VOICE of Sheikhs

  • Home
  • VOICE of Sheikhs

VOICE of Sheikhs Mun bude wannan cibiya mai suna Muryar shehunanmu domin yada karantarwar Ahlulbayt (A. S) +23480363

MUNA BA ‘YAN UWANMU TABBACIN MUNA NAN DARAM A KAN ABIN DA S**A BAYAR DA JINANANSU A KAI- Inji Jagora Shaikh Ibraheem Zak...
15/12/2024

MUNA BA ‘YAN UWANMU TABBACIN MUNA NAN DARAM A KAN ABIN DA S**A BAYAR DA JINANANSU A KAI

- Inji Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky a taron shekara tara (9) da Waki’ar Buhari ta 2015 da aka yi a Abuja

Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

Da yake jaddada mika ta’aziyarsa ga ‘yan uwa a yayin tunawa da kisan kiyashin Zaria da sojoji s**a yi a shekarar 2015, a ranar Asabar 14 ga watan Disamba 2024, Jagora, Shaikh Ibraheem Zakzaky ya ba da tabbaci ga wadanda aka kashe a lokacin cewa muna nan daram a kan tafarkin da s**a bayar da jinanensu a kai har karshen rayuwarmu.

Jagoran ya mika jajensa da cewa: “Muna jajantawa dukkan iyalan wadanda aka kashe; iyayen da aka kashe musu ‘ya’ya, da ‘ya’yan da aka kashe musu iyaye; da matan da aka kashe musu mazaje, da mazajen da aka kashe musu mata; da ‘yan uwan da aka kashe musu ‘yan uwansu; da masoyan da aka kashe musu masoyansu; da abokanan arziki, duk muna jajanta musu. Sannan muna kara wasiyya ga junanmu da mu daure, jarabawa ce.”

Ya kara da cewa: “Muna ba wadanda s**a sadaukar da ransu, s**a ba da jinanensu, s**a dake a wannan waki’a (ta 12-14 ga Disambar 2015) da waki’o’in da s**a biyo baya sak**akon wannan, muna ba su tabbacin cewa muna nan daram akan abin da s**a bayar da jinanensu, Insha Allah ba za mu canza ba.”

Da yake bayanin waki’ar, Jagora ya bayyana cewa, mahukuntan kasar nan sun dade suna yunkurin dirar wa Harkar Musulunci da nufin kawar da ita. “Sun dade suna tsara abubuwansu (na yunkurin kawar da mu), saboda haka wannan abu tsararre ne. To kuma mun samu wani labari, cewa za a dira mana ranar Asabar 12 ga watan Disamba, kuma lallai mu ake nufi, kuma an gama shirya soja kaf, amma ba a ce musu me za a yi ba.”

Ya bayar da misalan yadda a lokuta daban-daban aka rika kitsa ma soja abubuwa daban-daban da nufin su kawo wa ‘yan uwa hari a lokuta daban-daban, k**ar cewa an sace wani mutum, kuma soja za su kwato shi (a Gyallesu), da cewa an samu labarin (‘yan uwa) za su kitsa juyin mulki kuma soja za su hambare yunkurin. Yace; “amma duk (sojan) ba su san wannan wane aiki ne za su yi ba, har abubuwan su kwaranye.”

Yace: “To wannan karon da Allah Ya tashi tozarta su, sai ba su iya cewa komai ba, sai cewa an tsare hanya. Sai s**a shirya dirama, s**a dauki wasu mutane s**a ba su dubu biyar-biyar s**a zo suna ta ihu. Ihu sosai wanda ba wanda ya san ‘yan uwa da zai ce wadannan ‘yan uwa ne. Mutane gari ma suna cewa wadabbab va ‘yan uwa ba ne, don har sun saka ma taya wuta, wanda yake a tarihinmu na shekara 40 ba mu taba kona taya ba. Kuma sun rike sanduna wanda ba a taba ganinmu da sanduna ba. Har mutanen gari suna cewa wannan ba Shi’a ba ne. Suna ta ihu sun saka bakaken kaya. Inda ma s**a buga kenan, don Asabar din nan wanda ya yi daidai da 12 ga watan Disamba, rannan ne 1 ga watan Rabi’ul Auwal, kuma a rannan za mu canza tuta ne; za mu cire bakin tuta mu saka koriya mai rubutu fari da ‘Labbaika Ya Rasulalllah’, saboda haka rannan ranar farin ciki ne, za a shiga watan Mauludi ne, ba ranar jaje ba ne, saboda haka sun buga da s**a saka bakin kaya. Kuma s**a buga da s**a yi ihu.”

