KAITA MEDIA

KAITA MEDIA Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from KAITA MEDIA, River nice, Katsina.

Tinubu ya ce babu wani matsin lamba da zai hana shi cimma ƙudirin da yake da shi ga NigeriaDuba wannan shafin domin samu...
16/04/2026

Tinubu ya ce babu wani matsin lamba da zai hana shi cimma ƙudirin da yake da shi ga Nigeria

Duba wannan shafin domin samun cikakken labarin:

President Bola Tinubu has declared that no amount of pressure or intimidation will distract him from pursuing his vision for Nigeria. Tinubu made the

23/01/2026

Shout out to our newest followers! We are excited to have you onboard! Naseer Umar, Usman Aliyu Kaita, Bash M Bash.

A yammacin jiya Litinin ne gwamnan jihar Kano Abbah Kabir Yusuf ya yi tattaunawar sirri da shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinu...
20/01/2026

A yammacin jiya Litinin ne gwamnan jihar Kano Abbah Kabir Yusuf ya yi tattaunawar sirri da shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu a fadar shugaban ƙasar dake birnin Abuja. Tattaunawar sirrin ta gudana a tsaka da lokacin da ake jita-jitar sauya sheƙar gwamnan daga jam'iyyar NNPP zuwa jam'iyya mai mulki ta APC.

Sai dai kamar yadda mai magana da yawun gwamnan ya bayyana, tattaunawar ta shafi batutuwan tsaro a jihar ta Kano, ayyukan cigaba, da kuma haɗa ƙarfi-da-ƙarfe tsakani gwamnatin tarayya da ta jihar Kanon domin shawo kan matsalar tsaron da ta addabi jihar a ƴan kwanakin nan.

KARƁAR HORO, YAWON BUƊE IDO, KO WAWUSHE DUKIYAR AL'UMMA?Ra'ayin Wani Matashi Kenan Mai Suna Umar Maida.Wai yanzu a haka ...
09/11/2025

KARƁAR HORO, YAWON BUƊE IDO, KO WAWUSHE DUKIYAR AL'UMMA?

Ra'ayin Wani Matashi Kenan Mai Suna Umar Maida.

Wai yanzu a haka yadda ake gudanar da mulkin ƙananan hukumomi a jihar Katsina har ilimin shuwagabannin ya wuce su karɓi horo da dabarun gudanar da mulki daga hannun ɗinbin masanan da muke dasu a cikin faɗin jihar da ma tarayyar Nijeriya gabaki ɗaya. Wannan abun sai ya tunamin wani karatu wai shi zuuƙu!

Gaskiyar zance wannan batun ya saɓawa tsarin Aulawiyya (fi-fita abu mai muhimmanci). Yayinda malaman jami'ar mu s**a niƙi yaji — amma na aiki, ɗalibai suke zaune a gidajen iyayen su, mutanen karkara suke fama da matsanancin rashin wadatacen ruwan-sha, ajujuwan zama domin ɗaukar darasu, magani a asibitoci, da sauran matsal-tsalu da s**a addabi kananan hukumomi da karkara; a irin wa'annan yanayin ne aka cire maƙudan kuɗaɗen talakawa daga lalitar gwamnati domin kai shuwagabannin ƙananan hukumomi a ƙasar Birtaniya domin karɓar horo da dabarun gudanar da mulki — wanda ba lallai ne ya amfani talaka ba.

Idan ban mantaba, watanni biyu zuwa uku da s**a shuɗe, Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafen Al'umma da Yaƙi da Cin-hanci da Rashawa (Public Complain and Anti-corruption Commission) ta jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Dr. Jamilu Abdussalam Charanci, ta gudanar da wani taron wayar da kan kansilolin jihar Katsina baki ɗaya. Muna da fa masana kuma gogaggi akan mulki da gudanarwa a faɗin jihar nan. Superstructure ta Najeriya daban da ta ƙasar Ingila, mu muka san a ina ɗakinmu yake zubar da ruwa.

Wannan dai kawai an ɗauke su ne zuwa yawon buɗe ido da sunan karɓar horo — kuma mu talakawan jihar Katsina, muna tur da Allah wadai da wannan lamarin.

Assalamu alaikum.A yau saƙon al'umma ne muke ɗauke da shi zuwa ga masu ruwa da tsaki a ƙaramar hukumar Kaita, musamman s...
21/09/2025

Assalamu alaikum.

A yau saƙon al'umma ne muke ɗauke da shi zuwa ga masu ruwa da tsaki a ƙaramar hukumar Kaita, musamman shugaban ƙaramar hukumar da kuma sauran wakilan majalisar tarayya da wakilin majalisar dokoki ta jiha.

Al’ummar garin Gabasawa da ke cikin gundumar Ba'awa suna kira da roƙo zuwa ga hukumomin ƙaramar hukumar Kaita da su dubi matsalolin su na yau da kullum da idon basira.

Al'ummar wannan gari na Gabasawa ƙarƙashin wakilcin wani matashi mai suna Mu'azzam Gabasawa sun bayyana abubuwa guda biyu da s**a zama manyan damuwar su kuma suke ci masu tuwo a ƙwarya:

Na farko, suna roƙon gwamnati da ta gina masu magudanan ruwa (water channels) domin kare al’ummar su daga bala’in ambaliyar ruwa da ya zama ruwan dare a ƴan kwanakin nan. Ambaliya tana lalata gidaje, tana hallaka amfanin gona, tana kuma jefa jama’a cikin mummunan halin rayuwa.

