Nasara Clique Media Team

Nasara Clique Media Team Nasara Clique Media Team

GWABNATI KE AMFANA DA TASHIN DALABy: Abubakar Salihu Dantsuntsu 22/02/2024 - 06:18 PMGwamnatin tarayya ce ke amfana da t...
23/02/2024

GWABNATI KE AMFANA DA TASHIN DALA

By: Abubakar Salihu Dantsuntsu
22/02/2024 - 06:18 PM
Gwamnatin tarayya ce ke amfana da tsadar dala - Sanata Ali Ndume

Sanata Ali Ndume ya ce gwamnatin tarayya bata yin asara daga karyewar darajar Naira akan Dalar Amurka, sai dai ma samun riba domin samun ƙarin kuɗin shigar da za ta aiwatar da kasafin kudin 2024.

Ya bayyana cewa kasafin kudin 2024 da shugaba Bola Tinubu ya gabatarwa majalisar dokoki a watan Nuwamba, kasafi ne na dala kan kuɗin da za su riƙa shigarwa gwamnati, saboda galibin kuɗin shigar da za su zo ma gwamnati daga ɗanyen man fetur ne da ta ke fitarwa waje, wanda ake sayarwa kan farashin dala.

Da yake magana a lokacin da gidan talabijin na Channels ke zantawa da shi, Sanata Ali Ndume ya ce ya yin da darajar dala ke ci gaba da ƙaruwa, gwamnatin za ta samu kuɗin Naira masu yawa da za ta gudanar da manyan ayyuka.

Ya ƙara da cewa babban arziƙin da Nijeriya ta ke da shi man fetur ne, kuma har yanzu ana matuƙar buƙatarsa a kasuwar duniya, kan haka Nijeriya za ta amfana sosai daga kasuwar hada-hadar chanjin kuɗin waje.

Da dumi'dumi: An bawa gwamnoni Naira Biliyan 30bn su rabawa jama'rsu domin rage radadin tsadar rayuwar da ake fuskanta ~...
22/02/2024

Da dumi'dumi: An bawa gwamnoni Naira Biliyan 30bn su rabawa jama'rsu domin rage radadin tsadar rayuwar da ake fuskanta ~Sanata Godswill Apabio

Ya ƙara da cewa baya ga N2bn da gwamnatin tarayya ta ba gwamnoni aro, Ya ce kowace jiha sun samu ƙarin wasu N30bn daga hannun FIRS.

Kuma ya faɗi haka ne a zaman majalisa na ranar Laraba 21 ga watan Fabrairun 2024, Ya ƙara da faɗin daga wajen kason da gwamnonin suke samu daga asusun tarayya domin a taimaka masu su magance matsalar ƙarancin abinci.

Kazalika, Akpabio ya ce gwamnoni suna da rawa sosai da za su taka, ya nanata zargin cewa suke da iko da ƙananan hukumomin, Kuma ya yi kira ga gwamnatocin jihohi su yi amfani da kuɗin yadda ya dace domin yunwa ta ragu a yankin su.

Me zaku ce?

Akwai ban tausai da tayar da hankali a labarin Kabiru Yusuf ma'aikacin gidan gyaran hali da yan bindiga s**a dauka a cik...
22/02/2024

Akwai ban tausai da tayar da hankali a labarin Kabiru Yusuf ma'aikacin gidan gyaran hali da yan bindiga s**a dauka a cikin garin Bilbis bayan kwanaki, yau ake zargin har sun hallaka shi

A yau an tashi cikin jimami gami da alhini bisa labarin da ya bulla na cewa yan bindigar da s**a yi garkuwa da Kabiru Yusuf ma'aikacin gidan gyaran hali dake jihar Zamfara, sun kashe shi, bayan har an biya kudin fansa Naira miliyan uku ba tare da sun sako shi ba.

Kamar yadda Katsina Daily News ta samu, daga wasu ganau a yankin Sabon Garin Bilbis dake cikin karamar hukumar Faskari nan jihar Katsina, shi ne kusan kasa da sati biyun da s**a gabata, shi Kabiru Yusuf yana da mata a nan cikin garin Bilbis, ya kawo ta ta gaisa da iyayenta, ranar da ya dawo daukar matar ya shigo cikin garin na Bilbis a nan unguwar Maje, ashe yan bindigar sun biyo shi har cikin garin, kafin ya buɗe mota ya fito har sun zagaye shi, nan s**a yi gaba da shi

Wata majiyar ta ce bayan da yan bindigar s**a fahimci cewa jami'in tsaro ne sun rika azabtar da shi fiye da kowa a wurin, inda wasu matan da yan bindigar s**a yi garkuwa da su kusan lokacin da s**a dauke jami'in tsaron, bayan an biya kudin fansarsu Naira dubu dari biyu da hamsin su biyar an biya jimillar Naira miliyan ɗaya kenan, bayan sun fito, s**a bayyana wa yan uwansa cewa, sai dai a yi hakuri, amma yan bindigar sun daɗe ma da kashe shi, duk da haka ƴan uwan jami'in tsaron dake magana da masu garkuwar game da biyan kudin fansar, s**a yi waya da yan bindigar a nan ma s**a tabbatar masu da maganar matan, k**ar yadda majiyar ta rawaito.

