Triple H Multimedia

Triple H Multimedia Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Triple H Multimedia, News & Media Website, Katsina.

Acigaba da ganawar da Mai girma Jagoran Adawar Siyasar Jihar Katsina Malam Dr Mustapha Muhammad Inuwa Tsohon Sakataran G...
07/09/2025

Acigaba da ganawar da Mai girma Jagoran Adawar Siyasar Jihar Katsina Malam Dr Mustapha Muhammad Inuwa Tsohon Sakataran Gwamnatin Jihar Katsina Yakeyi da Al'umma badare ba Rana.

Ayau Lahadi 7/9/2025.

Mai girma Jagora Yagana da Wasu Kungiyoyi guda 4 wadanda S**a Fito daga kananan Hukumomi daban daban dake Fadin Jihar Katsina baki daya.

Kungiyoyin Sune kamar haka.

1 Dr. Mustapha Muhammad Inuwa Awareness and Mobilization katsina State.
2 Salamah Foundation.
3 Rahamawa star's Youth Assistance ( K..R.S )
4 Dandagoro Youth Development And Mobilization Forum.

Alh. Sufiyanu Halliru Shine Shugaban Wannan Kungiya ta Dr. Mustapha Muhammad Inuwa Awareness and Mobilization.

Hajiya Sale itace Shugabar Wannan Kungiya ta Salamah Foundation.

Comrd. Abba Aminu Ibrahim Shine Shugaban Wannan Kungiya ta Rahamawa star's Youth Association.

Mal. Lukuman Usman Abubakar Shine Shugaban Wannan Kungiya ta Dandagoro Youth Development And Mobilization Forum.

Dukkannin Wadannan Shuwagabannin Kungiyoyi Sun Sanar da Mai girma Dr. Mustapha Inuwa Cewa sunkawo Wannan Ziyara Ne domin S**ara Jaddada goyan Bayan su Akan Wannan Sabuwar Jam'iyya ta ADC Anan Jihar Katsina Akalkashin Jagorancin Shi.

Anashi Jawabin Dr. Mustapha Inuwa Yayi dogon Jawabi tare da Kara Kira dakuma bada Shawara ga daukacin Wadannan Yan kungiyoyi Cewa.

S**ara Tashi tsaye domin Shiga Cikin Hidimar Siyasa Amatsayin su Na Matasa Masu takawo domin Sune Shuwagabannin Gobe.

Daga Karshe Kuma Yasake Kira ga Wadannan Shuwagabannin Kungiyoyi Cewa Yazama Wajibi sushiga Lungu da Sako domin Kara wayar da Kawunan Al'umma Akan Wannan Sabuwar Tafiya ta Jam'iyyar ADC Anan Jihar Katsina.

Anas Sulaiman Kbai
CEO Triple H Multimedia

*NIGERIA NA CIKIN WAHALA DA RUDANI KARKASHIN  SHUGABA BOLA AHMAD TINUBU*Idan ba a ɗauki mataki na gaggawa ba, ƙasar na i...
07/09/2025

*NIGERIA NA CIKIN WAHALA DA RUDANI KARKASHIN SHUGABA BOLA AHMAD TINUBU*

Idan ba a ɗauki mataki na gaggawa ba, ƙasar na iya nitsewa cikin rikici.

Najeriya a yau tana cikin rudani, Ƙasar da da ake kira maikarfi wadatatta da yalwar albarkatun ɗan Adam da na halitta, yanzu ta makale cikin mugun yanayi na talauci, yunwa da rashin tsaro a ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Miliyoyin ’yan Najeriya suna fama da wahalar rayuwa a kullum.

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ruwaito cewa hauhawar farashin kaya ya tsaya a kashi 21.88% a watan Yuli 2025, ƙasa da kadan daga watan da ya gabata. Abin da ya fi tayar da hankali shi ne hauhawar farashin abinci wanda ya haura zuwa kashi 22.74%, lamarin da ya sa kusan ba zai yiwu iyalai su iya sayen abincin yau da kullum ba. A ƙauyuka, garuruwa da birane, yunwa ta addabi ’yan ƙasa.

