Katsina Network News

Katsina Network News An bude wannan shafi na Katsina Network News a ranar 24 ga watan Yuli 2020 domin wallafa Labarai da Video a cikin Halshen Hausa

Sojoji sun dakile yunkurin ‘yan bindiga na shiga yankunan Shanono a KanoSojojin rundunar haɗin gwiwa (JTF) sun yi nasara...
02/01/2026

Sojoji sun dakile yunkurin ‘yan bindiga na shiga yankunan Shanono a Kano

Sojojin rundunar haɗin gwiwa (JTF) sun yi nasarar dakile yunkurin ‘yanbindiga na kutsawa wasu yankuna a karamar hukumar Shanono ta jihar Kano bayan musayar wuta mai tsawo.

Lamarin, wanda ya fara da tsakar daren Alhamis har zuwa safiyar Juma’a, ya auku ne a Yankwada, Babanduhu da wasu ƙauyuka makwabta a yankin.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin ga kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN), kakakin rundunar Sojin Najeriya a Kano, Manjo Zubair Babatunde, ya ce ‘yanbindigar sun yi ƙoƙarin shiga yankunan ne a kan babura suna harbe-harbe.

Babatunde ya ce harin ramuwar gayya ne bayan da wasu daga cikin ‘yan bindigar s**a rasa rayukansu sakamakon bude wutar da sojoji s**a yi musua wata arangama da aka yi makon da ya gabata.

A cewarsa, maharan sun kutsa ƙauyukan da abin ya shafa da misalin ƙarfe 1:00 na dare, lamarin da ya sa sojoji s**a gaggauta mayar da martani.

“An yi artabu da ‘yan bindigar yadda ya kamata kuma sojoji sun kore su,” in ji shi.

Babatunde ya ƙara da cewa saurin shigar JTF ya hana asarar rayuka da dukiya a yankunan da abin ya shafa.

Ya tabbatar wa mazauna yankin cewa sojoji za su ci gaba da kare rayuka da dukiyoyi, tare da roƙon su su ci gaba da ba jami’an tsaro haɗin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai a kan lokaci.

Kakakin rundunar ya ce sojoji na ci gaba da kasancewa cikin shirin ko-ta-kwana domin hana duk wani sabon hari da kuma tabbatar da zaman lafiya a faɗin jihar.

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa a jamʼiyyar LP, Peter Obi ya sanar da sauya sheƙa zuwa jamʼiyyar ADC.Yayin wani taro da...
31/12/2025

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa a jamʼiyyar LP, Peter Obi ya sanar da sauya sheƙa zuwa jamʼiyyar ADC.

Yayin wani taro da magoya bayansa a Enugu, Obi ya ce za su yi "duk mai yiwuwa don daƙile maguɗi da murɗiyar zaɓe a 2027."

Zargin Badakalar kuɗaɗe: EFCC ta gurfanar da Malami da dansa gaban kotuHukumar EFCC ta gurfanar da tsohon ministan shari...
30/12/2025

Zargin Badakalar kuɗaɗe: EFCC ta gurfanar da Malami da dansa gaban kotu

Hukumar EFCC ta gurfanar da tsohon ministan shari’a Abubakar Malami, tare da ɗansa Abubakar Abdulaziz Malami da wani abokinsa, Bashir Asabe, a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja kan tuhume-tuhume 16 na badakalar kuɗi.

EFCC ta ce tsakanin 2018 zuwa 2025, waɗanda ake tuhuma sun ɓoye da sarrafa biliyoyin naira ta hanyar asusun banki da sayen kadarori a Abuja, ciki har da gidaje a Maitama, Jabi da Garki.

An bayyana cewa kuɗaɗen sun haɗa da fiye da N1bn da aka rika biya ta kamfanoni da asusun banki daban-daban.

Dukkan waɗanda ake tuhuma sun ƙi amsa laifin, kuma Mai Shari’a Emeka Nwite ya ɗage sauraron shari’ar.

