Katsina Network News

Katsina Network News An bude wannan shafi na Katsina Network News a ranar 24 ga watan Yuli 2020 domin wallafa Labarai da Video a cikin Halshen Hausa

Da Dumi-Dumi: Hukumar ICPC ta ki bayar da belin El-rufai kwanaki takwas bayan tsare shi - HadiminsaA wata sanarwa da mai...
23/02/2026

Da Dumi-Dumi: Hukumar ICPC ta ki bayar da belin El-rufai kwanaki takwas bayan tsare shi - Hadiminsa

A wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Muyiwa Adekeye, ya fitar, ya ce El-Rufai ya miƙa kansa ne ga EFCC ranar 16 ga Fabrairu, 2026, bisa gayyata, kafin daga bisani a miƙa shi hannun ICPC a daren 18 ga Fabrairu.

Lauyoyinsa sun ce sun nemi beli tun 19 ga Fabrairu amma har yanzu ba su samu amsa ba, inda suke zargin cewa an tsare shi fiye da sa’o’i 48 da doka ta tanada ba tare da gurfanar da shi a kotu ba.

Rahoton jaridar Daily Trust ya ambato an kuma shirya sauraron ƙarar kare haƙƙinsa a babbar kotun babban birnin tarayya ranar 25 ga Fabrairu, inda yake neman a bayar da belinsa.

Haka zalika, ana sa ran gurfanar da shi a wannan rana kan tuhume-tuhumen da DSS ta shigar a kansa.

Me za ku ce?

Copied

Yadda aka gabatar da Sallar Jumu'ah ta farko a Ramadan 1447/2026 a Masallacin Haramin Makkah Me alfarma.📸 Haramain
20/02/2026

Yadda aka gabatar da Sallar Jumu'ah ta farko a Ramadan 1447/2026 a Masallacin Haramin Makkah Me alfarma.

📸 Haramain

Kalli sabon gidan sarauta da gwamnatin Zamfara ta gina wa Sarkin Anka Hoto: FB/Bahsan Online Tv
17/02/2026

Kalli sabon gidan sarauta da gwamnatin Zamfara ta gina wa Sarkin Anka
Hoto: FB/Bahsan Online Tv

A cewar hukumomin Saudiyya, za a tashi da azumin Ramadana na shekarar Musulunci ta 1447 a kasar a gobe Laraba 18 ga wata...
17/02/2026

A cewar hukumomin Saudiyya, za a tashi da azumin Ramadana na shekarar Musulunci ta 1447 a kasar a gobe Laraba 18 ga watan Fabrairu, 2026.

Bbchausa

17/02/2026

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal ya ce ba zai zama butulu ba, ya sauya sheka zuwa wata jam'iyya don PDP na da matsala.

Kalli yadda gobara ta yi ɓarna a Gidan Gilas da ke kasuwar Singa a jihar Kano.📸: Sani Ibrahim P**i
14/02/2026

Kalli yadda gobara ta yi ɓarna a Gidan Gilas da ke kasuwar Singa a jihar Kano.

📸: Sani Ibrahim P**i

APC ta yi Alla-Wadai da lalata allunan tallan Tinubu a Zamfara Jam’iyyar APC ta Jihar Zamfara ta yi Allah-wadai da lalat...
14/02/2026

APC ta yi Alla-Wadai da lalata allunan tallan Tinubu a Zamfara

Jam’iyyar APC ta Jihar Zamfara ta yi Allah-wadai da lalata allunan tallan hotunan Shugaba Bola Tinubu a Gusau, tana mai cewa “ya isa haka”.

Sakataren yaɗa labarai na APC a Zamfara, Malam Yusuf Idris, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a Gusau ranar Juma’a.

Idris ya ce irin waɗannan ayyuka na iya haifar da tashin hankali na siyasa a jihar.

A cewarsa, jam’iyyar ta lura da cirewa da lalata dukkan allunan talla da ke ɗauke da hotunan shugaban ƙasa, Bola Tinubu, a faɗin jihar.

Ya ce, “Wannan ɗabi’a ta rashin tsari ta daɗe tana faruwa, inda aka fara da sauke dukkan allunan tallan APC har sai da jam’iyyar ta kai ƙorafi ga hukumomin tsaro.”

Sai dai ya zargi wasu ‘yan daba da aka ɗauki nauyinsu da yunƙurin haddasa rikici gabanin tarukan zaɓen shugabannin jam’iyya da kuma babban zaɓen shekarar 2027.

