FTNews

FTNews FTNews kamfanine da yake kawo maku sahihai kuma ingantattun labarai daga kowane bangare a cikin jihohi da yankuna na Nigeria dama kasashen ketare

DA DUMI-DUMI: ‘Yan Sanda Sun Karya Wa Sowore Hannunsa na Dama, Sun Kuma Tura Shi Wani Wuri da Ba a Bayyana ba a AbujaRah...
07/08/2025

DA DUMI-DUMI: ‘Yan Sanda Sun Karya Wa Sowore Hannunsa na Dama, Sun Kuma Tura Shi Wani Wuri da Ba a Bayyana ba a Abuja

Rahotanni daga jaridar Sahara Reporters sun tabbatar da cewa da misalin ƙarfe 6:00 na safiyar yau, wata tawagar ‘yan sanda ƙarƙashin jagorancin wani CSP daga sashen sa-ido na Sufeto Janar na ‘Yan Sanda (IGP Monitoring Unit) sun kutsa cikin ɗakin tsarewar Omoyele Sowore da ke hedkwatar FID a birnin tarayya, Abuja.

A yayin wannan kutse, jami’an sun yi amfani da ƙarfin tsiya, inda s**a karya hannun daman Sowore, kafin daga bisani su ɗauke shi zuwa wani wuri da har yanzu ba a bayyana ba.

"Abin mamaki ne yayin da miliyoyin ‘yan Nijeriya ke cikin matsananciyar yunwa, amma shugaba Tinubu ya ware Naira biliyan...
07/08/2025

"Abin mamaki ne yayin da miliyoyin ‘yan Nijeriya ke cikin matsananciyar yunwa, amma shugaba Tinubu ya ware Naira biliyan 712 dan gyaran filin jirgin saman Legas" Inji Peter Obi.

Obi ya ƙara da cewar, ciyar da mutane yakamata a yi tukunna kafin gyaran Filin jirgi.

07/08/2025

Tsira Aminci Daraja Martaba Matsayi Girmamawar Allah su kara tabbata ga Mai Salsabilu da tafkin Alkausara
MUHAMMAD RASULULLAH

Mafi yawancin ƴan siyasar Najeriya basu da tarbiyya--Sarkin Kano SunusiSarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya bayyan...
06/08/2025

Mafi yawancin ƴan siyasar Najeriya basu da tarbiyya--Sarkin Kano Sunusi

Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya bayyana cewa babban dalilin da ke janyo yawaitar cin hanci da rashawa a Najeriya shi ne rashin tarbiyya tun daga tushe, musamman a tsakanin 'yan siyasa da masu rike da madafun iko.

A wata hira da aka yi da shi a cikin shirin Politics Today na Channels TV a daren Laraba, Sanusi ya ce yawancin masu mukaman gwamnati sun hau kujerar ne ba bisa kwarewa ko kishin kasa ba, sai dai don wata manufa ta kansu.

“Da yawa daga cikin masu rike da mukamai ba su da tarbiyyar gaskiya da rikon amana,” in ji shi. “Yawanci sun shiga gwamnati ne saboda dalilai na son zuciya.”

Sarkin ya ce halayen kirki da darajar da al’umma ke mutunta su sun dusashe gaba ɗaya. Ya ce: “Yanzu marasa tarbiyya ne ke mulkar kasar; mutane da ba su da abin alfahari kuma ba su da niyyar barin wani abin kwatance bayan sun tafi.”

Sanusi ya kuma bayyana damuwarsa kan yadda mutane ke fifita dukiya da jin daɗi fiye da mutunci da nagarta.

“Mutane suna alfahari da dukiyar da s**a tara, irin su gidaje da jiragen sama, amma ba sa tunanin yadda al’umma ke kallon su a matsayin ɓarayi,” in ji shi.

