Dikkofied

Dikkofied Wannan Shafi ne na Masoya mai Girma Gwamna Jahar Katsina Malam Dikko Umar Radda Kuma Muna tallatashi.

This is a page we opened to promote PhD Dr Dikko Umar Radda and the Governor-in-waiting of Katsina State

YANZU-YANZU : Shirye-shiryen ƙaddamar da fara rabon takin zamani a ƙaramar hukumar Kusada, wanda Gwamnan jihar Katsina M...
05/05/2025

YANZU-YANZU : Shirye-shiryen ƙaddamar da fara rabon takin zamani a ƙaramar hukumar Kusada, wanda Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD,CON, ya samar ga manoman jihar Katsina, kafin saukar damunar bana.

Gwamna Radda Ya Nuna Jin Dadinsa Da Ziyara mai Ɗumbin Tarihi wacce Shugaban Ƙasa Bola Tinubu Ya kawo jihar Katsina.Gwamn...
04/05/2025

Gwamna Radda Ya Nuna Jin Dadinsa Da Ziyara mai Ɗumbin Tarihi wacce Shugaban Ƙasa Bola Tinubu Ya kawo jihar Katsina.

Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya nuna matukar jin dadinsa ga al’ummar jihar Katsina bisa gagarumin fitowar da s**a nuna a ziyarar aiki ta kwanaki biyu da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya kai jihar.

Gwamnan ya yabawa ‘yan kasar bisa kyakkyawar tarba da nuna kyakykyawan karbuwar da s**a nuna a Katsina, wanda ya taimaka matuka wajen samun nasarar ziyarar shugaban kasar.

A yayin zuwan nasa, shugaba Tinubu ya ƙaddamar da wasu muhimman ayyuka guda biyu na samar da ababen more rayuwa:

- Cibiyar samar da aikin gona ta jihar Katsina da kuma hanya mai tsawon kilomita 24.

Gwamnan ya kuma tabbatar wa al’ummar Katsina cewa sabbin hanyoyin da aka kaddamar tamkar tulun kankara ne, ya kara da cewa Insha Allah watanni masu zuwa za a kaddamar da sabbin ayyukan raya kasa.

Gwamna Radda ya kuma mika godiya ta musamman ga shugaban kasa Tinubu bisa girmama gayyatar da ya yi masa da kuma bikin auren ‘yar sa Aisha Dikko Umaru Radda da Ahmed Usman.

Gwamnan ya bayyana halartar shugaban kasa a wajen bukin a matsayin wani gagarumin fatan alheri da iyalansa za su ci gaba da rikewa har abada.

Muna matukar farin ciki da cewa Shugaba Tinubu ya tsaya a matsayin Waliyi ga diyata a wannan gagarumin biki.

Halartan sa ya kara wa bikin kima da kima da kuma nuna kyakykyawan alaka tsakanin iyalanmu,” inji Gwamnan.

Bugu da kari, Gwamna Radda ya nuna matukar godiya ga takwarorinsa gwamnoni, manyan Sanatoci da ‘yan majalisar wakilai, manyan ministoci, masu rike da mukaman shugaban kasa, shugabannin ‘yan kasuwa, da masu hannu da shuni da s**a yi tattaki daga nesa da kusa domin gudanar da bukukuwan.

Gwamna Radda ya kara da cewa, "Kasancewar ku ya kara dankon zumuncin da ya daure mu a matsayinmu na al'umma da kuma kasa baki daya, hadin kan da shugabanni ke nunawa a tsakanin bangarori daban-daban na siyasa ya nuna irin sadaukarwar da muka yi na ci gaban Najeriya."

Gwamnan ya jaddada aniyar gwamnatin sa na aiwatar da ayyukan da s**a dace da jama’a, wadanda za su inganta rayuwa ga daukacin mazauna jihar Katsina, a bisa manufofinsa na ci gaba.

Shugaban Ƙasa Asiwaju Bola Tinubu, Ya Bayar Da Auren Ɗiyar Gwamna Raɗɗa.Shugaban ƙasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya baya...
03/05/2025

Shugaban Ƙasa Asiwaju Bola Tinubu, Ya Bayar Da Auren Ɗiyar Gwamna Raɗɗa.

Shugaban ƙasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya bayar da auren Aisha Dikko Umaru Raɗɗa, ɗiyar gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda PhD.