Jagora yace daga baya duk sun kai wadannan bayanan diramar tare hanyar kotunda daban-daban amma kotuna sun tabbatar da ‘yan uwa basu tare hanyar ba. Yace: “Duk sun kai wadannan diraman kotuna, sun ce gashi an tsare hanya ne. To kotuna High Court daban-daban har guda uku a Kaduna, kowannensu yace ba a tsare hanya ba! Ba ma kawai wadanda aka kawo gaban kotu ba su tsare hanya ba, sun ce tsare hanyar ma ba a yi ba! To ina mamakin har yanzu saboda bushewan zuciya, kaga mutum ya kekeshe kasa yace wai abin da ya faru sak**akon wai an tsare hanya ne. Kuma s**a ce an yi barazana ga rayuwar wani mutum wai shi Buratai. To shi ma duk sun kawo wadannan abubuwan a kotu, duk kotu tace ba a haka ba ne.”

Jagora yace: “Mu kaddara an tsare maka hanya, mu kaddara kuma doka ta yi tanadin duk wanda ya tsare ma wani babban mutum hanya kashe shi ake yi. To ya za a yi kisan? Dole a k**a shi a kai shi kotu, kotu ta yanke masa hukunci ko? Ba wanda ya baka dama kawai sai ka harbe mutum, ka zartar da hukuncin, in ma hukuncin hukuncin kisa ne. To kuma idan hukuncin kisa ne, an tsare hanya, kuma kai an baka dama kana iya kashe wa, wanda na san ba za a iya baka wannan damar ba, to me ya hada ka da gyallesu? Me ya kai ka Gyallesu? Ita ma tana hanyar Sakkwato ne? – Don Husainiyyah ita ce No. 1A akan hanyar Sokoto… (da ke Zariya)

“Idan mu kaddara hukuncin wanda ya tsare maka hanya shi ne ka kashe shi, to a No. 1A-B a Sokoto Road an tsare maka hanya, to me ya kai ka (Darur Rahma da ke) hanyar Jos? Darur Rahma ba tana daidai kan hanyar Jos ba ne ma, sai ka saki hanyar Jos ka k**a hanyar wani kauye da ake ce masa gidan Rahma, wanda ta nan muka ba gurin suna Darur Rahma… Me ya kai su nan, wanda sai ka bar ma hanyar Jos? Me kuma ya hada su da Fudiyyah Center, wadda take hanyar Wusasa? Ita ma tana kan hanyar Buratai ne? Me ya kai su kuma cikin gari gidan mahaifiyata, inda na bizne ta. S**a je har s**a rusa gidan a lungun da dakyar muke shiga mota?... Har ma s**a ce za su kwakwale kabarin mahaifiyata, sai da mutanen unguwar s**a fito s**a ce sai dai a yi fada, ba za su yarda a yi wannan abin a gabansu ba. Akwai wani tsoho da yace sai dai ya mutu, ba zai yarda a yi wannan abin a gabansa ba, ya san wacece wannan da aka bizne a wajen.

“Kuma me ya kai su tsare duk hanyoyin da ake shiga cikin Zariya, daga hanyar Kano, s**a tsare wajen masallacin Annur, duk motar da s**a gani da alamar ‘yan uwa sai su harbe su. Sannan kuma ta hanyar Malumfashi, shi ma in s**a ga alaman wani mai k**a da dan uwa, ko yar uwa mai hijabi sai su watsa ma motar fetur su kona gabadaya, da direba da kwandasta da duk wadanda ke ciki kona su suke yi. Na hanyar Jos akwai wanda yake bani labarin su rika rabawa, sai su kwashe wadanda suke so, sai su kyale direba da kwandasta su wuce, sannan su shiga da wadannan cikin fadama su harbe su. Har wani soja yana ba da labarin cewa ‘mun ta harbe su suna cewa Allahu Akbar.’”

Shaikh Zakzaky ya bayyana takaicinsa ga yadda azzaluman mahukuntan kasar nan a yanzu ke takurawa Harka ta hanyar hana hatta a ba da hayan dakunan taro a Abuja, inda yace wai suna haka ne bisa hujjar wai an haramta IMN. Yace: “Yanzu duk sun bi inda aka yi taro sun gargadi mutanen kar su sake bamu wuri. Hujjarsu shi ne wai mu sunanmu IMN ne, kuma wai an yi ‘banning’ dinmu.”