Talauci ya kai wani mataki mai tayar da hankali. A shekarar 2023, kusan ’yan Najeriya miliyan 104 wato kashi 47% na al’umma – suna rayuwa ƙasa da layin talauci. Babban Bankin Duniya ya yi hasashen cewa nan da shekarar 2027, talauci zai shafi kashi 56% na ’yan Najeriya, wato fiye da rabin jama’ar ƙasar za su fada cikin ƙangin ƙunci. A shekara guda kacal, kusan ’yan Najeriya miliyan 10 sun ƙara shiga cikin talauci sakamakon manufofin gwamnati Bola Ahmad Tinubu

Batun rashin wadatar abinci ya fi muni. Majalisar Ɗinkin Duniya ta kiyasta cewa zuwa karshen 2025, kusan ’yan Najeriya miliyan 31 za su kasance cikin haɗarin yunwa mai tsanani, inda rashin tsaro ke ƙara tsananta matsalar. Ambaliyar ruwa ta lalata fiye da hekta miliyan 1.5 na gonaki musamman a Arewacin Najeriya, ta tilasta iyalan manoma barin gonakinsu tare da barazana ga samar da abinci. Wannan, a ƙasa mai yalwar ƙasa mai noma, shaida ce ta rashin tsari da jagoranci mara hangen nesa.

Rashin aikin yi na ci gaba da zama bam din da ke jira ya fashe. Ko da yake hukumomi sun bayyana cewa rashin aikin yi ya tsaya a kashi 4.84% a 2025, wannan adadi bai bayyana gaskiyar halin matsalar ba. Miliyoyin matasa masu digiri, HND, diploma, NCE da Masu takardun kammala secondary suna zaune Gwamnati ta kasa samar da yanayi mai kyau na masana’antu da samar da ayyukan yi.

Rashin tsaro na daga cikin manyan kalubalen Najeriya. Hare-haren ta’addanci a Arewa maso Gabas, ’yan fashi da makami a Arewa maso Yamma, rikice-rikicen makiyaya a tsakiyar Najeriya, garkuwa da mutane a Kudu, da rikice-rikicen birane na ci gaba da kashe rayuka a kullum. Yayin da Sace mutane da garkuwa dasu tare da kashesu a Arewa masu yamma yake kara ta'zzara Yan ƙasa yanzu na rayuwa cikin tsoro, ba su da tabbacin komawa gida lafiya. Ko zasu kai gobe ba tare da ankai masu hariba

Gwamnati Nigeria ba za ta iya tabbatar da tsaro ba ta gaza a mafi yawancin alkawurran data dauka

Rashawa da son kai suna ci gaba da bayyana . Ana naɗa mukamai ba a bisa cancantaba ko ƙwarewa ba, ana ƙara farashin kwangila, kuma ba a bin diddigi. Sakamakon haka, jama’a sun daina amincewa da gaskiyar gwamnati. Misalin irin wannan ya faru a Jami'ar zurgazurga ta Daura (University of Transport) da Dr. Bala Usman College of Education and legal studies Daura inda s**a nada University Librarian da College librarian ba'a bisa kaida ba.

Kamfanoni na rufewa saboda manufofin gwamnati marasa tabbas, haraji mai tsanani da rashin tsaro. Masu zuba jari na gudu zuwa wasu ƙasashe.

Idan ba a ɗauki mataki ba, ƙasar na iya nitsewa cikin rikici.

Dole a farfaɗo da noma masana’antu a tallafa musu, a kirkiro ayyukan yi.

’Yan Najeriya kansu ba su kamata su zauna shiru ba. Jama’a dole su tashi a hade wajen neman gaskiya daga shugabanni. Dole su yi amfani da muryoyinsu da ƙungiyoyinsu wajen tabbatar da cewa shugabanci na yi wa jama’a hidima, ba wasu ƴan tsiraru masu iko ba. Dimokuraɗiyya tana bunƙasa ne kawai idan jama’a sun kasance masu faɗa a ji, masu lura da kuma jarumta.

