Dandume Reporters

  • Home
  • Dandume Reporters

Dandume Reporters Ingantattun Labarai Ba Tare Da Cin Mutuncin Kowa Ba Shine Manufar Wannan Feji.

Fuskar sabon shugaban karamar hukumar Dandume kenan Hon. Bashir Sabi'u Gyazama.Allah ubangiji ya bada ikon sauke nauyi. ...
15/04/2025

Fuskar sabon shugaban karamar hukumar Dandume kenan Hon. Bashir Sabi'u Gyazama.

Allah ubangiji ya bada ikon sauke nauyi. Amen

Ubangiji Allah ya kawo sauki wa Alummar birnin Maiduguri da ambaliyar ruwa ta afka musu. Allah ya basu mafita na Alkhair...
10/09/2024

Ubangiji Allah ya kawo sauki wa Alummar birnin Maiduguri da ambaliyar ruwa ta afka musu. Allah ya basu mafita na Alkhairi.

Tsohon shugaban riko na karamar hukumar Ɗandume Alh Haruna Ja Abdullahi ya rasuAllah mai kowa mai komai ya yi wa tsohon ...
21/11/2022

Tsohon shugaban riko na karamar hukumar Ɗandume Alh Haruna Ja Abdullahi ya rasu

Allah mai kowa mai komai ya yi wa tsohon shugaban riko na karamar hukumar Ɗandume Alh Haruna Ja Abdullahi rasuwa sakamakon gajeruwar jinya.

Muna rokon Allah Ya ji kansa Ya gafarta amin

Majalisar jihar Katsina tayi wata bita ta kwanaki kan matsalar tsaro data addabi jahar, kamar yadda tsohon kakakin majal...
19/08/2022

Majalisar jihar Katsina tayi wata bita ta kwanaki kan matsalar tsaro data addabi jahar, kamar yadda tsohon kakakin majalisar Rt. Hon Aliyu Sabi'u Muduru ya wallafa a shafinsa na facebook. Allah ya sa bitar ta amfanar da al'ummar Jahar Katsina musamman kan abinda akayi bitar domin sa Amen.

28/07/2022

A karɓa da haƙuri...

Tsananin kaiwa Number 9 a munafurci ne wani azzalumi yace maka wai laifukanmu ne ya hanamu zaman lafiya kana ya kawo bala'in ta'addancin da ake mana...

Ba wai kuma ina nufin laifi ba zai zama fitina ba, a'a amma dai tsananin ƙin Allah ne wani wanda lokacin gwamnatin baya bai san ana laifin ba sai yanzu don ya kai almuri yace wai ai laifin mune...

Akwai ƙasashen duniya da duk wani laifi da kasan anayi a Nigeria to can an ninkashi (saurari wa'azizzikan Sheikh Bashir Ɗanfili Sokoto). Misali akwai ƙasashen da sun halarta auren jinsi da zina a fili da shan giya da rushe masallatai ma, kai da sauran nau'ikan laifukan da ba don Allah yasa munzo a zamanin fiyayyen halitta ba, da yanzu wani zancen ake, amma waɗannan ƙasashe sune kan gaba a zaman lafiya, saboda adalcin shuwagabanninsu.

Ya kamata mu sani cewa komin yadda kafirci yake yakan zama cikin salama inda adalci, akasin haka kuma kan faru da Musulunci ko shakka babu..

Ba wani ɗan iska a Nigeria da zaice wai laifinmu yasa ƴan ta'adda ke kashemu malam, Allah ya jarabcemu da asalin azzaluman shuwagabanni ne kawai a sama kana ya jarabcemu da azzaluman malamai da a bakinsu kaɗai Allah yake...

Kuma ai ya kamata mu sani shin su laifukan da ake cewa daga 2015 zuwa yanzu ne aka fara su don haka sai yanzu hukuncin yazo?

Allahumma dammirhum tadmira.🙏

Innalillahi wa inna ilaihi rajiun 😭Allah yayiwa mahaifin Alh Abubakar Salisu Asas rasuwa.Alh Abubakar Asas shine dan tak...
10/07/2022

Innalillahi wa inna ilaihi rajiun 😭

Allah yayiwa mahaifin Alh Abubakar Salisu Asas rasuwa.

Alh Abubakar Asas shine dan takarar kujerar majalisar tarayya da zai wakilci kananan hukumomin Funtua da Dandume a zaben 2023 karkashin jam'iyar PDP.
Muna addu'a Allah gafartawa mahaifin nasa ya sa aljanna makomarsa Amen.