Yace: “Su kansu ba su san doka ba. Ba yadda za a yi su kai wannan kalmar ‘banning IMN’ zuwa kotu, saboda babu wata doka a gaban wata kotu da tace an yi ‘banning’ wani abu wai shi IMN. Kun san wa ke doka a kasa a bisa ka’idojin doka? Kotu tana yin doka ne? An ce shi shugaban kasa an bashi dama yana iya haramta kungiya na kwana 14. To shi ne wannan abin, tsanani kwana 14 ne a kwansitushen, amma yanzu yau tun 2019 wai sun yi ‘banning IMN’.”

Ya kara da cewa: “To kuma mu bamu taba kiran kanmu IMN ba, su s**a saka mana wannan sunan. Mu mun ce muna Musulunci ne, mun ce muna addini ne mu, sunan addini ne IMN? In muka ce ma mutanen nan yaushe aka kafa IMN din? Kila su ce 1980 ne aka kafa. To shi addinin Musulunci a 1980 aka fara shi? Ashura a 1980 aka fara? Mauludin Annabi a 1980 aka fara? Wani abu ne haka nan, duk abin da muka yi na addini sai ku ce (IMN)?”

Yace: “A Zaria akwai wani alkalin Majestari da yake ma ‘yan uwa hukunci wai ya daure su wai sun shiga kungiyar IMN. To shi ne sai CJ na wancan lokacin yace a tuhume shi, ina ya ga dokar? Bisa ka’ida shi Majestari ba yana karanta doka a jarida ba ne, ana bashi dokan ne a rubuce a kotu (da ke samansa).”

Jagora ya kuma bayyana yadda azzaluman mahukuntan kasar nan da jami’an tsaronsu a lokuta daban-daban suke karya dokan kotunan kasar nan. Yace: “Karya doka suke yi. Wadansu dokoki ne basu karya ba? Kun ga alal misali, kotu tace a sake mu ba tare da gindaya sharadi ba, a biya mu ‘compensation’ (kudin ramuwa), a bamu gidan da za mu zauna a gurin da muka zaba a Arewacin Nijeriya, kuma a ajiye masu gadi don su kare mu daga hadarin da s**a ce suna kare mu daga gare shi. (Alkalin) yace, kuma wannan ba yana nufin za a je a tsare mu ne a gidan ba, muna da hurriyan mu je duk inda muka ga dama. To amma ba su bi umurnin kotun ba har yanzu (tun 2016).

“Kuma ‘yan uwa da aka saka karo na farko su 77, kotu ta basu takardar cewa kowannensu yana iya komawa bakin aikinsa, kuma a biya shi albashinsa na duk watannin da ya yi a tsare, saboda tsarewan da aka yi ba bisa ka’ida ba ne, don bai yi laifin komai ba. Amma sam gwamnati ba ta komar da su ayyukan nasu ba, kuma bata biya su ba. Haka ma kotu na biyu, duk haka nan ne.

“Irin wannan ya auku a wani lokacin Ashura a Sakkwato, sun kashe wasu ‘yan uwa, ‘yan uwa muka kai su kotu, kotu tace abin da (‘yan sandan) s**a yi ya saba ka’ida, dole su biya ‘compensation’. S**a daukaka kara. Kotun daukaka kara tace dole sai sun biya ‘compensation’, amma har yau ba su bi umurnin kotun ba!

“Nan a Abuja, sun hahharbi mutane na July, 2019, s**a dauki gawarwaki, s**a tafi ‘mortuary’ s**a ajiye, aka yi aka yi su bayar da su s**a ki. Aka kai su kotu, kotu tace su ba da wadannan gawarwakin (ga ‘yan uwa), kuma su biya ‘compensation’. S**a ki. Sai da aka daukaka kara, aka kai su wani kotu, wata kotu tace, to shi IG ya kawo dalilin da yasa ba za shi kurkuku ba saboda kin bin doka? Sannan ne sai yace a ba su gawan, amma ‘compensation’ bai bayar ba.

“A Kaduna ma kazalik, sun harbi ‘yan uwa, an kai su kotu, kotu tace lallai su biya ‘compensation’, har yau basu ba da ko kwabo ba! Duk doka su basu bi, suna karairaya doka yadda ransu ya ga dama, abin da s**a ga dama shi suke yi.” Inji Shaikh Zakzaky.