Gwamnatin tarayya ta kuma bayyana cewa ta gano kadarori 41 da darajarsu ta kai Naira biliyan 212 da ake zargin suna da alaƙa da Malami.

Bam ya tashi a babban asibitin KebbiRundunar ‘yansanda a jihar Kebbi ta tabbatar da afkuwar fashewar bam da sanyin safiy...
30/12/2025

Bam ya tashi a babban asibitin Kebbi

Rundunar ‘yansanda a jihar Kebbi ta tabbatar da afkuwar fashewar bam da sanyin safiyar Talata a babban asibitin Bagudo, da ke karamar hukumar Bagudo ta jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Bashir Usman, ya fitar a Birnin Kebbi.

Usman ya ce: “Muna son tabbatar wa mazauna yankin cewa an shawo kan al’amuran tsaro gaba ɗaya bayan wata babbar kara ta fashewa da ta auku a babban asibitin Bagudo da sanyin safiyar Talata, 30 ga Disamba.

“Ƙungiyar tsaro ta haɗin gwiwa wadda ta ƙunshi ‘yansanda, sojoji da ‘yan sa-kai ta kulle tare da tabbatar da tsaron yankin cikin gaggawa. Ƙwararrun jami’an EOD-CBRN suna wurin suna gudanar da cikakken bincike.

“Muna farin cikin sanar da cewa babu wanda ya rasa ransa. Duk da cewa wani gini a bangaren ma’aikata ya lalace, mazauna wajen sun riga sun fice lafiya.

“Kwamishinan ‘yansanda na jihar ya ƙara tura jami’an tsaro na musamman domin tabbatar da zaman lafiya da doka.”

Jam'iyyar NNPP a Najeriya ta kori shugaban jam'iyyar na jihar Kano Hashimu Dungurawa daga jam'iyyar.Wannan na zuwa ne ba...
30/12/2025

Jam'iyyar NNPP a Najeriya ta kori shugaban jam'iyyar na jihar Kano Hashimu Dungurawa daga jam'iyyar.

Wannan na zuwa ne bayan kiraye-kirayen da ƴaƴan jam'iyyar ke yiwa Gwamnan Jihar Abba Kabir Yusuf da ya fice daga jam'iyyar ya koma APC.

NNPP ta yi amannar cewa sakaci da kuma rashin ƙwarewar Dungurawa ne ya janyo wannan fitintunu.

Rundunar ƴansanda a jihar Zamfara ta ce ta daƙile wani yunkurin ƴanbindiga na kai hari a karamar hukumar Maru a safiyar ...
28/12/2025

Rundunar ƴansanda a jihar Zamfara ta ce ta daƙile wani yunkurin ƴanbindiga na kai hari a karamar hukumar Maru a safiyar yau Lahadi.

Da Dumi-Dumi Shugaban Nijeriya Bola Tinubu zai yi balaguro zuwa Turai
28/12/2025

Da Dumi-Dumi

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu zai yi balaguro zuwa Turai

Sojoji sun dakile harin ‘yan ta’adda tare da kashe kasurgumin dan bindiga a PlateauSojojin Runduna ta 3 da kuma Joint Ta...
26/12/2025

Sojoji sun dakile harin ‘yan ta’adda tare da kashe kasurgumin dan bindiga a Plateau

Sojojin Runduna ta 3 da kuma Joint Task Force Operation Enduring Peace (JTF OPEP) sun dakile wani shirin hari da ‘yan fashi dauke da makamai s**a yi niyyar kaiwa a Jihar Plateau.

Sojojin sun kuma kashe wani fitaccen shugaban ‘yan ta’adda tare da kwato makamai a yayin aikin.

Bisa sahihin bayanan sirri da aka samu da sanyin safiyar ranar 25 ga Disamba, sojojin sun kaddamar da farmaki a unguwar Gwande da ke Monguna District, karamar hukumar Bokkos.

A wata sanarwa, jami’in yada labarai na aikin, Samson Zhakom, ya ce an tare ‘yan fashin ne yayin da suke shirin kai hari wani gari makwabta, inda aka yi artabu da su.

