Horizon News Hausa

Horizon News Hausa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Horizon News Hausa, Media/News Company, Batsari Road, Katsina.

Kungiyar Hada Kan Matasan Arewa Zata Karrama Hazikin Matashi Ambasada Kaikai Da Lambar YaboMatashin Dan Siyasa Kuma mai ...
22/10/2022

Kungiyar Hada Kan Matasan Arewa Zata Karrama Hazikin Matashi Ambasada Kaikai Da Lambar Yabo

Matashin Dan Siyasa Kuma mai bada tallafin Jin kai dan Asalin Jihar Katsina Ambasada Injiniya Abubakar Shehu Kaikai, na daya daga cikin muhimman mutane da Kungiyar Hada Kan Matasan Arewa, wato ' Arewa Youth Mobilization Forum' zata karrama a kwanan nan.

Bayanin tabbatar da karrama Injiniya Kaikai da lambar yabon na a cikin wata takarda mai dauke da sa hannun Sakataren Yada Labaru na Kungiyar Kwamarad Yusuf Mahmud.

Kamar yadda takardar ta bayyana, za'a gabatar da lambar yabon ne ga hazikin matashin Ambasada Kaikai a lokacin wani babban taro da Kungiyar ta shirya zai gudana a Jihar Kaduna a ranar 29 ga wannan watan da muke ciki.

An dai karrama Kaikai ne bisa ga dogon nazari da bincike da Kungiyar ta gudanar akan ayyukan jin kan al'umma da yake gudanarwa, musamman a Mazabar shi ta Kankia/Ingawa/Kusada da ke Jihar Katsina.

Taron gabatar da lambar yabon zai gudana ne a 'Arewa House' kusa da Masallacin Sultan Bello da ke Kaduna a ranar 29 ga watan Oktoba da muke ciki da misalin karfe 4 na yamma, bayan Kammala daurin auren Shugaban Kungiyar.

Da Accuracy News ke zantawa da shi akan karamcin, hazikin matashin Ambasada Kaikai, ya nuna farin cikin shi akan yadda Kungiyar ta zabe shi daga cikin wadanda zata baiwa lambar yabon.

Injiniya Kaikai ya ce, karamcin zai kara mashi kwarin guiwa na cigaba da aiwatar da ayyukan taimakon al'umma, musamman marayu da masu karamin karfi, domin su san cewa an kula da su.

Ya yi fatan cewa al'umma zasu cigaba da taya shi addu'a akan Allah SWT ya kara bashi kwarin guiwar cigaba da taimakon mabukata.

Innalillahi Wa'inna Ilaihir Raji'un Allah ya yi wa Dan Isan Katsina Hakimin Rimye Alh. Yusuf Yakubu Rasuwa.Kamar Yadda M...
17/10/2022

Innalillahi Wa'inna Ilaihir Raji'un

Allah ya yi wa Dan Isan Katsina Hakimin Rimye Alh. Yusuf Yakubu Rasuwa.

Kamar Yadda Majiyar Horizon News Hausa ta tabbatar, Dan Isan ya rasu ne a cikin Daren jiya Lahadi da misalin ƙarfe 12.30am na dare a wata asibiti dake garin Kano.

Ya rasu ya bar mata da 'ya'ya da dama.

Za'a yi Jana'izar shi da misalin ƙarfe Biyu na Rana 2.00pm) Yau Litinin idan Allah ya kaimu lafiya, a garin Rimaye ƙaramar hukumar Kankia ta jihar Katsina.

Allah ya gafarta mashi, yasa Aljannah ta zama makoma a gare shi.

Cikin  Hotuna: Yadda Tawwagar Shehunnai Daga Jihar  Katsina S**a Halarci Taron Mauludin Annabi SAW A Kasar Mali.
17/10/2022

Cikin Hotuna: Yadda Tawwagar Shehunnai Daga Jihar Katsina S**a Halarci Taron Mauludin Annabi SAW A Kasar Mali.

