Gaskiya Da Gaskiya

  • Home
  • Gaskiya Da Gaskiya

Gaskiya Da Gaskiya An samar da wannan dandali domin kawo masu bibiyar shi sahihan labarai daga ko'ina a fadin duniya.

Wata soja ta yi wuf da Sanata Kawu Sumaila Sanatan mai wakiltar Kano ta Kudu, Abdulrahman Kawu Sumaila, ya auri Aisha Is...
18/11/2025

Wata soja ta yi wuf da Sanata Kawu Sumaila

Sanatan mai wakiltar Kano ta Kudu, Abdulrahman Kawu Sumaila, ya auri Aisha Isah, wata jami’ar soja da ke aiki a rundunar Sojin Saman Najeriya.

Daily Trust ta rawaito cewa an ɗaura auren ne a fadar Sarkin Rano da ke Jihar Kano a jiya Litinin da safe.

Mataimaki na musamman ga Kawu Sumaila kan yada labarai, Muttaqa Babire, ya tabbatar da wannan labari a wani rubutu da ya wallafa a Facebook, inda ya wallafa hoton sanatan tare da amaryarsa wacce ke sanye da kayan soji.

Shi ma wani mataimaki nasa, Ahmad Tijjani Salisu Kiru, ya wallafa: “JUST IN: Alhamdulillah, yau 17-11-2025, Sanata S.A. Kawu Sumaila OFR PhD ya ɗaura aure a Rano. Allah ya albarkaci wannan aure ya bada zuriya ta gari.”

Babu wata sanarwa a bayyane kafin auren, kuma hotunan daga wurin sun nuna cewa ba a yi gaiya wajen daura auren ba.

Yan Nijeriya zasu yi kewar shugaba Bola Tunibu ta kwana biyu.AShugaba Tinubu zai tafi kasashen Afirka ta Kudu da Angola ...
18/11/2025

Yan Nijeriya zasu yi kewar shugaba Bola Tunibu ta kwana biyu.
A
Shugaba Tinubu zai tafi kasashen Afirka ta Kudu da Angola a gobe Laraba domin halartar taron G20 tsakanin kasashen kungiyoyin Afirka da tarayyar turai

Wane Ci gaba kuke fatar ganin an samo wa Nijeriya?

Gwamna Yusuf zai gabatar da kasafin kuɗi na Naira Tiriliyan 1, irinsa na farko a tarihin KanoGwamnan Jihar Kano, Alhaji ...
15/11/2025

Gwamna Yusuf zai gabatar da kasafin kuɗi na Naira Tiriliyan 1, irinsa na farko a tarihin Kano

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya ce gwamnatin sa na shirin gabatar da kundin kasafin kuɗi na shekarar 2026, wanda ya kai naira tiriliyan 1 wanda shi ne mafi girma a tarihin jihar da ma yankin Arewa baki ɗaya.

A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Juma’a, gwamnan ya bayyana hakan yayin bude taro na musamman na majalisar zartarwa domin tattauna kasafin kafin mikawa majalisar dokoki a mako mai zuwa.

Yusuf ya ce girman kasafin ya samo asali ne daga karuwar kudaden Harajin cikin gida (IGR) da rufe guraben ɓarnar kuɗi, yana mai bada tabbacin cewa hakan zai baiwa gwamnati damar gudanar da manyan ayyukan raya kasa a 2026.

Kasafin 2026 zai mai da hankali kan gine-gine da noma da ilimi da kiwon lafiya, da tallafawa kananan masana’antu, domin kara farfado da tattalin arziki da inganta rayuwar al’umma.

An bayyana cewa da zarar an kammala, za a mika kasafin kuɗin ga Majalisar Dokokin Kano don tantancewa da amincewa.

Gwamna Yusuf ya nanata kudurinsa na gaskiya, rikon amana da inganta ayyuka ga ’yan jihar.

Rundunar Sojin Saman Najeriya, ta yi wa wani sansanin ’yan bindiga a Jihar Zamfara luguden wuta.Rundunar ta bayyana cewa...
15/11/2025

Rundunar Sojin Saman Najeriya, ta yi wa wani sansanin ’yan bindiga a Jihar Zamfara luguden wuta.