Idris ya ƙara da cewa, “A ranar Laraba, wasu ‘yan daba da aka ɗauki nauyi sun yi yunƙurin lalata wani allon tallan shugaban ƙasa wanda kuma ke ɗauke da hotunan Ministan Tsaro na Ƙasa, Dakta Bello Matawalle, da Sanata Abdulaziz Yari, dukkansu tsofaffin gwamnoni kuma jagororin jam’iyyar. An kafa allon ne a gaban gidan Ministan da ke Gusau.

“Da sauri jami’an tsaro da ke gadin gidan s**a shiga tsakani, lamarin da ya hana faruwar ɓarna.

“Jam’iyyar na sake kira ga hukumomin tsaro a jihar da su dakatar da irin wannan ɓarna da rashin mutunci ga shugaban ƙasa", inji sanarwar.

Shugaban Kasar Najeriya Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya kaddamar da bude sabuwar Sakatariyar Ma'aikan jihar Kebbi da Tituna...
14/02/2026

Shugaban Kasar Najeriya Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya kaddamar da bude sabuwar Sakatariyar Ma'aikan jihar Kebbi da Tituna, Tashar Mota, da makarantar unguwar zoma watau School of Nursing.

Wanda Gwamna jihar Kebbi Kwamared Dakta Nasir Idris Kauran Gwandu ya gina, daga bisa ni ana saran shugaban kasa tare da ƴan tawagar shi zasu isa Argungu domin halartar bikin kamun kifi da ake yi.

Yadda aka gudanar da gasar ninƙaya ta maza da mata a wurin bikin gasar Argungu Fishing Festival rana ta uku. 📸Kaltungo C...
13/02/2026

Yadda aka gudanar da gasar ninƙaya ta maza da mata a wurin bikin gasar Argungu Fishing Festival rana ta uku.

📸Kaltungo Chiefdom

Wasu daga cikin hotuna da aka ɗauka wajen taro na nuna goyan baya ga Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Radda PhD CON da ...
02/02/2026

Wasu daga cikin hotuna da aka ɗauka wajen taro na nuna goyan baya ga Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Radda PhD CON da shugaban Ƙasar Nijeriya Sanata Bola Ahmad Tinubu.

Taron ya guda a ranar Litinin 02/02/2026, a babban filin wasa na Muhammad Dikko dake cikin birnin Katsina.

📷 Mobile Media Crew

Shigar Abba APC: Yanzu zan yi bacci da ido biyu - BarauMataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...
27/01/2026

Shigar Abba APC: Yanzu zan yi bacci da ido biyu - Barau

Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu ya umarci shugabannin jam’iyyar APC a Jihar Kano da su bai wa Gwamna Abba Kabir Yusuf cikakken goyon baya tun gabanin sauya shekarsa zuwa jam’iyyar.

Sanata Barau ya ce Shugaban ƙasar ya jaddada muhimmancin haɗin kai da haɗin gwiwa domin samun ingantaccen shugabanci a jihar.

Barau ya bayyana hakan ne yayin da yake zantawa da ‘yan jarida a Kano, a ranar Talata.

Ya ce Shugaba Tinubu, wanda ya bayyana a matsayin gogaggen shugaba a harkar siyasa, ya shawarci masu ruwa da tsaki a jam’iyyar da su yi aiki kafada da kafada da gwamnan, tare da gujewa duk wani aiki da zai iya karkatar da hankalinsa daga samar da nagartaccen shugabanci ga al’ummar Jihar Kano.

“Yau rana ce da zan kwanta cikin natsuwa saboda jam’iyyarmu ta samu gwamna. Fiye da shekara guda, muna karɓar ‘yan sauya sheka daga jam’iyyu daban-daban, ciki har da NNPP. Yanzu, da yardar Allah, mun karɓi gwamna mai ci na jiha kamar Kano,” in ji Barau.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa ya ce yanzu APC a Kano ya kamata ta mai da hankali wajen tallafawa Gwamna Yusuf don ya yi nasara, inda ya lura cewa haɗin kai a cikin jam’iyyar yana da matuƙar muhimmanci don cimma ci gaba.

“Abin da ya fi muhimmanci yanzu shi ne tallafa masa da kuma ba shi shawara, har da addu’a. Halin da ake ciki a Kano na bukatar mu hada kai ta hanyar dimokuradiyya don taimaka masa ya yi nasara,” in ji shi.

Barau ya bayyana cewa, bayan shigar gwamnan cikin APC, duk wani nau’i na fafatawa ta siyasa da burin ƙashin kai a cikin jam’iyyar ya kamata a ajiye a gefe don tabbatar da kwanciyar hankali da ci gaba.

Address

Kofar Kaura
Katsina

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina Network News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share