Mai Dubu-Dubu Tata Ya Magantu Akan Ficewar Mustapha Inuwa Daga APC "Maganar matsala tsaro tunda aka kafa gwamnatin APC a...
16/10/2022

Mai Dubu-Dubu Tata Ya Magantu Akan Ficewar Mustapha Inuwa Daga APC

"Maganar matsala tsaro tunda aka kafa gwamnatin APC a jihar katsina wake shugabantar kwamitin tsaro, kuma ina kuɗaɗen da yake cewa, yana warewa domin taimakawa wajen shawo kan matsalar tsaron a baya?

"Ku tambayi Mustapha Inuwa sau nawa yana amfani da jami'an tsaro a k**a ni har gidan yari ake kaini, akan nace a kori yinwa, sai yace, na yiwa gwmanatin sa ƙazafi, don haka a kamo ni"

"Amma yanzu shine ke faɗar idan har APC na son sake cin zaɓe sai ta magance waɗannan, a tunani na ko da hakan gaskiya ne, to ba'a bakin sa ya k**ata aji hakan ba"

"Ɓarnar da Mustapha Inuwa da irinshi su ka yiwa Jihar katsina ba y'ar karama bace ba, don haka ina baiwa Dr. Dikko Radda shawara akan kada ya Ɓata lokaci wajen yin magana akan shi, mu tashi mu cigaba da shiga jama'a muna basu hakuri, domin yanzu sheɗanin daya kashe jihar yayi ƙaura zuwa wata sheƙar, don neman wata damar da zai ida kai jihar kabari".

Fastar Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina Dr.Mustapha Muhammad Inuwa Bayan Ficewar Shi Daga Jam'iyar APC  Zuwa PDP...
16/10/2022

Fastar Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina Dr.Mustapha Muhammad Inuwa Bayan Ficewar Shi Daga Jam'iyar APC Zuwa PDP.

Wane Fata Kuke Yi Mashi?.

Real Madrid Ta Lallasa Barcelona Da Ci 3 A El-Classico.
16/10/2022

Real Madrid Ta Lallasa Barcelona Da Ci 3 A El-Classico.

Sojin Saman Najeriya Sun Yi Luguden Wuta Akan Yan Ta'adda A Kaduna.....Sun Hallaka Rikakken Dan Ta'adda Ali Dogo Da Wasu...
11/10/2022

Sojin Saman Najeriya Sun Yi Luguden Wuta Akan Yan Ta'adda A Kaduna
.....Sun Hallaka Rikakken Dan Ta'adda Ali Dogo Da Wasu Yaran Shi.

Sojin Sama Sun Hallaka Shugaban Ƴan Bindiga Ali Dogo Da Wasu 30 A Kaduna

Rohotanni da ke shigo mana na nuni da cewar, Sojojin Najeriya sun kashe wani fitaccen shugaban ‘yan bindiga a jihar Kaduna, Ali Dogo, da mayakansa 30, k**ar yadda PRNigeria ta rawaito.

An bayyana cewa, an kashe Dogo, wanda aka fi sani da Yellow, tare da ‘yan kungiyarsa, sak**akon harin da jiragen yakin rundunar sojin sama su ka kai a karshen mako.

Da ta ke tabbatar da tashin bama-baman kan Yellow da mayakansa, wata majiyar leken asiri ta tsaro ta shaida wa PRNigeria cewa fitaccen shugaban ‘yan bindigar, da ‘yan ta’addansa sun gudu daga jihar Neja zuwa wani gidan Alhaji Gwarzo da ke Yadi a Ƙaramar Hukumar Giwa domin tsira da rayukansu, sak**akon ci gaba da ruwan bama-bamai da jiragen NAF s**a yi akan maɓoyarsa a Neja a kwanan nan.

Majiyar ta ce: “Abin takaici ga Yellow da mayakansa, yayin da su ke cikin taro, jirgin NAF ya kai hari gidan Alhaji Gwarzo, wanda ya sa duk wanda ke cikin ginin ya hallaka su ciki har da Yellow din”.

A halin da ake ciki kuma, PRNigeria ta kuma tattaro cewa an kai hare-haren bama-bamai a rana guda kan ‘yan ta’adda a wani wuri mai nisan kilomita 33 Arewa maso yammacin Mando a Kaduna.