Jagoran ya kuma jaddada yabawansa ga ‘yan uwan da s**a tsaya kyam s**a dake a tsawon wadannan shekarun waki’ar ba tare da sun ja da baya ba wajen nuna yatsa ga azzalumai. “Mun ga wadanda s**a dake daram ba su ja baya ba. Har ma nake cewa, inda a ce su mutanen kasar nan duk abin da ka yi musu suna yin shiru ne. Za a ce banda su wane. Akwai wadanda za a ce su ba su yin shiru, ba sa yarda da zalunci. Har ma su mutane suna shaida, don haka ne ma, lokacin da suke fama da matsaloli (na tsadar rayuwa) suke cewa, da ‘yan Shi’a za su taimaka, da abin ya yi daidai. Ka san Dan Shi’a ba ya ja da baya, ko za a harbe shi ne. To amma shi ya san dalilin da yasa ba ya ja da bayan, yana yin haka ne da yakinin cewa yana yin addini ne, ba zai yi maka akan harigidon duniya ba.” Inji Jagora.







13/Jimada ath-Thaniyah/1446
14/12/2024

Le Hijab, la Liberté Religieuse, les Lois Nigérianes, et les Conséquences de la Violation des Droits des Porteuses de Hi...
30/08/2024

Le Hijab, la Liberté Religieuse, les Lois Nigérianes, et les Conséquences de la Violation des Droits des Porteuses de Hijab

Par Zaharaddeen Ishaq Abubakar

Le hijab occupe une place importante dans l'Islam, en particulier pour préserver la dignité et maintenir l'honneur des femmes musulmanes. Dans de nombreux pays à majorité musulmane, le port du hijab est une pratique à la fois religieuse et culturelle. Au Nigéria, un pays avec une population musulmane importante, la question du port du hijab est étroitement liée à la liberté religieuse et aux droits individuels.

Selon les enseignements islamiques, le port du hijab est un commandement divin pour les femmes et est considéré comme une forme d'obéissance aux principes religieux. Dans un pays comme le Nigéria, caractérisé par une diversité religieuse, le droit à la liberté religieuse est d'une importance capitale. La Constitution nigériane de 1999, dans son article 38, garantit à chaque citoyen le droit de pratiquer sa religion sans interférence. Cela inclut le droit des femmes musulmanes de porter le hijab.

Les lois nigérianes prévoient la protection des droits des femmes musulmanes à porter le hijab. La constitution comporte des dispositions qui protègent chaque citoyen contre toute discrimination fondée sur la religion, et permet à chaque individu d'exercer ses droits religieux sans interférence. Cela signifie qu'aucune femme musulmane ne doit être empêchée de porter le hijab en aucune circonstance.

La loi au Nigéria stipule clairement que harceler ou discriminer des femmes qui portent le hijab est une infraction punissable. Selon la Constitution nigériane, chaque citoyen a le droit de demander une protection contre le harcèlement et les abus. Par conséquent, toute personne qui harcèle ou discrimine une femme, quel que soit son statut ou son autorité, et indépendamment de l'infraction qu'elle aurait pu commettre, peut être tenue responsable d'une infraction liée au harcèlement ou à l'abus. Ces personnes feront face à des conséquences juridiques sévères, comme prévu par la loi.

Le hijab est un aspect essentiel de la vie et des pratiques religieuses des femmes musulmanes. Le droit de porter le hijab au Nigéria est ancré dans la constitution, et la loi prévoit une protection pour toute personne dont les droits sont violés en raison de cette pratique religieuse.

الحجاب وحرية الدين والقوانين النيجيرية وعواقب انتهاك حقوق مرتديات الحجاببقلم زهر الدين إسحاق أبو بكريمثل الحجاب جزءًا مه...
30/08/2024

الحجاب وحرية الدين والقوانين النيجيرية وعواقب انتهاك حقوق مرتديات الحجاب

بقلم زهر الدين إسحاق أبو بكر

يمثل الحجاب جزءًا مهمًا في الإسلام، خاصةً في الحفاظ على كرامة وشرف النساء المسلمات. في العديد من البلدان ذات الأغلبية المسلمة، يُعتبر ارتداء الحجاب عادةً دينية وثقافية. في نيجيريا، وهي دولة تضم عددًا كبيرًا من المسلمين، يرتبط موضوع ارتداء الحجاب ارتباطًا وثيقًا بحرية الدين وحقوق الأفراد.