Yankin karamar hukumar Faskari, yanki ne dake fama da matsalar tsaro, inda ko a daran jiya yan bindigar sun shiga garin Munhaye dake yankin Sabon Layi, inda s**a kone shago ɗaya, tare da harbin mutum ɗaya sannan kuma s**a yi garkuwa da wasu

Haka abin yake a garin Yankara, inda masu garkuwa da mutane s**a shiga cikin garin bayan sun yi harbe-harbe, s**a fasa gidan ta baya s**a shiga s**a dauki matar wani magidanci mai suna Babangida Usman

Duka hakan na zuwa ne kasa da kwanaki biyu da shigarsu garin Yan-nasarawa duka a cikin karamar hukumar ta Faskari, inda s**a kashe kusan mutum 8, sannan s**a kone shaguna da gidaje tare da kore shanu da kuma yin garkuwa da kusan mutum 45

A yau kenan 22/02/2024. Wajen gaisuwar Shugaban Tsaro na, Katsina state community watch corp's na yankin Kankara Wanda A...
22/02/2024

A yau kenan 22/02/2024. Wajen gaisuwar Shugaban Tsaro na, Katsina state community watch corp's na yankin Kankara Wanda Allah yayi mashi Rasuwa A jiya 21/02/2024 yayin Gumurzu da s**ayi Da Barayin Daji Wato Bandits muna Rokon Allah Ubangiji ya Gafarta mashi Ameen!!

Mai Girma mataimakin Gwamnan jahar katsina Mal.Faruk Lawal Jobe, yana Mika Ta'a ziyyarshi ga Iyalan mamacin da Kuma Al'ummar Garin Kankara gaba daya, Allah ya jikanshi ya Gafarta Allah yasa Aljannah ce makomarshi Ameen.

Da Duminsa: Sojoji sun tarwatsa gungun matasan da s**a daka Wawa a motocin dakon kayan abinci da s**a dakko shinkafa a j...
22/02/2024

Da Duminsa: Sojoji sun tarwatsa gungun matasan da s**a daka Wawa a motocin dakon kayan abinci da s**a dakko shinkafa a jihar Niger

Matasan sun saci buhunan shinkafa da taliya na tirelolin da za su wuto zuwa Kaduna

Wani abu mai k**a da mafarki da ya faru a yankin Suleja dake cikin jihar Niger a yau Alhamis, shi ne yadda wasu gungun matasa dake zanga-zangar kukan yunwa, s**a tare manyan motocin dakon bayan abinci da duka hada da shinkafa da taliya

Matasan sun tare hanyar ne ta Suleja da ta taso daga Kudancin Nijeriya ta yo Abuja za su hau kan hanyar zuwa Kaduna

Duk da sojoji sun kai dauki wurin da lamarin ya faru, amma majiyarmu ta rawaito cewa da dama daga cikin matasan sun yi nasarar tserewa da buhunan shinkafa da kuma Kwalayen taliya da dama

Meye Gaskiyar Wannan Maganar?
22/02/2024

Meye Gaskiyar Wannan Maganar?

GWAMNA DIKKO GASKIYA A SAKE LALERubutawah, AbdulHadi Ashamed Bawa✍️Yanzu nike kallon wani rahoto a TRUST TV a kan harin ...
22/02/2024

GWAMNA DIKKO GASKIYA A SAKE LALE

Rubutawah, AbdulHadi Ashamed Bawa✍️

Yanzu nike kallon wani rahoto a TRUST TV a kan harin 'yan bindiga a kauyen lamba, Wurma B, ta karamar hukumar Kurfi.

Abinda ya dauki hankalina shi ne yadda dan jaridar, daga nan cikin garin Katsina, ya sami labari har ya isa kauyen ya sami janazar mutane takwas din da aka kashe, amma kuma babu wakili ko daya, walau na karamar hukumar Kurfin ko na gwamnatin jiha.

A yadda ya fadi a rahoton shi, a duk jami'an gwamnati da ya nemi yaji ta bakin su, babu ɗaya da ya bashi wani bayani kan wannan lamari. Daga wanda yace ba hakkin shi bane bada bayanin, sai kuma wadanda basu daga wayarsu ba kuma sakon (SMS) da ya tura masu har ya zuwa bada rahoton babu amsa daga gare su.

Wannan rahoto ya nuna k**ar gwamnatoci basu damu da halin da al'umma suke ciki ba, ko suke shiga ba idan irin haka ta faru. Bahaushe ke cewa "sannu ba ta warkar da ciwo, amma tana da dadi".

Ya k**ata gwamnati ta sani cewa, bada bayanai sahihai a kan irin wadannan hare haren ba shi ke nuna gazawarta ba, hasali ma, badawar za ta hana yada nakasassun bayanai ga duniya, su kuma al'ummar da abin ya shafa za su san cewa gwamnati ta damu tare da nuna kulawa ga halin da suke ciki.