“Bayan bayanan sirri na shugabannin ‘yan ta’adda da sojojinsu da ke taruwa a karkashin bishiya a wurin taron, an kashe ‘yan ta’adda da dama,” k**ar yadda wata majiya ta NAF ta shaida wa PRNigeria.

Air Commodore Edward Gabkwet, mai magana da yawun NAF, ya tabbatar da nasarar harin jiragen saman, inda ya ce, “Rundunar sojin sama bisa umarnin shugaban hafsan sojin sama, Air Marshal Oladayo Amao, za ta ci gaba da kai hare-hare kan wadannan miyagu tare da hadin gwiwar jami’an tsaro. Bangaren kasa da sauran hukumomin tsaro domin kawar da yankin na hadin gwiwa da ma yankin Arewa maso yamma gaba daya daga ayyukan ta’addanci da sauran ayyukan ta’addanci”.

Atiku Ya Nada Shema Kwamandan Yakin Neman Zaben Shi A Arewa Maso YammaDan Takarar Shugaban Kasa na Jam'iyar PDP Alhaji A...
11/10/2022

Atiku Ya Nada Shema Kwamandan Yakin Neman Zaben Shi A Arewa Maso Yamma

Dan Takarar Shugaban Kasa na Jam'iyar PDP Alhaji Atiku Abubakar, ya amince da nada tsohon Gwamnan Jihar Katsina Barista Ibrahim Shehu Shema, a matsayin kwamandan yakin neman zaben shi a shiyyar Arewa Maso Yamma.

Nadin Shema dai ya biyo bayan bude yakin Neman zaben Shugaban Kasa da aka yi, gabanin zaben shekarar 2023 da ke tafe.

Likkafar Jami'in Hulda Da Jama'a Na Hukumar Alhazai Ta Jihar Katsina Ta Daga.... Ya Zama Uban Kungiyar Wayar Da Kan Jama...
08/08/2022

Likkafar Jami'in Hulda Da Jama'a Na Hukumar Alhazai Ta Jihar Katsina Ta Daga
.... Ya Zama Uban Kungiyar Wayar Da Kan Jama'a Akan Kyawawan
Manufofin Yan Siyasa Ta Jihar Katsina

Kungiyar Da Ke Wayar Da Kan Jama'a Akan Kyawawan Manufofin Yan Siyasa Ta Jihar Katsina, ta nada Jami'in Hulda Da Jama'a na Hukumar Alhazai ta Jihar Alhaji Badaru Karofi, a matsayin Uban Kungiyar.

Shugaban Kungiyar Malam Abdulrashid Sule tare da wasu daga cikin Shuwagabannin Kungiyar ne s**a gabatar mashi da takardar bashi matsayin.

A cewar Shugaban Kungiyar, nadin Alhaji Badaru Karofi a matsayin Uban Kungiyar, ya biyo bayan aminta da s**a yi da nagartar shi ta fuskar rike mukamin.

Malam Abdulrashid Sule ya bayyana cewar, sabon Uban Kungiyar mutum ne mai kyakkyawar alaka da jama'a, wanda hakan ne ya ba Kungiyar sukunin ganin ya chachanta ta nada shi a matsayin.

Da yake maida jawabi, sabon Uban Kungiyar Alhaji Badaru Karofi, ya nuna farin cikin shi akan wannan karamchi da kungiyar ta yi mashi.

Alhaji Badaru Karofi ya sha alwashin yin aiki tukuru wurin sauke nauyunda kungiyar ta daura mashi domin tabbatar da an samu nasara bisa ga dalilin kafa kungiyar.

Ya kuma hiri Shugabancin Kungiyar akan bukatar kasancewa an yi aiki da hankali da natsuwa wurin mu'amalar su da wasu yan siyasa da zasu iya yin amfani da su wurin cimma kudirin su na son zuciya.