في التعاليم الإسلامية، يُعد ارتداء الحجاب للنساء أمرًا إلهيًا، ويُعتبر جزءًا من الطاعة الدينية. في بلد مثل نيجيريا، الذي يتميز بتعدد الأديان، تُعتبر حرية الدين أمرًا في غاية الأهمية. يكفل الدستور النيجيري لعام 1999، في المادة 38، لكل مواطن الحق في ممارسة دينه دون تدخل. وهذا يشمل حق النساء المسلمات في ارتداء الحجاب.

تقدم القوانين النيجيرية حماية لحقوق النساء المسلمات في ارتداء الحجاب. يحتوي الدستور على أحكام تحمي كل مواطن من التمييز على أساس الدين، وتتيح لكل فرد ممارسة حقوقه الدينية دون تدخل. وهذا يعني أنه لا ينبغي منع أي امرأة مسلمة من ارتداء الحجاب تحت أي ظرف من الظروف.

تنص القوانين في نيجيريا بشكل واضح على أن مضايقة النساء اللاتي يرتدين الحجاب أو التمييز ضدهن بسبب ارتداء الحجاب هي جريمة يعاقب عليها القانون. وفقًا للدستور النيجيري، يحق لكل مواطن طلب الحماية من المضايقة والاعتداء. لذلك، يمكن اعتبار أي شخص يضايق أو يميز ضد امرأة، بغض النظر عن وضعه أو سلطته، وبغض النظر عن الجريمة التي قد تكون ارتكبتها، قد ارتكب جريمة تتعلق بالمضايقة أو الاعتداء. سيواجه هؤلاء الأفراد عواقب قانونية صارمة كما هو منصوص عليه في القانون.

الحجاب هو جزء أساسي من حياة النساء المسلمات وممارساتهن الدينية. ويستند حق ارتداء الحجاب في نيجيريا إلى الدستور، وينص القانون على توفير الحماية لأي شخص يتم انتهاك حقوقه بسبب هذه الممارسة الدينية.

Shaikh Yakub Yahya Katsina, accompagné de certains érudits musulmans de diverses régions de la communauté, ont assisté à...
24/08/2024

Shaikh Yakub Yahya Katsina, accompagné de certains érudits musulmans de diverses régions de la communauté, ont assisté à la visite de l'Arba'een de cette année, qui se déroule actuellement à Karbala, la ville sainte en Irak.

Le vendredi soir (24/08/2024), la délégation a rejoint la marche de l'Arba'een menée par les disciples de Sayyid Zakzaky (H) de Najaf à Karbala.

Cette marche est organisée pour exprimer le deuil et la sympathie envers la famille du Prophète de Miséricorde (S) pour le massacre commis contre eux à Karbala en l'an 61-62 après l'hégire du Prophète (S), et pour rappeler les souffrances qu'ils ont endurées, en étant enchaînés et traînés sur le sol brûlant du désert jusqu'au palais de Yazid (L.a).

Voici quelques photos de la marche.

الشيخ يعقوب يحيى كاتسينا مع بعض العلماء المسلمين من مختلف أنحاء الأمة حضروا زيارة الأربعين لهذا العام، والتي تجري حاليًا...
24/08/2024

الشيخ يعقوب يحيى كاتسينا مع بعض العلماء المسلمين من مختلف أنحاء الأمة حضروا زيارة الأربعين لهذا العام، والتي تجري حاليًا في مدينة كربلاء المقدسة في العراق.

مساء الجمعة (24/08/2024)، دخلت القافلة في صفوف مسيرة الأربعين التي ينظمها أتباع السيد زكزكي (ح) من النجف إلى كربلاء.

أُقيمت هذه المسيرة للتعبير عن الحزن والتعاطف مع عائلة رسول الرحمة (ص) بسبب المذبحة التي ارتكبت ضدهم في كربلاء في السنة 61-62 بعد هجرة الرسول (ص)، ولتذكر المعاناة التي تعرضوا لها، حيث تم تقييدهم بالسلاسل وسحبهم على الأرض في حر الصحراء حتى وصلوا إلى قصر يزيد (لع).

إليكم بعض الصور من موقع المسيرة.

