Hanyar Bi Abin Tunawata A Lokacin Da Ko Mai Ya Dauke Daga Tunanina*
*Shidin Tafiyata Ne Zama Nane Shiru Nane Magana Tane Zance Nane Tsayuwata Ne Kuka Nane Farin Ciki Nane Ko Mai Nane*
*Allah Ka Warama Maulanmu Shehu Ibrahimul Khaleel Ddm Yarda Ka Barmu Da So Yayyarshi Da Yin Biyayya A Kan Abinda Yayi Mana Nuni Dashi Na Al Khairi Da Kuma Gujema Abinda Ya Hanemu Dashi Na Sharri Allah Mun Godema Ka Santuwarmu A Qar Qashinshi Allah Ka Qara Ma Annabi Muhammad S a.w Daraja

مدرسة الأنصار العملية طندمي إعلان عن فتح باب القبول والتسجيلتسرُّ مدرسة الأنصار العملية الجديدة – طندمي أن تُعلن عن فتح ...
02/10/2025

مدرسة الأنصار العملية طندمي
إعلان عن فتح باب القبول والتسجيل

تسرُّ مدرسة الأنصار العملية الجديدة – طندمي أن تُعلن عن فتح باب القبول في مرحلة الحضانة، والابتدائي، وقسم تحفيظ القرآن الكريم.

📖 في مدرستنا:

نُدرِّس جميع المواد المطلوبة في مرحلتي الحضانة والابتدائي.

نُقدِّم دروس اللغة العربية بتوجيهٍ سليم.

نُوفِّر برنامج تحفيظ القرآن الكريم مع تحسين التلاوة.

نُربِّي الأطفال على الانضباط والأخلاق الحميدة.

نمنح ولدك نعمة الجمع بين التعليم العصري والمعرفة الإسلامية.

📍 العنوان: عبدالله يارو – مقابل المحكمة الشرعية – طندمي – ولاية كاتسينا
📞 للتواصل:
• شمس لوال قربابا– 08130697885
• حبيب خليل – 08062268042

The New Al-Ansar Pragmatic School, Dandume – Admission OpenThe new Al-Ansar Pragmatic School, Dandume is glad to announc...
02/10/2025

The New
Al-Ansar Pragmatic School, Dandume – Admission Open

The new Al-Ansar Pragmatic School, Dandume is glad to announce that admission is now open into Nursery, Primary and Qur’ān Memorization (Hifz) Section.

📖 At our school:

We teach all subjects required at nursery and primary levels.

We offer Arabic language lessons with proper guidance.

We provide Qur’ān memorization (Hifz al-Qur’ān al-Karīm) with correct recitation.

We nurture children with discipline and good morals.

Give your child the gift of both modern education and Islamic knowledge.

📍 Address: Abdullahi Yaro Opp. Sharia Court, Dandume, Katsina State
📞 Contact:
• Shamsu Lawal Qarbaba – 08130697885
• Habibu Khalil – 08062268042

🏫         Al-Ansar Pragmatic School, DandumeSabuwar Makarantar Al-Ansar Pragmatic School, Dandume, tana sanar da ku, ta ...
02/10/2025

🏫
Al-Ansar Pragmatic School, Dandume

Sabuwar Makarantar Al-Ansar Pragmatic School, Dandume, tana sanar da ku, ta buɗe sabon zangon karatu ga yara a matakin, nursiry, firamare da kuma sashen Haddar Al-Qur’ān Mai girma.

📖 A makarantar :

Ana koyar da dukkan darussa da ake koyarwa a matakin nursiry da firamare.

Ana koyar da Larabci cikin sauki da ƙa’ida.

Ana koyar da Haddar Al-Qur’ān Mai girma, tare da ingantaccen lafazi.

Ana tarbiyyantar da yara cikin ladabi da biyayya.

Ku kawo ‘ya’yanku ku more ingantaccen ilimi na zamani da na addini.

📍 Adireshi: Abdullahi Yaro Opp. Sharia Court, Dandume, Katsina State
📞 Lambar tuntuɓa:
• Shamsu Lawal Qarbaba
08130697885
• Habibu Khalil
08062268042

Allah Kar Ka Saka Mu Cikin Masu Taɓa Darajar Annabi ﷺ 🤲
30/09/2025

Allah Kar Ka Saka Mu Cikin Masu Taɓa Darajar Annabi ﷺ 🤲

Address

Khalilawa Street
Katsina

Telephone

+2349166020990

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sheikh Ibrahimul Khaleel Ɗandume Foundation And Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Sheikh Ibrahimul Khaleel Ɗandume Foundation And Media:

Share