Akwai Kyakkyawan Yakinin Cewa Dr.Dikko Radda Ba Zai Ci Amanar Katsinawa Ba Idan S**a Bashi Dama A 2023 - Cewar Masanin T...
07/08/2022

Akwai Kyakkyawan Yakinin Cewa Dr.Dikko Radda Ba Zai Ci Amanar Katsinawa Ba Idan S**a Bashi Dama A 2023 - Cewar Masanin Tattalin Arziki Ibrahim Jikamshi

Kwararrarren Masanin Tattalin Arziki kuma masani akan sha'anin Masana'antun wanda kuma shine Shugaban Hukumar Zuba Hannun Jari Ta Jihar Katsina, Alhaji Ibrahim Tukur Jiƙamshi, ya bayyana cewa al'ummar jihar Katsina ba zasu yi da na sani ba idan s**a ba Dr.Dikko Umar Radda damar zama Gwamnan Jihar.

Alhaji Ibrahim Tukur Jiƙamshi ya bayyana hakan ne jim kaɗan bayan kammala wata ganawa ta musamman da dan takarar gwamnan jihar Katsina a karƙashin jam'iyyar APC, Dakta Dikko Umar Radda a Ofishin yakin neman zaɓensa dake cikin garin Katsina.

Jikamshi ya ja hankalin yan Jihar akan su fito kwansu da kwarkwatarsu su zazzaga wa Dr. Dikko Umar Radda kuri'unsu don ganin ya samu nasarar lashe zaɓen Gwamnan Jihar zabe mai zuwa.

Ya kara tabbatar da cewa ba za su taɓa yin nadama ba, saboda saboda gogewar Radda a fannoni daban-daban da s**a shafi cigaban al'umma da kuma tarin Ilimin Addini da na boko da yake da shi da kuma hangen nesa.

Shugaban Hukumar Kula Da Zuba Hannun Jarin ya kara da cewar, a wannan zaɓe mai karatowa na 2023, al'ummar jihar idan s**a dubi kafatanin yan takarar gwamnan jihar Katsina a jam'iyyu mabanbanta yana da wahalar gaske a samu nagartaccen dan takarar k**ar Dr. Dikko Umar Radda.

Al'ummar Najeriya gaba daya sun amfana da irin kyakkyawan shugabancinsa na yadda ya riƙe Hukumar Kula Da Kanana Da Matsakaitan Masana'antun Ta Najeriya da kuma irin sauye-sauye da ya kawo a Hukumar cikin shekara biyar.

Alhaji Ibrahim Tukur Jiƙamshi ya cigaba da cewa jihar Katsina ana buƙatar matashin dattijo irin Dr. Dikko Umar Radda saboda irin baiwa da basira da kokarin ganin ya inganta rayuwar al'umma musamman matasa da kuma Kananan Masana'antun wanda ya ke da gogewa akan fannin.

''Ina da tabbacin zai kawo sauye-sauye masu ma'ana da za su inganta rayuwar al'umma jihar Katsina idan har s**a bashi dama ya zama Gwamnan Jihar''.

Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Ma'aurata A Cikin Birnin Katsina.... Sun Harbe Yan Sintiri Biyu Har LahiraA Daren Ranar ...
07/08/2022

Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Ma'aurata A Cikin Birnin Katsina
.... Sun Harbe Yan Sintiri Biyu Har Lahira

A Daren Ranar Asabar Ƴan Bindiga Sun Kai Hari A Unguwar Shola Dake Bayan Asibitin Koyarwa Ta Gwamnatin Tarayya Da Ke Cikin Garin Katsina Inda S**a Yi Garkuwa Da Mata Da Mijinta.

Kamar Yadda Majiyar Mu Ta Shaida Mana, Matashin Da Aka Yi Garkuwa Da Shi Da Matar Sa Sunan Shi Yusuf Bishir.

Haka zalika yan bindigar sun harbe wasu yan sintiri biyu dake aikin bayar da tsaro a Unguwar inda s**a kashe daya daga cikin su yayin d

Anya Kuwa Dagaske Gyara Suke So, Ko Dai Wata Boyayyar Manufa: Zauren Ƴan APC A GyaraDaga Muhammadu BelloDuk dai Hausawa ...
06/08/2022

Anya Kuwa Dagaske Gyara Suke So, Ko Dai Wata Boyayyar Manufa: Zauren Ƴan APC A Gyara