Shaikh Yakub Yahya Katsina tare da wasu malaman musulunci daga sassa daban-daban na al’umma sun halarci ziyara ta Arba’e...
24/08/2024

Shaikh Yakub Yahya Katsina tare da wasu malaman musulunci daga sassa daban-daban na al’umma sun halarci ziyara ta Arba’een na bana, wadda ke gudana a yanzu haka a birnin Karbala mai tsarki a kasar Iraq.

A yammacin Juma’a (24/08/2024), tawagar ta shiga sahun Tattakin Arba’een da 'yan’uwa almajiran Sayyid Zakzaky (H) ke gudanarwa daga Najaf zuwa Karbala.

An gudanar da wannan tattaki ne domin nuna juyayi da alhini ga iyalan Manzon Rahama (S) saboda kisan gillar da aka yi musu a Karbala a shekara ta 61-62 bayan hijirar Manzon Allah (S), da kuma tunawa da irin azabar da aka sha azabtar da su, inda aka ɗaure su da sarƙoƙi kuma aka ja su ƙasa cikin zafin sahara har zuwa fadar Yazidu (L.a).

Assalamu AlaikumƊan’uwa Bin Yaqoub Katsina, ke gabatar maku da Bidiyon waƙen juyayin Ashura 1446A yi kallo cikin juyayi....
14/07/2024

Assalamu Alaikum

Ɗan’uwa Bin Yaqoub Katsina, ke gabatar maku da Bidiyon waƙen juyayin Ashura 1446

A yi kallo cikin juyayi.

#وفاءللحسين
#لبيك ياحسين


Waken juyayin kisan Imam Hussain (A.S) daga bakin ɗan’uwa Bin Yaqoub Katsina

CONTINUATION DES OBSÈQUES D’ASHURA À KATSINAComme chaque année, cette année aussi, les frères musulmans disciples de Say...
12/07/2024

CONTINUATION DES OBSÈQUES D’ASHURA À KATSINA

Comme chaque année, cette année aussi, les frères musulmans disciples de Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) de la région de Katsina continuent les obsèques d'Achoura pour exprimer leur chagrin et leur tristesse face au massacre brutal perpétré par les Omeyyades contre les descendants du Prophète Mohammed (S) en l'an 61 après l'Hégire sur le champ de Karbala.

Ces obsèques sont une partie de l’expression de l’amour envers le Prophète et sa sainte famille, de même que partager leur tristesse montre l'affection, tout comme se réjouir de leur joie.

Le Sheikh Yakub Yahya Katsina dirige les séances où il récite l’histoire de cet événement tragique à partir de diverses narrations, notamment celles tirées des livres de la Sunnah. De plus, des centaines de musulmans compatissants envers les Ahlulbayt (A.S) de différentes parties de la ville de Katsina se rassemblent chaque jour pour écouter cette lecture au Markaz situé à Unguwar Ƙofar Marusa.

Aujourd'hui, vendredi 06/01/1446 (12/07/2024) marque la cinquième séance, comme le montrent les photos ci-dessous.

HADISAN GHADIR KHUMM. KASHI NA DAYA (1)Ghadir Khumm (Da Larabci : حَدِيْث ٱلْغَدِير ,Hadīth al-Ghadīr ) yana nufin taron...
24/06/2024

HADISAN GHADIR KHUMM. KASHI NA DAYA (1)

Ghadir Khumm (Da Larabci : حَدِيْث ٱلْغَدِير ,Hadīth al-Ghadīr ) yana nufin taron musulmi don halartar wa'azin da annabi Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallama ya gabatar a ranar 16 ga Maris 632 Miladiyya 18 Dhu al-Hijjah 10 AH). An ce taron ya gudana ne a Ghadir Khumm, wanda ke kusa da unguwar al-Juhfa a lokacin a kan hanyar da ta hada Makka da Madina, in da Annabi Muhammad (SAW) ya dakatar da ayarin musulmi da ke dawowa daga aikin Hajjin bankwana.

A cikin hudubar da aka yi jim kadan kafin wafatin Annabi a watan Yuni na shekara ta 632 Miladiyya (11H), Annabi Muhammad (SAWW) ya yi shela ga Ali bin Abi Talib, kaninsa kuma surukinsa, yana fadin cewa: “Wanda nake Shugaban sa. , Ali Shugabansa Ne. Musulmi ‘yan Shi’a sun yi imani da hakan a matsayin wata babbar alama da ke nuna cewa an nada Ali ne ya jagoranci al’ummar Musulmi bayan Wafatin Annabi Muhammadu (SAWW) suna kuma Murnar da kuma murnar zagayowar ranar bikin a matsayin Eid al-Ghadir. A halin da ake ciki Musulmin Sunna suna kallon sanarwar a matsayin wani abu mai sauki na tabbatar da darajar Annabi Muhammad (SAWW) ga Ali.