Tsohon gwamnan jihar Bauchi Isah Yuguda, ne ya amshi auren ga angon nata Ahmed Usman bisa sadaki Naira 700,000, wanda limamin masallacin juma'a na Usman Bn Affan Modoji Alh. Amadi Batagarawa ya ɗaura kamar yadda addinin musulunci ya tanadar.

Muhimman mutanen da s**a halarci ɗaurin auren akwai Kakakin majalisar wakilai Rt.Hon Tajuddeen Abbas, Mataimakin Shugaban majalissar dattawa Sanata Barau I Maliya, shugaban jam'iyyar APC na ƙasa Abdullahi Umar Ganduje, Gwamnan jihar Kwara kuma shugaban ƙungiyar gwamnoni Abdulrazaq Abdulrahman, na jihar Gombe Inuwa Yahaya, na jihar Borno Babagana Umara Zulum.

Sai Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal, na jihar Sokoto Ahmed Aliyu, na jihar Benue Hyacinth Alia, na jihar Yobe Mai Mala Buni, na jihar Kebbi Nasir Idris, na jihar Neja Muhammad Bago, na jihar Kaduna Uba Sani, na jihar Jigawa Umar Namadi, na jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf.

Sauran sun haɗa da ministan gidaje da raya birane Arc Ahmad Musa Dangiwa, Ministan yaɗa labarai Muhammad Idris Malagi, Ministan zirga-zirga Sa'idu Ahmed Alƙali, tsofaffin gwamnonin jihar Katsina Rt.Hon Aminu Masari, da Barr. Ibrahim Shema, Mataimakin gwamnan jihar Katsina Malam Faruk Joɓe, Mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan harkokin siyasa Ibrahim Kabir Masari, ƴan majalissar dattawa, na tarayya, na dokoki da na zartaswa.

Manyan ƴan kasuwa irin su ; Ɗahiru Mangal, Arthur Eze, Isah Gerawa, shugaban hukumar bunƙasa ƙanana sana'o'i ta ƙasa Charles Odii, sarakunan Katsina da Daura Alh. Abdulmumini Kabir Usman, da Umar Faruk Umar, da sauran su.

Shugaban kasa, Tinubu ya isa Katsina domin ziyarar aiki ta kwanaki 2 A yau ne shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya isa ji...
02/05/2025

Shugaban kasa, Tinubu ya isa Katsina domin ziyarar aiki ta kwanaki 2

A yau ne shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya isa jihar Katsina, inda ya fara ziyarar aiki ta kwanaki biyu tare da liyafar da gwamna Dikko Umaru Radda ya jagoranta.

Nan take shugaban ya Fara duba jami’an tsaro kafin ya yi jawabi ga dakarun sojojin Najeriya da ke yankin.

Wata babbar tawaga ta bi sahun gwamna Radda domin tarbar shugaban kasar, ciki har da gwamnan jihar Borno Babagana Zulum, gwamnan Kaduna Uba Sani, shugaban jam'iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Ganduje, tsohon gwamnan Katsina Ibrahim Shema, tsohon gwamna Aminu Bello Masari.
da kuma ministan noma da samar da abinci, Abubakar Kyari.

Mataimakin Gwamnan Katsina Faruk Lawal Jobe, Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Rt. Hon. Nasir Yahaya Daura, da mai taimakawa shugaban kasa Alhaji Ibrahim Kabir Masari sun kammala babban kwamatin karbar baki.

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD, ya ziyarci cibiyar samar da kayan noma da ya gina tare da saka kayan ...
02/05/2025

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD, ya ziyarci cibiyar samar da kayan noma da ya gina tare da saka kayan aiki na zamani wadda shugaban ƙasa Bola Tinubu, zai ƙaddamar a ziyarar aiki ta kwana 2 da zai kawo jihar Katsina.

📷 -Gwamnatin jihar Katsina.

Gwamna Raɗɗa ya bayyana gobe juma'a 2/05/2025, a matsayin ranar hutu ga ma'aikatan jihar Katsina, domin basu damar tarba...
01/05/2025

Gwamna Raɗɗa ya bayyana gobe juma'a 2/05/2025, a matsayin ranar hutu ga ma'aikatan jihar Katsina, domin basu damar tarbar shugaban ƙasa Asiwaju Bola Tinubu, wanda zai ziyarci jihar domin ƙaddamar da wasu muhimman ayyuka.