Yayin da kasa ke tunkarar zaben 2027, amincin tsarin zaɓe ba abu ne da za a yi wasa da shi ba. Zaɓe shi ne ginshiƙin dimokuraɗiyya, kuma idan jama’a sun rasa amincewa da tsarin, dimokuraɗiyya kanta ta shiga haɗari. Saboda haka, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) dole ta kasance adala.

Dole mu yi addu’a da kira ga INEC da hukumomin tsaro su kasance masu gaskiya, adalci, da rashin nuna bambanci. Su ba dukkan jam’iyyun siyasa da ’yan takara damar yin zaɓe a fili ba tare da magudi ba ko nuna bambanci ba. Ta haka ne za'a iya karfafa dimokuraɗiyya kuma a kiyaye haɗin kan Najeriya.

zabukan ƙasa na 2027 ke gabatuwa, muna kira ga Gwamnatin Tarayya, INEC da hukumomin tsaro da su kare dimokuraɗiyyar Najeriya.

Yin adalci a zaben 2027 shi kadene zai nuna makomar Kasarnan. Idan kuma Gwamnati tayi amfani da zalunci a zaben 2027 zai iya kawoma Kasarnan matsala karin tashe tashen kankulla

*Kabir Ibrahim Kangi Ph.D*

Welcome Home H.E Atiku Abubakar Our National Daddy 🤝👊
06/09/2025

Welcome Home H.E Atiku Abubakar Our National Daddy 🤝👊

‎Akaddamar da sabuwar Kungiyar Katsina State ADC Action Awareness Forum Karkashin Shugabancin Amb. Aminu Mai Gwanjo a gi...
06/09/2025

‎Akaddamar da sabuwar Kungiyar Katsina State ADC Action Awareness Forum Karkashin Shugabancin Amb. Aminu Mai Gwanjo a gidan Jagoran Hadaka Na Jahar Katsina Dr Mustapha M Inuwa

‎A yau 06 Sep 2025 Dr Mustapha M. Inuwa ya kaddamar da shugabannin kungiyar mai suna a sama wadda, Amb Aminu Maigwanjo zaici gaba da jagoranta,

‎A lokacin da yake gabatar da shugabannin kungiyar Dr Mustapha M Inuwa yanuna Jindadin sa matuka kan yadda yaga Matasa ne kusan kashi 80 na shugabannin inde yace gaba dacewa dama shi tsari na ADC shine mafi yawancin shugabannin ta dole su kasamce Matasa da Mata to da Alama ita kanta wannan kungiyar ta dauka hanyar bama, Mata da Matasa dama domin adama dasu

‎D Mustapha Inuwa yakara kira ga Shugabannin da suji Tsoron Allah sukuma jajirce domin Kungiyace ta Yan Adawa dole anaso acire kwadayi da Tsoro inde Nasara akae nema kuma ya gwada yanada tabbaci akan mutanen da yagani zasu jagorancin Kungiyar Yasan zasuyi duk abunda yadace dan ganin kungiyar da Ita kanta Jam'iyar sunyi Nasara

‎Shima A lokacin dayake Tofa albarkacin Bakinsa Hon Aminu Musa Karofi ya gwada jin dadinsa yadda yaga al'ummar jahar Katsina sunata fahimtar manufofin jam'iyar ADC yakuma yi kira ga Shugabannin kungiyar dasu tashi tsaye su shiga lungu da sako s**ara fadakar da Al'umma kan muhimmancin kanti zabe da ake cikin yi yanzu haka,

‎Hon Karofi yakara da cewa mutane sunyi fushi suna fadin basu karayin zabe saboda ko ka zaba baza'a baka wanda kazaba ba kuma wanda akabamawa baiyin abunda yadace, Karofi yace wannan kungiya tana daya gamasu alhakin tashi tsaye dan fadakar da alumma illar kinyin katin zaben.