HADISIN GADAR KHUMM.

Hadisin Ghadir wani hadisi ne da wani abu ya gabace shi, wani dabam kuma ya biyo bayansa. Bayani game da abin da ya gabace shi har zuwa shi kansa, wani abu ne da zai amsa shubuhar mai shubuhohi ta biyu; abin da kuwa ya biyo bayansa, duk da mahallin nan ba zai iya daukar cikakken bayani a kansa ba, sai dai dan abin da zai zo zai ba shi amsar shubuharsa ta uku. Don haka bari mu fara bisa yardar Allah mu gani.

Abin da Ya Gabaci Hadisin Ghadir

Bayan Manzon Allah (SAWW) ya kammala Aikin hajinsa da ake kira da Hajin Ban-Kwana, kuma ya k**a hanyarsa ta komawa Madina tare da ayarin Musulmi mahajjata da adadinsu ke da yawan gaske, a lokacin da ya iso wajen wata rijiya da ake kira Ghadir, wanda ke wani wuri da ake kira Khum, wanda yake yankin Juhfa (na kasar Hijaz ta da can ba Saudiyar yau da aka sauya tsarinta ba). Wajen na matsayin wata mararraba ce da hanyoyi s**a rarrabu zuwa Masar, Madina, Sham da Iraki; a nan ne Mala'ika Jibrilu (AS) ya sauko, a ranar alhamis 18 ga watan Zul-Hajji, da fadar Allah Madaukaki:

﴿يأيّها الرّسولُ بلّغ ما أُنزل أليك من ربّك وأن لم تفعل فما بلّغت رسالته والله يعصِمُك من النّاس أن الله لا يهدى القوم الكافرين﴾ سورة المائدة/67

Ma'ana:

Ya kai wannan Manzo, ka isar da abin da aka saukar zuwa gare ka daga Ubangijinka, idan ba ka aikata (haka) ba, to ba ka isar da (sauran) sakon Sa ba, kuma Allah Zai kare ka daga mutane, lalle Allah ba Ya shiryar da jama'a kafirai." Surar Ma'ida: 5:57.

Nan take ba tare da wani bata lokaci ba sai Manzon Allah (SAWW) ya aika da a tsayar da wadanda ke gabansu, sannan bayan ya cim musu, ya sa a jira wadanda ke baya har sai da s**a zo. Adadin su bai daya ya kai dubu saba'in ko fiye. Sai ya yi horo da kiran salla, ya jagoranci mutane sallar azahar, bayan ya kammala sai ya yi wa mutane huduba. Bayan ya gode wa Allah ya yabe Shi, sai ya yi wasici ya tunatar, ya fadi abin da Allah Ya so ya fada, sannan ya ce: "An kusa a kira ni in amsa, lalle ni abin tambaya ne ku ma wadanda za a tambaya ne, shin me za ku ce?"

Sai s**a ce: "Mun shaida cewa lalle ka isar, kuma ka yi nasiha, Allah Ya saka maka da alheri."

Sai ya ce: "Ashe ba ku shaida cewa babu abin bauta Sa Gaskiya sai Allah ba, kuma ni Muhammadu bawan Sa ne kuma Manzon Sa, kuma Aljanna gaskiya ce haka wuta gasikya ce ba?"

Sai s**a ce: "Kwarai kuwa mun shaida haka."

Sai ya ce:"Ashe ba ku san cewa ni ne mafi cancantar mai jibintar al'amurran Muminai fiye da su kansu ba?" Sai s**a ce: "Kwarai kuwa mun shaida haka ya Manzon Allah."

Sannan sai ya k**a hannun Ali bin Abi Dalib (AS) ya daga sama har sai da mutane s**a ga hammatarsu, sannan ya ce:

Duk wanda na zama majibincin al'amarinsa, to Ali ya zama majibincin al'amarinsa. Ya Allah Ka jibinci wanda ya mika wilaya gare shi, Ka kuma ki wanda ya ki shi; Ka kuma taimaki wanda ya taimake shi, Ka kuma tabar da wanda ya bar shi.

Sannan sai ya ce: "Ya Allah ka yi shaida."