Rundunar ta bayyana cewa ta ɗaiɗaita ’yan bindigar daga wuraren ɓuyansu da ke yankin Tsafe a jihar, yayin wani samame da s**a kai bayan samun bayanan sirri.

Kudin aikin hajjin bana ya koma naira miliyan 7.6 daga jihohin Arewacin Nijeriya
10/11/2025

Kudin aikin hajjin bana ya koma naira miliyan 7.6 daga jihohin Arewacin Nijeriya

Tinubu ya taya Soludo murnar sa ke lashe zaɓen gwamna a AnambraShugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Farfesa Chukwuma ...
09/11/2025

Tinubu ya taya Soludo murnar sa ke lashe zaɓen gwamna a Anambra

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Farfesa Chukwuma Charles Soludo murnar sake lashe zaben gwamnan Jihar Anambra, yana mai cewa nasarar ta nuna irin jagorancinsa mai hangen nesa.

A wata sanarwa daga fadar shugaban kasa, Tinubu ya yaba wa jama’ar Anambra da hukumar INEC, da jami’an tsaro bisa gudanar da zaben cikin lumana da gaskiya.

Ya ce sake zaben Soludo hujja ce ta cewa yana tafiyar da mulki cikin gaskiya, kwarewa da adalci, tare da amfani da ilimi wajen inganta rayuwar al’umma.

Tinubu ya bayyana cewa ayyukan raya kasa da ya kaddamar a lokacin ziyararsa zuwa Anambra sun tabbatar da irin cigaban da gwamnatin Soludo ta kawo.

Ya kuma shawarci Soludo da ya hada kai da abokan adawa don ci gaban jihar, tare da tabbatar masa da goyon bayan gwamnatin tarayya.

Shugaban kasa ya yaba wa shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan, bisa gudanar da sahihin zabe, yana mai bukatar hukumar ta ci gaba da inganta tsarin zabe a kasar.

DA ƊUMI-ƊUMI : An ga ɗalibin Jami’ar Bayero da ya ɓata a Kano shekaru 4 da s**a gabataAn ga wani dalibi na Jami’ar Bayer...
09/11/2025

DA ƊUMI-ƊUMI : An ga ɗalibin Jami’ar Bayero da ya ɓata a Kano shekaru 4 da s**a gabata

An ga wani dalibi na Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK), mai suna Shafiu Auwal Ibrahim, bayan shekaru hudu da bacewars a.

Shafiu, wanda mazaunin unguwar Janbulo ne a Kano, ya ɓata tun a 2021, lamarin da ya tayar da hankalin iyaye, ƴan uwa da abokansa da su ka shafe lokaci suna nemansa ba tare da nasarar ganinsa ba.

Daya daga cikin ‘yan uwansa ya tabbatar da hakan ga wakilin Daily Nigerian Hausa cewa an gano dalibin a jihar Kaduna.

A cewar dan uwan ɗalibin, an same shi ne a wani kauye tare da wani malami.

"An ganshi a wani kauye a Kaduna tare da wani malami wanda ya ce ya dade da tsintar sa. Malamin ya bayyana cewa lokacin da ya same shi kamar ba ya cikin hayyacinsa,” in ji dan uwansa.

Iyalansa sun bayyana farin cikinsu bayan dogon lokaci suna cikin rudani da damuwa, tare da tabbatar da cewa yanzu yana tare da su cikin koshin lafiya da natsuwa.

Zaɓen gwamnan Anambra: Ƴar takara a jam'iyyar AAC ta fitar da zafafan hotunan yaƙin neman zabe ‘Yar takarar jam’iyyar Af...
29/10/2025

Zaɓen gwamnan Anambra: Ƴar takara a jam'iyyar AAC ta fitar da zafafan hotunan yaƙin neman zabe

‘Yar takarar jam’iyyar African Action Congress (AAC) a zaben gwamnan Jihar Anambra da za a gudanar a ranar 8 ga Nuwamba, Chioma Grace Ifemeludike, ta haddasa cece-kuce a kafafen sada zumunta bayan ta fitar da jerin hotuna da bidiyoyin kamfen domin kalubalantar mamayar n maza a tsarin tafikar da mulki.