Na biyu, suna bukatar gwamnatin Kaita ta gina musu sabon masallaci ko kuma ta gyara tsohon masallacin su wanda ya lalace har ruwa na shiga a ciki a lokutan Damina. A halin yanzu ba sa iya gudanar da sallar Jumu’a, wadda ita ce sallah mai muhimmanci ga kowanne musulmi a duk mako. Wannan matsala ta hana al’ummar garin Gabasabawa gudanar da ibada yadda ya kamata, abin da ya zama babban abin damuwa ga mutanen garin.

Sun kuma yi jan hankali zuwa ga gwamnatin ƙaramar hukuma cewa: Gyara wannan masallaci ko gina sabo ba wai kawai zai ba su masaukin ibada ba ne, sai dai zai ƙarfafa haɗin kai da zaman lafiya a cikin al’umma. Masallaci shi ne cibiyar taro, koyarwa da tarbiyya ga yara, matasa da ma dattawa, don haka gyaransa ko gina sabo zai kasance tamkar gina al’ummar garin ne gaba ɗaya.

Saboda haka, al’ummar garin Gabasawa suna kira cikin girmamawa ga hukumomin Kaita da su ɗauki wannan kira da muhimmanci, su aiwatar da wadannan bukatu cikin gaggawa, domin kare rayukan jama’a, lafiyar su, da kuma martabar addini a cikin al’ummar su.

Umar Maida 🖋️
Sep 21st , 2025

MURYAR MARASA MURYA: SAƘON AL'UMMAR KARAMAR HUKUMAR KAITA Anyi kiran gaggawa zuwa ga shuwagabannin ƙaramar hukumar Kaita...
07/09/2025

MURYAR MARASA MURYA: SAƘON AL'UMMAR KARAMAR HUKUMAR KAITA

Anyi kiran gaggawa zuwa ga shuwagabannin ƙaramar hukumar Kaita da su dubi Allah su ji kiran talakawansu, su dubi mutanen garin Kagadama da al'ummar ƙaramar hukumar Kaita baki ɗaya, da su kawo ɗauki wajen gyara hanyar da ta tashi daga Babbar-Ruga ta bi ta Matsai ta kuma tuƙai a cikin garin Kagadama.

A wata hira da nayi dashi a ta wayar tarho; Alh. Babangida Umar Dankama (Babangida Ƙaura) babban ɗan kasuwa kuma ɗan gwagwarmayar siyasa, ya shaida man cewa “yakamata shuwagabannin ƙaramar hukumar Kaita su dinga duba matsaloli wanda s**a danganci gina ƙasa musamman hanyoyi da muke amfani dasu a matsayin mu na ƴan kasuwa na ƙaramar hukumar Kaita. Ƴan siyasa suna watsi da hanyoyi na neman abinci na ƴan asalin ƙasar hukumar Kaita. Musamman akwai wata hanya na nan da ta ɓullo daga Babbar-Ruga zuwa Tashar-Nakande. Hanya ce mai tarihin gaske kuma kuma mai kawo ma karamar hukumar Kaita kuɗaɗen shiga. Akwai wata kasu da ake ce ma Kagadama, wannan kasuwa tana bakin boda, kuma tsakanin ta da bodar bar wuce kilomita ɗaya ba.”

“Ƙaramar hukumar Kaita ta ta'allaka akan kasuwanni guda uku, wannan kasuwanni sune: Dankama, Kaita da Kagadama.” A cewar Alh. Ƙaura.

Ya ƙara da cewa: Sakamakon rashin kyakkyawan yanayin sufuri da lalacewar wannan hanyar yasa mutane da dama suke shakkar zuwa kasuwar Kagadama, idan kau har ka tafi musamman ta hanyar garin Dankama wacce ta ɓullo zuwa garin Kabobi kuma akayi ruwan sama to kai a ranar nan ta kulle da kai sakamakon wata ƙorama data gitta akan hanyar.

Daga ƙarshe dai Alh. Babangida yayi kira a madadin shi kanshi da ɗaukacin ƴan kasuwa da al'ummar ƙaramar hukumar Kaita zuwa ga shuwagabannin ƙaramar hukuma Engr. Bello Lawal Yanɗaki, da ƴan majalisun jaha da na tarayya Hon. Surajo Abdullahi Kwaskwaro da Hon. Sada Soli Jibia da su duba wannan lamarin domin samama al'ummar ƙaramar hukumar Kaita sauƙi.

MURYAR MARASSA MURYA: SAƘON AL'UMMAR ƘARAMAR HUKUMAR KAITAWannan shiri ne wanda zai riƙa isar da saƙunna,  buƙatu da kok...
05/09/2025

MURYAR MARASSA MURYA: SAƘON AL'UMMAR ƘARAMAR HUKUMAR KAITA

Wannan shiri ne wanda zai riƙa isar da saƙunna, buƙatu da koken al'ummar ƙaramar hukumar Kaita zuwa ga shuwagabanni da masu ruwa-da-tsaki a cikin gwamnati (akai-akai) domin magance matsalolin da s**a yi ma talakan ƙaramar hukumar Kaita katuku. Wannan shirye-shiryen an tsara su ne akan political neutralism (babu nuna ɓangaranci ko adawar siyasa). Manufar mu itace a isar da saƙon al'ummar ƙaramar hukumar Kaita zuwa ga shuwagabanni da mahukunta.

Zaku iya samun wa'yannan shirye-shiryen shafukan Facebook kamar haka:

🌍 •Kaita Media 🌐•Umar Maida

02/07/2025

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Rabson Guy Ontop, Maazu Salisu Kshagari, Saminu Abdul

Address

River Nice
Katsina

Telephone

+2348164333929

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when KAITA MEDIA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share