RG online tv

RG online tv Gaskiya da Gaskiya

Yadda jigo a tafiyar matasa ya canza sheƙa zuwa jam’iyyar adawa ta ADC a jihar Katsina Wani jigo a cikin tafiyar matasa ...
02/03/2026

Yadda jigo a tafiyar matasa ya canza sheƙa zuwa jam’iyyar adawa ta ADC a jihar Katsina

Wani jigo a cikin tafiyar matasa a jihar Katsina ya sauya sheƙa zuwa jam’iyyar adawa ta ADC.

Usman Alasan Ruwan Godiya wanda ya kasance mai magana da yawun tafiyar matasa a jihar Katsina, ya wallafa a shafinsa na Facebook katin mambarship na jam’iyyar ADC, tare da bayyana wasu dalilai da s**a sa ya bar tafiyar matasa ya koma jam’iyyar haɗakar adawa ta ADC a jihar.

Tsohon mai magana da yawun tafiyar matasan ya tabbatar da sauyin ne ta hanyar wallafar bayanin nasa, inda ya ce matakin ya zo ne bayan nazari da tunani kan makomar siyasa da burinsa na ci gaba da hidimtawa al’ummar ƙaramar hukumar faskari da jahar katsina baki daya

DAGA JIGAWAR NAJIRIYA:Ga Walida Abdulhadi Ibrahim tare da ‘yarta suna cikin kulawa da Gwamnatin Jihar Jigawa bayan kamma...
26/02/2026

DAGA JIGAWAR NAJIRIYA:Ga Walida Abdulhadi Ibrahim tare da ‘yarta suna cikin kulawa da Gwamnatin Jihar Jigawa bayan kammala mika su ga hukumomin jihar.

Rahotanni sun tabbatar da cewa a halin yanzu Walida na tare da Kwamishiniyar Ma’aikatar Harkokin Mata da Ci gaban Al’umma ta Jihar Jigawa, inda ake ci gaba da duba lafiyarta tare da tabbatar da samun kulawa da ya dace.

Majiyoyi daga gwamnati sun bayyana cewa an dauki matakan ne domin tabbatar da tsaro, walwala da kare mutuncinta, yayin da ake ci gaba da bin dukkan hanyoyin da doka ta tanada kan lamarin.

Gwamnatin Jihar Jigawa ta jaddada kudurinta na kare hakkokin ‘yan kasa tare da tabbatar da cewa an gudanar da al’amura cikin gaskiya da adalci.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya karɓi wata tawaga daga kamfanin Google a ofishinsa a ranar Tal...
26/02/2026

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya karɓi wata tawaga daga kamfanin Google a ofishinsa a ranar Talata, 25 ga Fabrairu, 2026.

Tawagar ta Google ta kasance ƙarƙashin jagorancin Charles Murito, Daraktan Yankin Afirka ta Kudu da Hamadar Sahara, tare da Adewolu Adene, Shugaban Harkokin Gwamnati da Manufofin Jama’a na Google, da kuma Dewole Ajao, Shugaban Kula da Ababen More Rayuwa na Google a Yammacin Afirka.

Ziyarar ta mayar da hankali ne kan tattauna fannoni na haɗin gwiwa da kuma damar aiki tare tsakanin Gwamnatin Tarayyar Najeriya da kamfanin Google.

Sabon Sufeto Janar na ƴan sanda Tunji Disu ya k**a aiki bayan karmar ragama daga hannun tsoho Sufeto Janar Kayode Egbeto...
26/02/2026

Sabon Sufeto Janar na ƴan sanda Tunji Disu ya k**a aiki bayan karmar ragama daga hannun tsoho Sufeto Janar Kayode Egbetokun a yau Laraba.

Me tallafawa gwamnan jahar Bauchi a ɓangaren matasa Bala Sale Chiroma Yayin wani shiga na sulke chikin rakiyar Gwamna a ...
26/02/2026

Me tallafawa gwamnan jahar Bauchi a ɓangaren matasa Bala Sale Chiroma Yayin wani shiga na sulke chikin rakiyar Gwamna a jejin Duguri /Gwana

An ga jinjirin watan Ramadan a SaudiyyaMusulmi za su tashi da azumi a gobe Laraba
17/02/2026

An ga jinjirin watan Ramadan a Saudiyya
Musulmi za su tashi da azumi a gobe Laraba

Hukumar EFCC Ta K**a Tauraruwar Kannywood, Samha Inuwa Kan Zargin Lalata NairaHukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Ji...
04/02/2026

Hukumar EFCC Ta K**a Tauraruwar Kannywood, Samha Inuwa Kan Zargin Lalata Naira

Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano, EFCC, a ranar Talata, 3 ga Fabrairu, 2026 ta k**a wata jarumar Kannywood, Samha Inuwa bisa zargin lalata Naira.

An k**a Inuwa bayan wani bidiyo da aka yaɗa a shafukan sada zumunta inda aka gan ta tana share majina daga hancinta ta amfani da kuɗin Naira.

Bayan fitar da bidiyon, Hukumar ta ɗauki mataki ta hanyar bin diddigin ta sannan ta k**a ta don amsa tambayoyi.

A halin yanzu tana tsare a wurin tsarewar Hukumar yayin da ake ci gaba da bincike.

Za a gurfanar da wanda ake zargi a gaban kotu bayan kammala bincike.

Inna LillaHi Wa Inna IlaiHi Raji'unNan wasu daga cikin gawarwakin da yan bindiga s**a kashe da ranar yau a garin Doma ta...
04/02/2026

Inna LillaHi Wa Inna IlaiHi Raji'un

Nan wasu daga cikin gawarwakin da yan bindiga s**a kashe da ranar yau a garin Doma ta Tafoki dake karamar hukumar Faskari

Rahotanni na nuni da cewa sama da mutum 20 yan bindigar s**a kashe a wannan harin doma dai wane kauyini Wanda ki iyaka da tafoki da Ruwan Godiya a karmar hukumar faskari

Usman Alhasan – Ruwan GodiyaMuna kira da babbar murya ga Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, Mal. Dikko Umar Radda, da ya d...
26/01/2026

Usman Alhasan – Ruwan Godiya

Muna kira da babbar murya ga Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, Mal. Dikko Umar Radda, da ya duba halin da ake ciki tare da ɗaukar mataki na gaggawa kan hanyar Kankara zuwa Sheme, wadda ke haɗa ƙananan hukumomi uku a wannan yanki.

Wannan hanya na da matuƙar muhimmanci ga rayuwar al’umma, ganin irin gudunmawar da mutanen yankin s**a bayar wajen zaɓen gwamnatinsa, har ma da sadaukar da rayukansu domin samun shugabanci nagari.

Haka kuma, muna jaddada cewa za mu kula da wasu ’yan’uwanmu a kafafen hidima, musamman waɗanda ba su fahimci rawar da kafafen hidima ke takawa ba wajen ci gaban al’umma.

Idan har matasan Ƙaramar Hukumar Faskari s**a ci gaba da yin watsi da siyasar mai gida wanda bai damu da halin da mutanensa ke ciki ba, ko da lokaci ya ja, hakan zai kai mu ga koma baya da jahilci.

Don haka, muna kira ga matasan Faskari da su tashi tsaye, su haɗa kai, su bayar da gudunmawa domin ganin yankinmu ya samu ci gaba mai ɗorewa.

11/01/2026

Wata sabuwa:daya daga cikin Ya 'yan tafiyar matasa the movement sun faraja dabaya

11/01/2026

Address

Ruwan Godiya
Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when RG online tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to RG online tv:

Share

Category