Innalillahi wainna ilaihi rajiun 😭Yan ta'adda sun kashe DCP Aminu Umar area commander na dutsimma da yammacin yau talata...
05/07/2022

Innalillahi wainna ilaihi rajiun 😭

Yan ta'adda sun kashe DCP Aminu Umar area commander na dutsimma da yammacin yau talata 5/7/2022.

An ruwaito cewa barayin sunyi musu kwanton bauna ne, kuma s**a halaka shugaban yan sandan

Muna Addu'ar Allah ya gafarta masa ya kyautata makwancinsa Amen

Sabon Alkalin Alkalan Nigeria Kenan, Justice Olukayode Ariwoola.
27/06/2022

Sabon Alkalin Alkalan Nigeria Kenan, Justice Olukayode Ariwoola.

Dan Karamar Hukumar Dandume Ya Zama Dan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa A Jam'iyyar APP.
25/06/2022

Dan Karamar Hukumar Dandume Ya Zama Dan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa A Jam'iyyar APP.

15/06/2022
MU NA NAN A APC...Daga Lawal Hudu Dandume.Kasan wani baida gadonka amma yana da gadon maganar ka, cece-kuce yayi yawa ak...
10/06/2022

MU NA NAN A APC...

Daga Lawal Hudu Dandume.

Kasan wani baida gadonka amma yana da gadon maganar ka, cece-kuce yayi yawa akan batun wai Baba Hon Haruna Goma ɗan majalisar mu mai wakiltar ƙaramar hukumar Ɗandume karo na biyu kuma shugaban kwamitin muhallin jihar Katsina ya bar Jam'iyyar APC...

Wannan labari ne mara tushe kuma shaci faɗi da wasu waɗanda suke ganin in sune a matsayin shi to haka zasuyi, niko nasan in har Baba ya bar APC to Insha Allah bana tunanin zan wuce mutum goma na farko da zasu fara sani....

Koda ma mukayi magana da Baba Hon Haruna Goma sai ya kashe mun jiki da cewa " Karka manta fa munyi takara a 2015 mukayi nasara, muka nemi tazarce 2019 mukayi nasara, muka ɗaga hannun Alh Yahaya Nuhu Mahuta shima yayi nasara, muka nemi kujerar reps Allah ya bawa waninmu, to kenan in muka bar Jam'iyyar me muke nufi kenan? Shin Ubangijin dake badawa a APC kenan bashi bane a sauran jam'iyyun? Kenan mun munanawa Allah zato cewa sai a wani wuri zai bamu, ba zamuyi haka ba" Inji Baba....

Muna nan daram a APC damu aka ƙirƙireta kuma asalima nina fara cin gajiyarta a duk faɗin ƙaramar hukumar Ɗandume don kuwa ni na fara cin zaɓen fidda gwani a cikinta gaba ɗaya...

Ba kuma zamu zama irin wasu da s**a bar tasu jam'iyyar s**a dawo wata ba saboda rasa mulki cikin yan satittika ba kamar yadda ya faru a baya..

"Sai dai ba dalilin da baka nememu a hidimarka ba mu shiga ko mu tura yaranmu su shiga wannan kam ba dalili"...

"Kuma ma a halin da muke ciki ya kamata ne duk mai takara a APC ya himmatu wurin neman hanyar nasarar jam'iyyar ba wai cin zarafin wanda kayi takara tare dasu ba"..

"Akwai matakai da yawa da zamu taimaki APC a matsayinta na jam'iyyar mu wanda yasha banban da irin taimakon da ɗan takara kuma zai iya samu, don munyi gogewar rarrabe su a ma'auni na siyasa".. Inji Baba..

"Duk bamu san me Allah zaiyi gobe ba amma dai maganar barin APC ba gaskiya bane kuma muna cikinta kuma muna tare da waɗanda s**a ga cewa muna da muhimmiyar rawa da gudummawar da zamu basu ba cin mutumci ko cin zarafi ko habaici ko yafice ko muzgune b***e kuma zagi da ƙazafi"...

Allah ya tabbatar mana da dukkan alkhairi ya kuma ƙara dauwamar mana da zaman lafiya a dukkan ƙasarmu da sauran ƙasashen Musulmi Amen.

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Katsina ya sayi fom ɗin takarar gwamnaMe fatan ku gareshi?
27/04/2022

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Katsina ya sayi fom ɗin takarar gwamna

Me fatan ku gareshi?

Address


Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dandume Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

  • Address
  • Alerts
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share