Daga nan Muhammad (SAWW) ya gabatar da huduba ga dimbin al’ummar musulmi in da a cikinta k**ar yadda Hadisin Thaqalayn ya bayyana, ya jaddada muhimmancin abubuwa biyu: Alkur’ani da Ahlulbaiti iyalansa). Wannan hadisin duk sunna da shi'a ne sun ruwaito shi. Musamman ma sigar da ta zo a cikin Musnad Ibn Hanbal madogaran Ahlus-Sunnah, ita ce k**ar haka:

Na bar muku taska guda biyu, idan kuka yi riko da su, ba za a batar da ku a bayana ba. Daya daga cikinsu ya fi daya girma: Littafin Allah, wanda igiya ce daga sama zuwa kasa, da zuriyata, Ahlul-baiti.

Daga nan sai Abubakar (RA) da Umar (RA) s**a je wajen Ali (AS) su na taya shi murna suna cewa: "Barkanka! Barkanka dan Abu Dalib!! Daga yau ka zama majibincin al'amarin kowane mumini da mumina."

Bayan Manzon Allah (SAWW) ya aiwatar da abin da Allah Ya h**e shi a gaban shedun da adadinsu ya wuce dubu saba'in, sai Mala'ika Jibrilu (AS) ya sauko da fadar Allah Madaukaki:

﴿اليومُ أكملتُ لكُم دينَكم وأتممتُ عليكم نعمتى ورضيتُ لكم الاسلام دينًا﴾ سورة المائدة/3

Ma'ana:

A yau na cika muku addinin ku, kuma na cika ni'ima Ta a kanku, na kuma yardar muku Musulunci a matsayin addini. Surar Ma'ida, 5:3.

Wannan shi ne abin da ’Yan Shi'a ke fada a takaice. Kuma sun yi imani da cewa wannan na daya daga cikin nassosin da s**a tabbatar wa Imam Ali (AS) shugabancin Muminai da Khalifancin Manzon Allah (SAWW); daya daga cikinsu ba ya taraddudi a kan haka.

Saliadeen Sicey ✍️

Ina masu cewa "da ma 'yan Shi'a na zuwa hajji?" TO GA NAKU!Wannan labarin ze ɓata ran wasu amma dole mu faɗa sai dai Haƙ...
19/06/2024

Ina masu cewa "da ma 'yan Shi'a na zuwa hajji?" TO GA NAKU!

Wannan labarin ze ɓata ran wasu amma dole mu faɗa sai dai Haƙuri...

Hukumar dake kula da aikin Hajji a ƙasar Saudiya sun ambaci Alhazan ƙasar Iraqi a matsayin Alhazan da s**a fi kowassu Alhazzai kula da bin doka tare da tsari. An basu kyautar karramawa bisa hakan. Shekarar da ta gabata Alhazan ƙasar Iran ne aka zaɓa da s**afi ɗa'a da tsafta, domin ance suna tafiya tare da wakilan su da suke tsaftace duk inda s**a zauna ko robar ruwa basa yarwa.

A wani labarin kuma, ga hoton Sheik Sami Al-Mas'udiy (Shugaban Hukumar Alhazai ta Iraqi ) ke fitowa daga dakin Ka'aba bayan an buɗe musu sun shiga a wata ziyara tasu kasar Saudiyya. Sama da ƴan Shi'a dubu ɗari 3 ne s**ayi aikin hajjin bana daga ƙasashen Iran, Iraqi, Lebanon, Najeriya da sauran sassan duniya. Musulmi ɗan uwan Musulmi ne!

Hoto: Al-Abdul Faneey Al-kanaweey

Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) ya dawo gida bayan halartar taron ƙasa da ƙasa na nuna goyon baya ga  al'ummar Palast...
12/05/2024

Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) ya dawo gida bayan halartar taron ƙasa da ƙasa na nuna goyon baya ga al'ummar Palastinu, wanda ya gudana a birnin Bagadaza, kasar Iraki, a ranar Laraba 08 ga watan Mayu 2024.

Leader Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) on Tuesday paid visit to Al-Khazimayn Holy Shrine, which includes the graves of Imam ...
07/05/2024

Leader Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) on Tuesday paid visit to Al-Khazimayn Holy Shrine, which includes the graves of Imam Musa Khazim and Imam Muhammad Jawad (S) in Baghdad.

Sayyid Ibraheem Zakzaky Office


07/05/2024
27/Shawwal/1445

Address


Telephone

+2348036342932

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when VOICE of Sheikhs posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share