Zamani Media crew

Zamani Media crew News
Reports
Enlightenment
Entertainment
Photos Videos Editing
Adverts
Documentary
Film Making etc editors

10/06/2025
Zakarun musabaƙar Kur'ani da Sanata Lado ya shirya a Kano sun samu kyautar gidaje da Umrah da kuɗaɗe Ahmad Shuaibu, wand...
03/06/2025

Zakarun musabaƙar Kur'ani da Sanata Lado ya shirya a Kano sun samu kyautar gidaje da Umrah da kuɗaɗe

Ahmad Shuaibu, wanda ya wakilci ƙaramar hukumar Shanono a musabaƙar Kur'ani da Sanata Bashir Garba Lado ya shirya a jihar Kano ya lashe gasar a izifi 60.

Shuaibu ya samu kyautar gida da kujerar Umrah da kudi Naira miliyan 1 da kuma tallafin karatu daga gwamnatin Qatar har zuwa jami'a da kuma sauran kyaututtuka.

Itama Maryam Abubakar Muazu, wacce ta wakilci ƙaramar hukumar Dala ta kuma samu nasara s izifi 60, ta samu irin wannan kyauta.

Sauran wadanda su ka zo na 2 da na 3 a duk rukunan gasar su ma sun samu kyaututtuka da dama da su ka hada da babura mai kafa uku da mai kafa biyu da kudade da shaddoji da ayamfuna da tallafi karatu da sauran su.

Da ya ke jawabi a yayin rabon kyautukan, Lado, wanda aka fi sani da Ladon Alheri ya yi kira ga iyayen waɗanda su ka lashe gasar da su tabbata an yi amfani da kyaututtukan ta inda ya dace.

Ya ce ya shirya musabaƙar ne domin tunawa da irin aiyukan alheri da mahaifiyar shugaban kasa, Hajiya Abibat Mogaji Tinubu ta yi kafin rasuwar ta.

A cewar Lado, an shirya musabaƙar ne duba da muhimmancin karanta Kur'ani da don ladan da ake samu wajen karanta shi, inda ya kara da cewa an biyawa zakarun Umrah ne domin su kara samun tsoron Allah da kyawun zuciya.

DAILY NIGERIAN HAUSA ta rawaito cewa an kwashe tsawon wata daya ana fafatawa a musabaƙar.

Jami'in 'Civil Defence' ya tsinci guzirin wata maniyyaciya a sansanin alhazai na Yola ya kuma mayar mataWani Jami’in huk...
18/05/2025

Jami'in 'Civil Defence' ya tsinci guzirin wata maniyyaciya a sansanin alhazai na Yola ya kuma mayar mata

Wani Jami’in hukumar tsaro ta 'Civil Defence' mai suna Abubakar Abdulƙadir Mayos, ya mayar da kuɗin guzirin wata maniyyaciya da ya tsinta, har Dalar Amurka $505 da Riyal 30 na Saudiyya a sansanin alhazai na birnin Yolan Jihar Adamawa ya kuma miƙa su ga mai su.

Rahotanni sun baiyana cewa kuɗaɗen mallakar wata maniyyaciya, mai suna Maimuna Salihu Abdullahi, ƴar Jihar Taraba.

Nan take, a cewar rahotanni ya mayar da kuɗin ga jami'an alhazai inda su kuma ba su yi wata-wata ba su ka miƙa mata kayanta a gaban jami’in hukumar NAHCON da daraktan tsare-tsare na hukumar alhazai ta Taraba da sauran jami’ai.

Gabanin zaben gwamna da za a yi a ranar 8 ga Nuwamba, 2025 a jihar Anambra, jam’iyyar People’s Democratic Party ta kafa ...
29/04/2025

Gabanin zaben gwamna da za a yi a ranar 8 ga Nuwamba, 2025 a jihar Anambra, jam’iyyar People’s Democratic Party ta kafa wani kwamitin dabarun yakin neman zabenta da sauran tsare-tsare.

Da Dumi-Dumi : Gwamnan Jihar Delta, Sheriff Oborevwori, ya fice daga PDP zuwa APCGwamnan Jihar Delta, Rt. Hon. Sheriff O...
23/04/2025

Da Dumi-Dumi : Gwamnan Jihar Delta, Sheriff Oborevwori, ya fice daga PDP zuwa APC

Gwamnan Jihar Delta, Rt. Hon. Sheriff Oborevwori, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyar APC.

Sanarwar ta fito ne bayan wani taro na manyan gwamnati da aka gudanar a gidan gwamnati da ke Asaba, babban birnin jihar a yau Laraba.

~ Daily Nigerian Hausa

Gwamnatin jihar Katsina ta kashe Naira biliyan N36.7 don inganta tsaron al'ummar jihar Katsina - Mataimakin gwamnan jiha...
23/04/2025

Gwamnatin jihar Katsina ta kashe Naira biliyan N36.7 don inganta tsaron al'ummar jihar Katsina - Mataimakin gwamnan jihar Katsina ya fada wajen yi wa yan jaridu bayanin abin da jihar ta gudanar

Wallahi idan kaga Shugaba Tinubu bai dawo ba a zaben 2027 sai dai in mutuwa ya yi, inji ƴar siyasa a jam'iyyar APC Marya...
23/04/2025

Wallahi idan kaga Shugaba Tinubu bai dawo ba a zaben 2027 sai dai in mutuwa ya yi, inji ƴar siyasa a jam'iyyar APC Maryam Kofar Mata

Ta bayyana hakan ne ta cikin shirin (Podcast) na Jaridar Dokin Ƙarfe TV.

Bayan gama kushe Jam'iyyar APC da Kwankwaso Yayi da Kiran duk Wanda yazabeta, A Matsayin Mara Hankali,Yanzu Haka Rahoton...
23/04/2025

Bayan gama kushe Jam'iyyar APC da Kwankwaso Yayi da Kiran duk Wanda yazabeta, A Matsayin Mara Hankali,

Yanzu Haka Rahotonni nuna Cewa Kwankwaso na Shin shina Jam'iyyar APC Saboda Nemawa Kansa Makoma A zaben 2027

~ Cewar Abdullahi Ahmad

DA DUMI-DUMI: Jama'a barkanmu da warhaka. Bayanai da ke shigowa ya nuna cewa shahararren mai fafutukan kwatar yancin bil...
22/04/2025

DA DUMI-DUMI: Jama'a barkanmu da warhaka.

Bayanai da ke shigowa ya nuna cewa shahararren mai fafutukan kwatar yancin bil-adama, wato "Ordinary President" Ahmed Isah, yana bukatan addu'a ta musamman domin yana cikin sarkakiya.

Allah Ubangiji Ya kawo masa dauki na gaggawa....

-Daga Idris Ahmed shugaban kungiyar CUPPS

Address

Katsina Liyafa Junction
Katsina
180101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zamani Media crew posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zamani Media crew:

Share