Katsina City News

Katsina City News Katsina City News is published by Matasa Media Links Nig Ltd, publishers of The Links News, Jaridar Taskar Labarai and Matasa motivational magazine.

Katsina City News is managed by professional journalists from Katsina state.

16/02/2023

Salam, Innalillahi wa ina ilaihirraji un.Allah yayi ma mahaifiyar Alhaji suleman Kuki( ES katsina state pilgrims welfare board) Rasuwa.za a yi Jana izarta da karfe uku na Rana a unguwar gidajen Goriba dake nan katsina.
Allah ya bada ikon halarta

KAKAKIN MAJALISAR DOKOKIN JAHAR KATSINA YA TSALLAKE RIJIYA DA BAYA ....Saura kiris a tsige shiMu'azu Hassan @ Katsina Ci...
31/01/2023

KAKAKIN MAJALISAR DOKOKIN JAHAR KATSINA YA TSALLAKE RIJIYA DA BAYA

....Saura kiris a tsige shi

Mu'azu Hassan
@ Katsina City News

Jaridun Katsina City News, sun tabbatar da labarin cewa saura kiris da an tsige Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Katsina, Alhaji Musa Tasi'u Maigari.

Majiyarmu ta tabbatar mana da cewa, masu yunkurin sun fara shirinsu ne tun ranar Litinin 23/1/2023. Kuma har sun samu amincewa da sa hannun 'yan Majalisar Jihar 18.

Majiyarmu ta ce ya zuwa ranar Juma'a 28/1/2023, masu yunkurin suna da cikakken goyon bayan mafi yawan 'yan Majalisar da za su tsige Kakakin nasu.

Majiyarmu ta ce wani dan Majalisa daga shiyyar Funtua ne ya jagoranci karya lagon shirin, inda ya k**a daki a wani sabon katafaren otal da ke nan cikin birnin Katsina inda ya yi aikin wargaza shirin.

Daga wannan otal aka samu sa hannun 'yan Majalisa tara wadanda s**a fitar da hannunsu daga shirin.

Babban Editan jaridun Katsina City News ya ga takardu biyu na sa hannun farko na kudurin tsige Kakakin Majalisar da kuma wanda 'yan Majalisa tara s**a sanya wa hannu da ba su yarda da tsigewar ba.

Majiyarmu ta ce wani dan Majalisa daga shiyyar Funtua, kuma na kusa da Kakakin Majalisar shi ne ya jagoranci wannan yunkurin.

Matsalar da ya samu ita ce, ya nemi in yunkurin ya yi nasara shi ya zama Kakakin Majalisar na sauran watannin da s**a rage.

Wani dan Majalisa daga shiyyar Daura ya tabbatar wa da jaridunmu cewa, daya daga cikin dalilan da s**a sanya shirin ya kasa nasara shi ne, kudirin dauke kujerar Kakakin Majalisar daga shiyyar Daura ta koma shiyyar Funtua na sauran watannin da s**a rage.

Masu yunkurin sun zargi Kakakin Majalisar da son kansa da kin taimakon su lokacin zaben fitar da gwanin 'yan takarar da aka yi.

Da kuma cewa maganar kudi shi kadai yake amfana, yayin da su kuma ya bar su cikin wahala har gwamnatin ta zo karshe.

Wata majiya ta ce hatta Gwamnan Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari CFR sai da ya sa baki wajen ceto kujerar Kakakin Majalisar.

Zaman jiya 30/1/2023 aka so a tabbatar da juyin mulkin, amma bai yi nasara ba.

Duk da majiyarmu tamu ta ce ya zuwa yanzu komai ya daidaita a Majalisar, amma daya daga cikin masu shirin ya ce sun sa ido idan Kakakin ya canza, to magana ta wuce, amma idan ya ki canzawa za su canza salo.

08/12/2022
'YAN TA' ADDA, YARAN  ALERU  SUN NUFO KATSINA? City News Majiyoyi masu karfin gaske dake da alaka jami'an tsaro masu san...
13/09/2022

'YAN TA' ADDA, YARAN ALERU SUN NUFO KATSINA?

City News

Majiyoyi masu karfin gaske dake da alaka jami'an tsaro masu sanya Ido da tattara bayanai akan masu aikata, miyagun laifuffuka sun tabbatar ma da Jaridun Katsina City News, cewa anga wasu Babura k**ar guda arba in sun baro Dutsen Sola garin shahararren Dan ta addar nan mai suna Adamu Aleru, sun tunkaro jahar Katsina.

Wasu kauyukan da masu Baburan s**a bi, wani Ɗan sa kai ya tabbatar ma da Jaridun mu cewa sun Kirga Babura 40 kowane Babur da goyon daya-daya.

Wata majiya tace, sun rika haduwa da wasu Baburan akan hanya suna hadewa dasu.

Majiyarmu tace, yaran Aleru sun fita daga dajin Zamfara ya zuwa lokacin wannan rahoton suna cikin dajin jahar Katsina.

Majiyarmu tace, Babu Wanda yasan ina zasu kai Kari? Ko kuma ina s**a dosa?

Adamu Aleru, shine Wanda aka ba sarkin Fulanin daji a jahar Zamfara, kuma yana da kyakykawar alaka ta sulhu da Gwamnatin jahar Zamfara.

Wadannan miyagun ko ina s**a dosa? Ko ina zasu kai Hari? Allah yayi maganin su.

Gobe Talata Ƙungiyar Ladon Alkhairi Za Ta Kaddamar Da Shugabanninta Na Shiyyar KatsinaShahararriyar Kungiyar Nan Mai Kok...
12/09/2022

Gobe Talata Ƙungiyar Ladon Alkhairi Za Ta Kaddamar Da Shugabanninta Na Shiyyar Katsina

Shahararriyar Kungiyar Nan Mai Kokarin Fadakar Da Al'ummar Jihar Katsina, Cancantar Sanata Yakubu Lado Danmarke Zama Gwamnan Jihar Katsina A Ƙarƙashin Jam'iyyar PDP, Kungiyar Ladon Alkhairi Za Ta Kaddamar Da Shugabanninta Na Shiyyar Katsina Ta Tsakiya A Gobe Talata Idan Allah Ya Kaimu.

Bayanin Hakan Na Kunshe A Cikin Wata Takardar Manema Labarai Da Darakta Janar Na Ƙungiyar, Honarabul Musa Gafai Ya Sanya Wa Hannu Aka Rabawa Manema Labarai A Katsina Yau Litinin.

Honarabul Musa Gafai Ya Kara Da Cewa Shugabannin Da Za'a Kaddamar Sun Fito Daga Kananan Hukumomin Goma Sha Ɗaya Na Mazabar Majalisar Dattawa Na Shiyyar Katsina.

Address

Yahaya Madaki Way Opposite Danmarna Filling Station
Katsina
820241

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina City News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share