Walwala Da Jin Daɗin Ma'aikata Na Da Matuƙar Muhimmanci A Gwamnatin Mu - Saƙon Gwamna Raɗɗa A ranar Ma'aikata Gwamnan ji...
01/05/2025

Walwala Da Jin Daɗin Ma'aikata Na Da Matuƙar Muhimmanci A Gwamnatin Mu - Saƙon Gwamna Raɗɗa A ranar Ma'aikata

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD,CON, ya yaba ma irin gudummuwar da ma'aikatan gwamnati ke badawa wajen cigaban jihar Katsina, hakan na ƙunshe a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan Ibrahim Kaulaha Mohammed ya fitar a daren ranar Laraba 30/05/2025, a saƙon Gwamnan na ranar ma'aikata ta duniya.

A cikin saƙon Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD,CON, ya ce gwamnatin shi zata cigaba da kula da walwala da jin daɗin ma'aikatan jihar, ta hanyar shirye-shirye da dama da zasu samar da hakan.

"Ma'aikatan gwamnati sun kasance ƙashin bayan tafiyar da gwamnati, hakan ya sanya gwamnatin mu ta karkata wajen samar da walwala da jin daɗin ma'aikata, domin ƙara masu ƙwarin guiwa wajen gabatar da ayyukan al'umma" cewar gwamna Raɗɗa.

Sanarwar tace Gwamnan ya kuma sanya duk wani ƙarin matsayi da ya kamata ma'aikata su samu tun daga shekarar 2023, inda ya tabbatar da kowane ma'aikaci ya samu ƙarin matsayi ta hanyar zana jarabawa ba tare da nuna sanayya ko ɓangaranci ba, an kuma sake gabatar da jarabawar ƙarin girman a shekarar 2024 ga ma'aikatan da s**a chanchanta.

"Gwamnatin mu ta biya ma'aikata, tare da ƴan fansho kuɗi Naira Miliyan 957 domin yin hidima a watan Ramadan, haka kuma mun kashe Naira Miliyan 200 domin baiwa ma'aikatan gwamnati bashin da aka riƙa fitarwa a hankali, tare da ƙarin Naira Miliyan 250 da aka fara aiki da su, hakan yasa mun kashe jimillar kuɗin da muka ba ma'aikata bashi Naira Miliyan 450" Injii Gwamna Raɗɗa

Bugu da ƙari kuma Gwamnan yace ma'aikatan gwamnati 14 ne s**a karɓi kyautar girmamawa bayan nuna ƙwazo a wajen ayyukan su, wanda ya haɗa da Motoci, kuɗi kimanin Naira Miliyan biyu ga kowane, duk kuma a yunƙurin gwamnati mu na inganta aikin gwamnati.

A ɓangaren biyan kuɗin ƴan fansho kuma, Gwamnan yace mun amince da fitar da Naira Biliyan 24, domin biyan kuɗin ajiye aiki ga ma'aikatan da s**a ajiye aiki na ƙananan hukumomi da jiha, yunƙurin da ya sanyaya zukatan dubban ƴan fansho da kuma iyalan su cikin farin ciki.

A wani ƙoƙarin kuma gwamnati ta samar da "Rumbun Sauƙi" domin sayar wa ma'aikatan gwamnati abinci a farashi mai rahusa, duk domin kyautata ma ma'aikatan.

Kamar yadda muke murnar zagayowar ranar ma'aikata ta duniya, ina mai kira ga ma'aikatan gwamnati da su dage wajen gudanar da ayyukan su domin ciyar da jihar Katsina gaba, kuma gwamnatin mu zata cigaba da ƙoƙari domin samar da walwala da cigaban ma'aikata, sabo da hakan yana da muhimmanci a gwamnatin mu.

Gwamna Raɗɗa Ya Ƙaddamar Da Manufofin Jihar Katsina Akan Sauyin YanayiGwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD,...
23/04/2025

Gwamna Raɗɗa Ya Ƙaddamar Da Manufofin Jihar Katsina Akan Sauyin Yanayi

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD, ya ƙaddamar da manufofin da za su kai jihar Katsina tudun mun tsira akan abun da ya shafi sauyin yanayi a ranar Laraba 23/04/2025, taron ya wakana a ɗakin taro na masaukin baƙin Transcorp Hilton da ke birnin tarayya Abuja.

An bayyana manufofin ne a lokacin taron ƙaddamar da lalubo hanyoyin da zasu samar da muhalli mai kyau a jihar Katsina wanda aka yi ma suna "Katsina State Green Growth Agenda (KAGGA)" wanda ke da manufar samar da tsirrai da nufin daƙile matsalar sauyin yanayi.

