21/09/2025
Assalamu alaikum.
A yau saƙon al'umma ne muke ɗauke da shi zuwa ga masu ruwa da tsaki a ƙaramar hukumar Kaita, musamman shugaban ƙaramar hukumar da kuma sauran wakilan majalisar tarayya da wakilin majalisar dokoki ta jiha.
Al’ummar garin Gabasawa da ke cikin gundumar Ba'awa suna kira da roƙo zuwa ga hukumomin ƙaramar hukumar Kaita da su dubi matsalolin su na yau da kullum da idon basira.
Al'ummar wannan gari na Gabasawa ƙarƙashin wakilcin wani matashi mai suna Mu'azzam Gabasawa sun bayyana abubuwa guda biyu da s**a zama manyan damuwar su kuma suke ci masu tuwo a ƙwarya:
Na farko, suna roƙon gwamnati da ta gina masu magudanan ruwa (water channels) domin kare al’ummar su daga bala’in ambaliyar ruwa da ya zama ruwan dare a ƴan kwanakin nan. Ambaliya tana lalata gidaje, tana hallaka amfanin gona, tana kuma jefa jama’a cikin mummunan halin rayuwa.
Na biyu, suna bukatar gwamnatin Kaita ta gina musu sabon masallaci ko kuma ta gyara tsohon masallacin su wanda ya lalace har ruwa na shiga a ciki a lokutan Damina. A halin yanzu ba sa iya gudanar da sallar Jumu’a, wadda ita ce sallah mai muhimmanci ga kowanne musulmi a duk mako. Wannan matsala ta hana al’ummar garin Gabasabawa gudanar da ibada yadda ya kamata, abin da ya zama babban abin damuwa ga mutanen garin.
Sun kuma yi jan hankali zuwa ga gwamnatin ƙaramar hukuma cewa: Gyara wannan masallaci ko gina sabo ba wai kawai zai ba su masaukin ibada ba ne, sai dai zai ƙarfafa haɗin kai da zaman lafiya a cikin al’umma. Masallaci shi ne cibiyar taro, koyarwa da tarbiyya ga yara, matasa da ma dattawa, don haka gyaransa ko gina sabo zai kasance tamkar gina al’ummar garin ne gaba ɗaya.
Saboda haka, al’ummar garin Gabasawa suna kira cikin girmamawa ga hukumomin Kaita da su ɗauki wannan kira da muhimmanci, su aiwatar da wadannan bukatu cikin gaggawa, domin kare rayukan jama’a, lafiyar su, da kuma martabar addini a cikin al’ummar su.
Umar Maida 🖋️
Sep 21st , 2025