Ya ce sojojin sun kwato bindiga kirar revolver da aka kera da hannu, bindiga karama (pistol) da aka kera da hannu, harsasai guda tara na 7.62mm, da kuma harsashi (cartridges) guda shida a wurin.

Zhakom ya kara da cewa binciken farko ya tabbatar da cewa dan fashin da aka kashe mamba ne na wata kungiya mai hatsari da ke addabar Gwande da yankunan da ke kewaye.

Bayan wannan artabu, sojojin sun kara kaimi wajen bin sawun sauran ‘yan kungiyar da s**a tsere.

Rundunar sojin ta tabbatar wa mazauna Jihar Plateau da kudurinta na tabbatar da zaman lafiya da tsaro, tare da rokon jama’a su ci gaba da bayar da sahihan bayanan sirri cikin lokaci.

Daily Nigeria Hausa

Yadda Aka Kebe Wurin Da Amurka Ta Kawo Harì A Jihar Sokoto
26/12/2025

Yadda Aka Kebe Wurin Da Amurka Ta Kawo Harì A Jihar Sokoto

Ana fargabar mutane da dama sun rasu yayin da dan kunar bakin wake ya tada bom a Masallaci a MaiduguriAn rawaito cewa da...
24/12/2025

Ana fargabar mutane da dama sun rasu yayin da dan kunar bakin wake ya tada bom a Masallaci a Maiduguri

An rawaito cewa daruruwan masu ibada sun rasa rayukansu bayan wani ɗan kunar bakin wake ya tayar da bam a masallacin Juma’a na Gambarou da ke Maiduguri, babban birnin jihar Borno.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa wasu daga cikin masu ibadar da s**a tsira daga harin sun ce maharan sun shiga masallacin a ɓoye, sannan s**a tayar da bam ɗin ne a lokacin sallar Magariba tare da jama’a.

“Ɗan kunar bakin waken ya tayar da bam ɗin ne a raka’a ta farko ta sallar Magariba. Mutane da dama sun mutu, wasu kuma sun jikkata da raunuka iri-iri,” in ji wani da ya tsira.

Sai dai ba a samu wanda ya ɗauki alhakin harin nan take ba, amma ana zargin ƙungiyar Boko Haram da aikatawa, kasancewar ta ƙaddamar da hare-haren kunar bakin wake da dama a yankin cikin ‘yan watannin da s**a gabata.

An Karrama Shugaban Masu Rinjaye (House Leader) na Majalisar Dokokin Jihar Katsina, Hon. Shamsuddeen Abubakar Dabai da l...
24/12/2025

An Karrama Shugaban Masu Rinjaye (House Leader) na Majalisar Dokokin Jihar Katsina, Hon. Shamsuddeen Abubakar Dabai da lambar yabo bisa gudunmuwar da yake baiwa harkar Ilimi.

A ranar Laraba 24/12/2025, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, CON, ya gabatar da lambar yabo.

Lambar yabon an bayar da ita bisa gagarumar gudummawa da Ɗan majalisar yake bayar wa wajen bunƙasa harkar ilimi ta hanyar bayar da tallafin karatu (scholarship) ga matasa.

An gabatar da lambar yabon ne a madadin Hukumar kula da bayar da Tallafin Karatu ta Jihar Katsina, inda Shugaban Ƙaramar Hukumar Danja, Hon. Rabo Tambaya, ya karɓi lambar yabon a madadin Hon. House Leader.

An yi jana'izar dan majalisar jihar Kano, Hon. Aminu Sa'adu Ungoggo a yammacin yau.Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...
24/12/2025

An yi jana'izar dan majalisar jihar Kano, Hon. Aminu Sa'adu Ungoggo a yammacin yau.

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf da Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso da shugaban majalisar dokokin Kano na daga cikin waɗanda s**a halarci jana'izar.

Dan majalisar ya rasu ne a dazu bayan gajeriyar rashin lafiya da ta same shi yana tsaka da aiki a majalisar.

Address

Kofar Kaura
Katsina

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina Network News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share