‎A lokacin da yake maida jawabinsa shugaban Kungiyar Amb Aminu Maigwanjo yayi godiya a madadin kubgiyar akan yadda Dr Mustapha da yan tafiyarsa suk tarbe shi tare da bama shugabannin kungiyar shawarwari masu kyau da kara daura Uwar kungiyar kan hanyar data dace yadda za'a ciyar da jam'iyar ADC da ita kanta kungiyar Gaba dan haka yace yana kara bada tabbacin Insha Allah wannan shawarwarin bazasu aje ko daya ba zasuyi amfani Dasu duka


‎Amb Maigwanjo yakara dacewa Ita wannan kungiyar Ba'irin sauran kungiyoyi bane irin na siyasa kungiyace wadda yana da tabbacin tun zuwan ADC babu wata kungiya da aka gina, gini mai inganci sama da wannan kungiya kuma insha Allah za'aga ayyukanta akasa daga karshe yayi godia da fatan Alkhairi

Anas Sulaiman Kbai

06/09/2025

‎Daga Gidan Dr Mustapha M Inuwa Ake Tabbatar da sabuwar Kungiyar Katsina State ADC Action Awareness Forum Karkashin Shugabancin Amb. Aminu Mai Gwanjo

06/09/2025

Daga Bakin Mataimakin Shugaban Jam'iyar ADC na Jahar Katsina, Hon Umar Shu'aibu

06/09/2025

Kira Na Musamman Daga Bakin Shugaban Matasan Jam'iyar ADC na Jahar Katsina Hon Aliyu Umar Sarkin Yaki. Akan Muhimmancin Yankan Katin Zabe

Shugaban Jam'iyar ADC na jahar Alhaji Musa Usman Wamba yayi kira ga al'ummar jahar Katsina dasu fito su yanki katin jefa...
05/09/2025

Shugaban Jam'iyar ADC na jahar Alhaji Musa Usman Wamba yayi kira ga al'ummar jahar Katsina dasu fito su yanki katin jefa kura'a da hukumar Zabe mai zaman kanta ta fara a fadin kasar

‎A Yau juma'a 5 Sep 2025 Mai girma shugaban Jam'iyar ADC na jahar katsina yayi wannan kira ne ga al'umma ta bakin mataimakin Hon Umar Shu'aibu a yayin gudanar da taron Shugabannin jam'iyar ADC na kananan Hukumomin wanda taron ya wakan a Babban Ofishin Jam'iyar na Jaha dake cikin Birnin Katsina.

‎Hon Umar Shu'aibu Yakara godewa shugannin da s**a hada Sakatere, Shugabar Mata da Shugaban matasan jam'iyar duk na kananan Hukumomi 34 dake fadin jahar akan namijin kokarin da suke wurin tabbatar da jam'iyar ta shiga lungu da sako na jahar, Ya kara dacewa shugaban Jam'iyar Alhaji Musa Wamba ne yace ayi wannan godiyar a madadinshi

‎A lokacin da take nata jawabin Shugabar matan ADC na jahar Katsina Hajiya Hauwa Jibrin (Yargata) tayi kira ga shugabanni matan na kananan hukumomin jahar Katsina da suci gaba aikin da suke na tallata jam'iya a duk inda s**a samu kansu misali Gidan suna, gidan Biki, kasawa Wurin saye da sayarwa da sauran su.

‎Hon YarGata taci gaba dacewa mata sune zabe domin sune masu jurewa duk zafi zasu tsaya suyi zabe kuma sune ake saurin yaudara da dan abu kalilan a canja musu tinani dan haka aikine gare mata kutashi ku wayar ma mata da kai akan wannan muhimman batutuwan.

