21/07/2025
IMAMU SAJJAD (A.S): Wanzuwar da ta Wanzar da Addini...
A cikin irin mawuyacin hali da aka fuskanta bayan kisan Imam Hussain (A.S), Imam Ali bn Hussain (Zainul Abidin A.S) ya ɗauki nauyin ceton addini daga shafewa gaba ɗaya. Duk alhini da ƙunci, ya tsaya da hikima da ƙarfin zuciya, ya fuskanci Yazidu (L.A) a cikin fadar sa a Damascus lokacin da aka zo da su a matsayin ribar yaƙi!
A wannan lokacin Yazidu (L.A) ya nuna jin daɗinsa bisa kisan Imam Hussain (A.S) har yana isgili da cewa: “Allah ne ya kashe su” (Ahlulbaiti), sai Imam Zainul Abidin (A.S) ya buɗe baki da furuci mai girgiza zuciya ya ce:
“أبِالقتل تفتخر يا يزيد؟”
“Shin da kisan (Babana) kake alfahari, ya kai Yazidu?)
A nan Yazidu (L.A) ya nemi ya fauce a kan maganar, amma Imam ya nace da zazzafar hujja ya cigaba da cewa:
“أما قرأت قول الله: (ولا تحسبن الذين قتلوا في سبيل (الله أمواتاً بل أحياءٌ عند ربهم يرزقون؟”
“Shin ba ka taɓa karanta zancen Allah ba cewa: (Kada ka ɗauka waɗanda aka kashe a tafarkin Allah sun mutu, a'a, su rayayyu ne a wurin Ubangijinsu suna azurtattu?)
Sai Imam ya cigaba da bayyana wa jama'ar da ke a gun shi waye da irin matsayin da Allah ya ba su, (domin Yazidu ya baza ƙarairayi da sharri kala-kala da ke nuna cewa waɗanda ya kashe a Karbala (Ahlulbaiti) ba musulmi ma ba ne kuma sun yi ƙoƙarin jayayya da mulki ne)...
Imam Zainul Abidin (A.S) ya yi ta khuɗba har sai da jikin mutane ya yi sanyi suna kuka, s**a fara la'antar Yazidu... Ganin haka Yazidu (L.A) ya sa aka kira Sallah.
Mai kiran Sallah a lokacin da ya zo dai-dai faɗar Ash’hadu Anna Muhammadan Rasulullah... Sai Imamu ya tambayi Yazidu (L.A) cewa: “Shin wannan da ake faɗa a kiran Sallah, kakanmu ne ko Kakanka? Idan ka ce Kakanka ne to haƙiƙa kowa ya san ka yi ƙarya, idan kuwa Kakanmu ne to dan me ya sa ka kashe mu tare da saka mu a halin da muke ciki?”...
Haka dai da irin waɗannan hujjoji ne Imamu Zainul Abidin ya kunyata Yazidu (L.A) sannan al'umma s**a fahimci makircin da Yazidu ya shirya... Dan haka wanzuwar Imamu Zainul Abidin ita ta wanzar da sahihin addinin Musulunci har zuwa yau ɗinnan...
A yau, muna tuna wannan babban Imami wanda shahadarsa ta faru a rana irin ta yau, 25 ga watan Muharram, kuma muna taya ’yan’uwa muminai ta’aziyyar wannan babban rashi.
أعظم الله أجورنا وأجوركم بشهادة الإمام السجاد (ع)