Ya kara da cewa matsalar ba ta tsaya ga shugabanni kadai ba, hatta sarakuna da malamai da ke jan ragamar jagoranci sun fada cikin ruɗani.

“Ko shugabannin addini sun ruɗe, haka ma sarakuna. Kusan kowa ya fada tarkon wannan ruɗanin,” in ji shi.

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Ma’aikatan Lafiya 70,000 Kafin Shekarar 2029Gwamnatin Tarayya ta bayyana shirin daukar ma’...
06/08/2025

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Ma’aikatan Lafiya 70,000 Kafin Shekarar 2029

Gwamnatin Tarayya ta bayyana shirin daukar ma’aikatan lafiya 70,000 nan da shekarar 2029, domin inganta tsarin kula da lafiyar al’umma da rage gibin ma’aikata a yankunan da ke da karancin asibitoci.

Shugaban Hukumar NPHCDA, Dr. Muyi Aina, ya bayyana cewa an tsara shirin ne domin a samu ma’aikacin lafiya ɗaya ga kowanne gida 250, don saukaka rigakafi, wayar da kai, da sa ido kan cututtuka a tsakanin sama da 'yan Najeriya miliyan 160.

Shirin zai haɗa da horarwa, kayan aiki, da goyon bayan fasaha, inda jihohi takwas da s**a haɗa da Bauchi, Borno, Kaduna, Yobe da Zamfara s**a riga sun amince da tsarin.

Wakiliyar UNICEF a Najeriya, Ms. Wafaa Saeed Abdelatef, ta yaba da shirin, tana mai cewa hakan zai taimaka wajen kai rigakafi ga yara da ba a kai musu ba, tare da tallafawa burin Tarayyar Afirka na ma’aikatan lafiya miliyan biyu kafin 2030.

Shugabannin Africa CDC sun ce ma’aikatan lafiya na unguwanni sune ginshikin kiwon lafiya ta kowa da kowa, kuma za su ci gaba da haɗin gwiwa da gwamnatocin Afirka don tabbatar da cewa ba a bar wata al’umma a baya ba.

HOTUNA 📸Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda PhD,CON, a birnin Riyadh na ƙasar Saudiyya.
06/08/2025

HOTUNA 📸Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda PhD,CON, a birnin Riyadh na ƙasar Saudiyya.

Sabuwar Jakadiyar Zaman Lafiya ta Majalisar Ɗinkin Duniya kenan Maryam Bukar Hassan wadda aka fi sani da Alhanislam yayi...
06/08/2025

Sabuwar Jakadiyar Zaman Lafiya ta Majalisar Ɗinkin Duniya kenan Maryam Bukar Hassan wadda aka fi sani da Alhanislam yayin da ta samu kyakyawar tarba a ofishin Majalisar da ke Najeriya bayan ta dawo daga Amurka inda aka karramata a makon jiya. Yayin ziyarar, ta samu ganawa da ma’aikatan Majalisar da ke ofishin tare da wasu matasa in da ta ƙarfafa musu gwiwa tare da bada labarin yadda ta faro gwagwarmayar neman zaman lafiya da kuma inda kai ta a rayuwa.

Shugaba Tinubu Ya Taya Dalibai Uku ‘Yan Arewa Murna Bisa Nasarar Da S**a Samu a Gasar Duniya Ta TeenEagleShugaban Ƙasa B...
06/08/2025

Shugaba Tinubu Ya Taya Dalibai Uku ‘Yan Arewa Murna Bisa Nasarar Da S**a Samu a Gasar Duniya Ta TeenEagle

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Nafisa Abdullahi Aminu mai shekaru 17, Rukayya Muhammad Fema mai shekaru 15, da Hadiza Kashim Kalli murna bisa nasarar da s**a samu a gasar TeenEagle ta duniya da aka gudanar a birnin London, Ƙasar Ingila. Nafisa ce ta lashe kyautar gwarzon daliba a fannin ƙwarewar harshen Turanci, yayin da Rukayya ta zama ta farko a muhawara, Hadiza kuma ta samu kyautar zinariya a matsayin mai hazaka.