A wani sako da ta wallafa a shafinta na X a ranar Talata, Ifemeludike ta bayyana kanta a matsayin ‘yar takara mafi cancanta a zaben da ke tafe, inda ta rubuta cewa:

"Ni ce mai rike da tuta ta jam’iyyar African Action Congress, kuma ina alfahari in ce ni ce mafi cancanta a zaben gwamnan Anambra na 8 ga Nuwamba. Haske na tafiya zai fara haskawa. .”

Sojojin Nijeriya za su murƙushe ‘yan ta’addan Lakurawa — Babban hafsan sojin kasa Janar Waidi Shaibu
29/10/2025

Sojojin Nijeriya za su murƙushe ‘yan ta’addan Lakurawa — Babban hafsan sojin kasa Janar Waidi Shaibu

YANZU-YANZU: Majalisar Wakilai ta amince da bukatar Tinubu na ciyo bashin dala biliyan 2.35 Majalisar Wakilai ta amince ...
29/10/2025

YANZU-YANZU: Majalisar Wakilai ta amince da bukatar Tinubu na ciyo bashin dala biliyan 2.35

Majalisar Wakilai ta amince da bukatar Shugaba Bola Tinubu na neman rancen dala biliyan 2.35 domin cike gibi a kasafin kudin shekarar 2025.

A zaman ta na ranar Laraba, majalisar ta kuma amince da shirin shugaban kasa na fitar da takardar bashi ta farko ta sovereign sukuk mai darajar dala miliyan 500 a kasuwar hada-hadar kudi ta duniya, domin samar da kudade don ayyukan gina manyan ababen more rayuwa da kuma fadada hanyoyin samun kudaden gwamnati.

Amincewar ta biyo bayan karɓar rahoton da Kwamitin Majalisar kan Tallafi da Rance da Gudanar da Bashin Kasa ya gabatar, wanda ya bada shawarar aiwatar da wannan shirin a matsayin wani ɓangare na dabarun kudi na gwamnatin tarayya na shekarar 2025.

Da Dumi-DumiTinubu ya cire masu manyan laifuka daga jerin wadanda za su amfana da afuwar shugaban kasa
29/10/2025

Da Dumi-Dumi

Tinubu ya cire masu manyan laifuka daga jerin wadanda za su amfana da afuwar shugaban kasa

Gwamnan Taraba na shirin komawa APC,  Inji hadimin saMai ba da shawara na musamman ga Gwamnan Jihar Taraba kan harkokin ...
29/10/2025

Gwamnan Taraba na shirin komawa APC, Inji hadimin sa

Mai ba da shawara na musamman ga Gwamnan Jihar Taraba kan harkokin siyasa, Josiah Kente, ya bayyana cewa yiwuwar Gwamna Agbu Kefas ya koma jam’iyyar APC wata dabara ce da za ta taimaka wajen samun karin c'i gaban jihar.

A wata sanarwa da ya fitar a Jalingo, Kente ya ce matakin zai baiwa Taraba damar samun karin ayyukan tarayya da hadin gwiwa a fannin tsaro da ci gaban tattalin arziki.

Ya bayyana cewa sauyin ba na son kai ba ne, amma domin muradin ‘yan Taraba na samun ci gaba mai ɗorewa.

Kente ya jaddada cewa Gwamna Kefas ya nuna jajircewa da jagoranci tun bayan hawansa mulki, kuma haɗin kai da gwamnatin tarayya zai kara karfafa shirin sa na ci gaban jihar.

Idan Kefas ya sauya sheka zuwa APC, hakan zai kawo ƙarshen mulkin jam’iyyar PDP a Taraba bayan sama da shekaru 26 da take rike da mulki tun 1999.

Address

Kofar Kaura Opp Magama Restaurant

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Gaskiya Da Gaskiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share