Daga Muhammadu Bello

Duk dai Hausawa na cewa gyara kayanka bai zama sauke a raba ba, kwatsam aka yi gari a jihar Katsina aka samu wasu tsirarun matasa da s**a kira kansu Zauren APC A Gyara kuma sun kira kansu masu son kawo gyara da kishin Jam'iyyar APC shi ne babban dalilin kafa wannan zaure a jihar Katsina. Amma abun tambaya anan shi ne shin dagaske gyaran suke so? Kuma wadanne hanyoyi s**a biyo na ankarar da gwamnatin jihar Katsina da Jam'iyyar APC ta jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Alhaji Sani Aliyu Daura, wanda s**a yi ko kuwa akwai wata boyayyar Manufa?

Jam'iyyar APC ta jihar Katsina ta kammala zaɓukan Fidda-gwaninta a matakai daban-daban ba tare da nuna banbanci ba, wadda a tarihin siyasar jihar Katsina ba'a taɓa samun haka na baiwa yan takara dama su nemi Jama'a tare da kokarin baiwa kowa damarsa ta dan Jam'iyya. A Zaɓen Fidda-gwani gwamna da aka gudanar gwamna Aminu Bello Masari ya yi kokarin matuka don gani an baiwa kowa damarsa ba tare da nuna Dan Bora da Mowa ba, wanda da yawa Jama'a sun yadda da sahihanci yadda aka gudanar da zaben. Yanzu haka babu wani korafi gaban kotu. Amma kwatsam sai ga Waɗannan matasa sun fito da rana tsaka suna kira a Gyara to gyaran yadda aka gudanar da zaben Fidda-gwani da mafi yawancinsu wadanda suke goyawa ma baya, sun tsaya takara a matakai daban-daban, Allah bai ba su nasara ba, shi ne saboda Allah suke so a zo gyara, don uwayen gidansu ba su samu nasarar ba, ina da tabbaci da ace Iyayen gidansu sun yi nasarar lashe zaɓukan da s**a tsaya da babu daya daga cikinsu zai fito ya ce a Gyara!

Idan muka koma tafiyar da gwamnati, gwamna Aminu Bello Masari yau shekararsa bakwai yana tafiyar da gwamnati a jihar Katsina. Tsakani da Allah cikin Waɗannan shekaru ba su taba fitowa da wani Zauren APC A Gyara sai yanzu da bai wuce saura watanni wa'adin Gwamnatinsa. Anya kuwa dagasken gyara suke so kuwa? Kamar yadda da yawa daga cikinsu sun bayyana cewa tare da su aka sha wahalar aka kafa gwamnatin Gwamna Masari a shekarar 2015, ba su taɓa sunsunar kafa wannan zaure ba, saboda Allah fa al'umma jihar Katsina ku yi mana alkalanci! Amma s**a yi gum da bakunansu.

Maganar shugaban Jam'iyyar APC na jihar Katsina, Alhaji Sani Aliyu JB kuwa duk tsohan dan Jam'iyyar APC ya san irin rawar da ya taka, saboda shi ne Sakatarenta na farko daga likkafarsa ta cigaba ya zama shugabanta a shekarar 2021. Duk wanda ya matsa kusa da shi mutum ne mai amsar gyara da kuma kokarin ganin an tafiyar da Jam'iyyar cikin adalci. Ina da yakinin cikinsu babu wanda ya taɓa kokarin yin mu'amalla da shi ko shigar da wani korafi na kawo gyara ace ya hau teburin na ki ba. Idan za ka yi adalci, farko ka fara kusantarsa kafin ka yanke masa hukunci.

Ni da a fahimta ta ko dai suna da wata boyayyar manufa, wadda nan gaba kadan al'ummar jihar Katsina za su fahimci haka. Yanzu dai babu abinda Gwamnatin Jihar Katsina da Jam'iyyar APC ke bukata, illa hadin kai yayan Jam'iyyar, ga zabe na tahowa na 2023, idan har nasarar Jam'iyyar APC suke so kyau su zo su marawa Jam'iyyar Baya ganin ta lashe zaɓukan, sannan duk wani gyara a zo ayi shi.

Address

Batsari Road
Katsina

Telephone

+17033444156

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Horizon News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Horizon News Hausa:

Share