16/03/2026
Bayan tashin Bom a Maiduguri: Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu tare da matarsa Oluremi Tinubu za su bar Abuja ranar 17 ga Maris domin kai ziyara ta ƙasa zuwa United Kingdom, bisa gayyatar King Charles III da matarsa Queen Camilla.
Za a karɓi Tinubu a Windsor Castle daga 18 zuwa 19 ga Maris. Wannan ita ce ziyara ta farko da shugaban Najeriya ya kai irin wannan cikin shekaru 37.