A lokacin da yake jawabin ƙaddamar da shirin Gwamna Raɗɗa ya ce akwai matsalolin sauyin yanayi da dama da ke tunkarar jihar Katsina, inda kaso 80% cikin ɗari na mutanen jihar sun dogara ne da noman damuna kawai, duk da barazanar kwararowar hamada, ƙarancin ruwan damuna, da kuma yanayi mai zafi da jihar ke fama da shi.

" Wan nan sauyin yanayin zai haifar da ƙarancin kayan gona, raguwar halittu, ƙarancin albarkatun ƙasa, tare da haifar da rashin tabbas ga matasan mu wajen hijira domin neman mafaka.

Da yake magana akan yadda za'a magance matsalar sauyin yanayi, Gwamna Raɗɗa yace sun yi shiri wanda zai wadatar da ruwa a jihar Katsina.

" Mun fahimci cewa wadatar da ruwa kamar magance matsalar sauyin yanayi ne, Inji Gwamnan, shiyasa kuma muka samar da hukumar noman rani wadda ta samar da famfunan ban ruwa masu amfani da hasken rana 4,000, tare da rijioyin ban ruwa 204, mun kashe Naira Biliyan ₦10.8 domin gina madatsar ruwa a Dam ɗin Jibia, an kashe Naira Biliyan ₦11.2 domin samar da manyan hanyoyin ruwa a cikin garin Katsina, haka kuma gwamnatin mu ta kashe Naira Biliyan ₦2.4 domin samar da famfuna masu amfani da hasken rana 120, tare da wasu guda 60 da ake tsaka da ginawa.

Haka kuma Gwamnan ya bayyana irin ƙoƙarin da ya yi a fannin noma inda yace ya samar da taraktoci 38, tare da samar da taraktocin na hannu 320, wanda kuɗin su ya kai Naira Biliyan Uku, tare da samar da hektocin noma 1,115, kuma gwamnati ta yi yarjejeniya da kamfanin Genesis ta Miliyan $500 domin samar da lantarki mai amfani da hasken rana a gidan Gwamnati da Babban asibitin Katsina.

Sannan kuma an koyar da mata da matasa sama da 5000, dabarun noman zamani mai suna "Waste-to-wealth".

Babban muhimmancin ƙaddamar da wannan shiri na manufofin jihar Katsina akan sauyin yanayi (KAGGA), shine domin samo hanyar da zata bunƙasa da kare rayuwar halittun dabbobi da tsirrai.

Wannan shirin manufofin kuma yana da ginshiƙai guda huɗu da s**a haɗa da samar da tsarin noma na zamani, shugabanci a ɓangaren samar da makamashi na zamani, dawo da martabar tsarin muhalli, da kuma wadatar da tsirrai ko dashen Itatuwa.

Domin samun nasarar aiwatar da wannan shiri, Gwamna Raɗɗa yace za'ayi doka akan manufofin sauyin yanayin cikin watanni 12, tare da ware kaso 30% na kasafin kuɗin jihar akan kawo ƙarshen matsalar sauyin yanayi, haka kuma za'a samar da asusun kuɗin kula da sauyin yanayi wanda yanzu haka an saka mashi Naira Biliyan ₦5.

Gwamna Raɗɗa ya kuma yi amfani da damar wajen gayyato masu saka hannun jari domin kawo masu saka makamashi na zamani masu amfani da hasken rana domin inganta noma da rainon tsirrai a jihar Katsina.

"A cikin shirin sauyin yanayida za'a kawo, gwamnati zata riƙa horar da mata da matasa 15,000 duk shekara, akan bunƙasa tsirrai, kuma arzikin da za'a samu wajen zai samar da aikin yi ga sama da mutane 50,000 a jihar Katsina zuwa shekarar 2030. Inji Gwamna Raɗɗa

Tun da fari a jawabin shi na maraba Kwamishinan Muhalli na jihar Katsina Hon. Hamza Sulaiman Faskari, ya bayyana cewa taron na da nufin lalubo hanyoyin da zasu kawo chanji akan matsalar sauyin yanayi, tare da bayyana irin yadda za'a bunƙasa rayuwar tsirrai da dabbobi a jihar Katsina.

Shima a nashi jawabin Ministan Muhalli Hon. Balarabe Abbas Lawal, ya yaba ma gwamnatin jihar Katsina, akan kawo wannan shirin na (KAGGA) tare da samar da majalissar kula da sauyin yanayi ta jiha, wanda ya bayyana hakan zasu taimaka ma jihar wajen magance matsalar sauyin yanayi.