Shugaba Tinubu ya jinjinawa waɗannan matasa na Najeriya da s**a ɗaga tutar ƙasa a idon duniya, yana mai cewa wannan nasara alama ce ta hasken makomar ƙasar. Ya kuma yaba da irin gudunmawar cibiyoyin ilimi da gwamnatocin jihohi wajen haɓaka ƙwarewar ɗalibai, yana mai cewa hakan na nuna ingancin tsarin ilimi da ƙasar ke da shi wajen haifar da matasa masu ƙwarewa da basira.

Shugaban ya ƙara jaddada cewa ilimi ginshiƙi ne na ci gaban ƙasa, wanda ya sa gwamnatinsa ke zuba jari a fannin tare da cire ƙalubalen kuɗi ga talakawa masu neman ilimi ta hanyar NELFUND. Ya yi kira ga Nafisa, Rukayya da Hadiza da su ci gaba da jajircewa a karatunsu, yana musu fatan samun karin nasarori a gaba.

Yadda Sheikh Ibrahim Maqari ya sayi wasu casbaha biyu a kan ₦60,000 a AbujaWaɗannan su ne casbaha da Babban Limamin Masa...
06/08/2025

Yadda Sheikh Ibrahim Maqari ya sayi wasu casbaha biyu a kan ₦60,000 a Abuja

Waɗannan su ne casbaha da Babban Limamin Masallacin ƙasa da ke Abuja Sheikh Farfesa Ibrahim Ahmad Maqari kenan yayin da ya yi cinikin wasu casbaha biyu akan Naira dubu 60 a lokacin da ya fito daga gidansa na Abuja kuma ya ci karo da masu sayarwa a kusa da gidansa.

Cikin wani bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta, an jiyo Malamin na taya casbahan ɗaya Naira dubu 40 ɗaya kuma dubu 20 bayan ya bayyana wa masu sayarwa da cewa shi masu tsada ya ke so.

Sai dai wani da abin ya faru a gaban shi har ma ake tunanin ƙila shi ne ya yi bidiyon ya yi baya ni da cewa,Malamin ya sayi casbahan kan wannan farashi ne domin ya tallafa wa masu sana'ar, amma ko shi kansa ya san da cewa ba za su kai wannan kuɗin ba in sun yi tsada a sayesu duka a kan Naira dubu 5.

Hon. Ibrahim Namadi, da ya yi murabus daga kujerar kwamishinan sufuri na jihar Kano, yace yin murabus ɗinsa ba don ya ai...
06/08/2025

Hon. Ibrahim Namadi, da ya yi murabus daga kujerar kwamishinan sufuri na jihar Kano, yace yin murabus ɗinsa ba don ya aikata laifi ba ne, illa dai don kare mutuncin gwamnati da kuma ƙarfafa amincewar jama’a ga tsare-tsaren da ake aiwatarwa.

Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Gusau da Tsafe dake jihar Zamfara Hon. Kabiru Maipalace, ya dauki nauyin gyaran makab...
06/08/2025

Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Gusau da Tsafe dake jihar Zamfara Hon. Kabiru Maipalace, ya dauki nauyin gyaran makabartu guda 80 a kananan hukumomin Gusau da Tsafe da ke fadin jihar.

DA DUMI-DUMIi:- Hukumar Hisbah Reshen Karamar Hukumar Katsina, Ta haramta goyon Mata a gaban Keke-Napep da aka sani da '...
06/08/2025

DA DUMI-DUMIi:- Hukumar Hisbah Reshen Karamar Hukumar Katsina, Ta haramta goyon Mata a gaban Keke-Napep da aka sani da 'yar kurkura a Birnin Katsina.

Address

Katsina

Telephone

+2348099111040

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when FTNews posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to FTNews:

Share