‎Shima shugaban Matasan Jam'iyar ADC na jahar Katsina Hon Aliyu Umar (Sarkin Yaki) ya kara godewa matasan jam'iyar Musamman Wa'inda ke amfani da kafafen sadar wurin tallata jam'iyar da Fadin manufofinta na Alkhairi ga mutanen jahar katsina, Haka kuma Hon Sarkin Yaki yaci gaba da cewa jam'iyar ADC Jam'iyace wadda take da nagartattun shugabanni tunda daga sama harkasa musamman nan Jahar Katsina da Allah yabamu shugabannin Jam'iya da S**a Hada. Alhaji Musa Wamba, Dr Mustapha M Inuwa, Sanata Ahmad Babba Kaita, Sanata, Surajo Aminu Makera, Arch Ahmed Aminu Yar'adu, Sanata Sadiq Yar'adua dadai sauran su


‎Sakataren Jam'iyar Hon Junaidu Lawal ne Yayi jawabin godiya a madadin Uwar Jam'iyar ta jaha yakumayi Addua Allah yamaida kowa gidansa lafiya

‎Anas Sulaiman Kbai
‎Triple H Multimedia

ADC TA SHIRYA TSAF DON MAYAR DA ZAMAN LAFIYA DA TSARO A JIHAR KATSINA DA MA WURARE DABAM-DABAMƘungiyar Masu Tallata Jam’...
05/09/2025

ADC TA SHIRYA TSAF DON MAYAR DA ZAMAN LAFIYA DA TSARO A JIHAR KATSINA DA MA WURARE DABAM-DABAM

Ƙungiyar Masu Tallata Jam’iyyar ADC ta Farko a Jihar Katsina tana bayyana damuwarta kan bayani da Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi kwanan nan game da ƙalubalen da gwamnatinsa ke fuskanta wajen magance matsalar rashin tsaro. Duk da kasancewar suna da fasahar zamani don bin sawun ‘yan ta’adda, gwamnatin jiha na fuskantar cikas sakamakon tsarin tsaro da ke karkashin ikon cibiyar Abuja kawai.

Sharhi

Wannan gaskiyar mai ban takaici ta nuna bukatar gaggawa ta sauya salon shugabanci da tsarin kula da tsaro a yankinmu. Jam’iyyar ADC na da imani cewa shugabanci ya zama mai hangen nesa, mai mayar da hankali kan al’umma, kuma ba ya gajiya wajen yaki da rashin tsaro.

Saboda haka, muna tabbatar wa da mutanen Jihar Katsina da ‘yan Najeriya gaba ɗaya cewa matsalar ‘yan fashi da duk wani nau’in laifi za a magance su gaba ɗaya idan aka ba ADC dama ta shugabanci. Jam’iyyarmu ta kuduri aniyar:

• Gyara tsarin haɗin gwiwar tsaro don samun saurin martani a matakin ƙasa. • Ƙarfafa al’umma da kayan aiki, horo, da albarkatu don kare kansu tare da haɗin gwiwa da hukumomin tsaro. • Zuba jari a fannin leƙen asiri da fasaha don bin sawun da kuma dakile ƙungiyoyin laifi. • Magance tushen matsalolin rashin tsaro ta hanyar bunƙasa tattalin arziki, ilimi, da haɗa kai da al’umma.

Tsaron rayuwar al’umma ba abu ne da za a yi sassauci a kai ba. ADC ta shirya tsaf don dawo da zaman lafiya, mutunci, da bunƙasa ga kowace al’umma a Jihar Katsina da ma ƙetare.

Ambassador Yakubu Mamman Rumah
Coordinator Ƙungiyar Masu Tallata ADC ta Farko a Jihar Katsina
5/8/25

05/09/2025

Abunda ke Faruwa garuruwan Katsina, Kebbi da Kaduna. Daga bakina Mai Girma Sanata Aminu Waziri Tambuwal

04/09/2025

DIST Ahmad Babba Kaita da Malam M Inuwa sunce a fadama yan Apc Idan angama Medo Raddi akwai sabon Topic da zasu bada

Address

Katsina

Telephone

+2348032771891

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Triple H Multimedia posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Triple H Multimedia:

Share