23/02/2026
Da Dumi-Dumi: Hukumar ICPC ta ki bayar da belin El-rufai kwanaki takwas bayan tsare shi - Hadiminsa
A wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Muyiwa Adekeye, ya fitar, ya ce El-Rufai ya miƙa kansa ne ga EFCC ranar 16 ga Fabrairu, 2026, bisa gayyata, kafin daga bisani a miƙa shi hannun ICPC a daren 18 ga Fabrairu.
Lauyoyinsa sun ce sun nemi beli tun 19 ga Fabrairu amma har yanzu ba su samu amsa ba, inda suke zargin cewa an tsare shi fiye da sa’o’i 48 da doka ta tanada ba tare da gurfanar da shi a kotu ba.
Rahoton jaridar Daily Trust ya ambato an kuma shirya sauraron ƙarar kare haƙƙinsa a babbar kotun babban birnin tarayya ranar 25 ga Fabrairu, inda yake neman a bayar da belinsa.
Haka zalika, ana sa ran gurfanar da shi a wannan rana kan tuhume-tuhumen da DSS ta shigar a kansa.
Me za ku ce?
Copied