A nashi ɓangaren Ministan gidaje da raya birane Arc Ahmad Musa Dangiwa, ya bayyana cewa ma'aikatar shi tana yin tsare-tsaren gini wanda zasu taimaka wajen kauce ma matsalar sauyin yanayi.

Kakakin majalissar wakillai Rt.Hon Tajuddeen Abbas, ya yaba ma ƙoƙarin gwamnatin jihar Katsina wajen magance matsalar sauyin yanayi musamman ƙoƙarin ta wajen kawo sauyi domin amfani da makamashi na zamani.

Hon. Sada Soli Jibia, a madadin ƴan majalissar tarayya 15 na jihar Katsina, yace a shirye suke domin goya ma gwamnatin Jihar Katsina baya wajen cimma ƙudurin ta na yaƙi da sauyin yanayi.

Sauran wanda s**a yi magana a wurin akwai Ministan al'adu Hannatu Musawa, wakilin tarayyar turai a Najeriya Mista Beatrice Eyong, Mataimakin sakataren majalisar ɗinkin duniya Mohammed M. Malick Fall, Jakadan ƙasar Misrah a Najeriya Mohammed Foud, da sauran su..

Malam Dikko Umaru Radda PhD
22/04/2025

Malam Dikko Umaru Radda PhD

Malam Dikko Radda, Ya Sanya Albarka Ga Makarantar Sakandiren Waƙafi Da Alh. Sani Zangon Daura Ya Samar A Garin Zango, Ta...
19/04/2025

Malam Dikko Radda, Ya Sanya Albarka Ga Makarantar Sakandiren Waƙafi Da Alh. Sani Zangon Daura Ya Samar A Garin Zango, Tare Da Alƙawarin Duba Ƙorafin Makarantar

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD,CON, ya ziyarci makarantar Sakandiren mata ta waƙafi da Alh. Sani Zangon Daura, ya samar a garin Zangon Daura, domin cigaban ilimi da kuma tallafawa marayu da masu ƙaramin ƙarfi.

Da yake gabatar da jawabi akan yadda makarantar zata kasance Injiniya Abba Mato wanda shine ke kula da ita, ya bayyana ma Gwamna Raɗɗa cewa Alh. Nasiru Sani Zangon Daura, ya assasa wannan makarantar ne domin taimakawa masu ƙaramin ƙarfi da marayu, kuma ɗaliban makarantar zasu riƙa karatu ne a kyauta ba tare da biyan ko kobo ba.

Ya ƙara da cewa Dan masanin Daura ya kashe sama da Naira Biliyan ɗaya wajen gina makarantar kuma ya ware wani kaso na dukiyar shi wanda za'a riƙa gudanar da ayyukan makarantar wanda ya fitar da shi daga cikin lissafin gadon shi ko da bayan ran shi.

Ya kuma roƙi gwamna Raɗɗa da shima ya saka tashi gudummuwar a cikin makarantar wajen samar da hanyar da za ta kawo mutum cikin makarantar da kuma hanyoyin ruwa wanda sune s**a rage a cikin aikin.

Da yake magana Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda,PhD,CON, ya jinjinawa ƙoƙarin Alh. Sani Zangon Daura wajen assasa makarantar, ya kuma ce samar da makarantar bai zama abun mamaki ba duba da kasancewar shi cikin muhimman mutanen da ake alfahari da su a jihar Katsina da ma ƙasa baki ɗaya.

Ya ƙara da cewa wannan wani aiki ne da zai taimaki gwamnati, sabo da yana ɗaya daga cikin abun da ya rataya kan ta, kuma samar da makarantar zai taimaka wajen inganta ilimin ƴaƴa mata a jihar Katsina.

A ɓangaren tallafin gina hanya da magudanan ruwa kuma, yace zai duba yaga abun da zai yiwu domin bayar da shima tashi gudummuwar.

Gwamna Mal Dikko Radda ya bayar da kwangilar aikin gina t**i mai tagwayen hannu da ya taso daga t**in Jabiri zuwa shatal...
13/11/2024

Gwamna Mal Dikko Radda ya bayar da kwangilar aikin gina t**i mai tagwayen hannu da ya taso daga t**in Jabiri zuwa shataletalen babban masallaci zuwa General Hospital a garin Funtua.

Address

Sabuwar Unguwa
Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dikkofied posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share