A wasu jihohin, gwamnatocin su ke fara fitar da bayani idan aka sami irin haka; bayanin yana kumsar sunan garin da abin ya afku tare da bayyana yawan mutanen da abin ya shafa har da sunayen su (wadanda s**a rasa rayuka da kuma wadanda aka jikkata), tare da sakon jajantawa tare da alhini gami da matakin da gwamnati ta dauka ko za ta dauka.

A cikin kwanaki hudu da s**a gabata, Allah kadai Ya san iyakar rayuka da dukiyar da aka rasa ta sanadiyyar wadannan hare hare, amma dai har yanzu banji gwamnatin jiha ta ce komai ba (kila kuma nine ban ji ba). Ko jiya an kashe kwamandan CWC na karamar hukumar Kankara, amma dai ni ban ga inda aka ce ita rundunar ko kuma gwamnati ta bada sakon jaje ga al'umma ba, musamman iyalan mamacin.

Ita kanta rundunar ta CWC, ban taba jin ta bada sanarwa ba, walau ta samun nasara ko akasi, duk kuwa da cewa a wurare da dama ta rasa jami'anta ta hannun wadannan 'yan ta'adda, a wasu lokutta kuma tana samun masu s**ar matakan da take dauka wajen gudanar da aikin ta.

Ya k**ata yadda sauran hukumomin tsaro suke da bangarorin hulda da jama'a, ita ma wannan runduna ya k**ata a sama mata nata, don ta rika bayar da sahihan rahotanni kan wannan aiki nata mai muhimmancin gaske.

Ina rokon gwamnati ta kalli wannan batu da idon basira, matsin da ake ciki yanzu, duk ya matso da zukatan mutane kusa. Ma'ana, ba wuya sai kaga abu kalilan amma mutum sai hassala, ka rasa kasa gane kan shi.

Ya Allah Ka ƙara tausaya mana, Kayi maganin abinda ya ishe mu.

Allahumma Aamiiin Ya Hayyu Ya Qayyum.

Shaye-Shaye Ba Naku Bane MatasaRubutawah, Mansir Lawal Baure✍️Lokaci ya wuce da za'a Rika amfani daku Don bukatar Kai da...
21/02/2024

Shaye-Shaye Ba Naku Bane Matasa

Rubutawah, Mansir Lawal Baure✍️

Lokaci ya wuce da za'a Rika amfani daku Don bukatar Kai da Kai.

Daku Ake Gina kasa Kuma ana amfani daku wajan rusa ta.

"Matasa kune ƙashin bayan ci gaban al'umma, Gujewa Shaye-shaye Shine matakin farko da zaku dauka Don bawa kanku damar yin ingantaccen Tunanin dazai ciyar daku gaba.

Sai daku ake samun cigaba mai ɗorewa, Ku gujewa ta'ammali da duk wani nau'i na kayan Maye.

INNALILLAHI WA'INNA ILAHIRRAJIUN ||'Yan Bindiga Sun Kashe Shugaban Hukumar Tsaron  da Gwamnatin jihar Katsina ta Samar d...
21/02/2024

INNALILLAHI WA'INNA ILAHIRRAJIUN ||

'Yan Bindiga Sun Kashe Shugaban Hukumar Tsaron da Gwamnatin jihar Katsina ta Samar domin dakile Hare-hare Yan Bindiga Masu suna Katsina State Community Watch Corp Na Karamar Hukumar Kankara Jihar Katsina Malam Sanusi Hassan.

Kamar yadda majiyar Rana24 ta ruwaito yan Bindiga sun kashe shine alokacin Wani artabu da aka gwabza a dajin garin Burdugau Ayau Laraba 22/2/2024

Allaha yajika shi da rahama Amin

‘Yan siyasar da s**a fadi zaben 2023 sune s**a jawo yunwa, tsadar rayuwa da hauhawar farashin kayayyaki - Kashim Shettim...
21/02/2024

‘Yan siyasar da s**a fadi zaben 2023 sune s**a jawo yunwa, tsadar rayuwa da hauhawar farashin kayayyaki - Kashim Shettima

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya zargi ‘yan siyasar da s**a sha kayi a zaben 2023 da yunkurin jefa Najeriya cikin rikici, tare da yiwa kasar zagon kasa ta hanyar safarar abinci zuwa wasu kasashe domin tayar da farashin kayan abinci.

Mista Shettima, a ranar Talata a wani taro kan harkokin kula da dukiyar jama’a a Abuja, ya yi ikirarin cewa an k**a manyan motoci 45 da ke safarar abinci daga kasarnan.

“Kimanin dare uku da s**a gabata, an k**a manyan motoci 45 na masara ana jigilar su zuwa kasashe makwabta,” in ji Mista Shettima. "Akwai a cikin wannan layin na Ilela, akwai hanyoyin fasa kwabri guda 32."

Ya kuma kara da cewa, a dalilin haka, farashin masara ya fadi.

“Kuma a lokacin da aka k**a wadannan kayan abinci, farashin masara ya fadi da N10,000. Ya sauko daga N60,000 zuwa N50,000. Don haka, akwai dakarun da ke da niyyar yi wa al’ummarmu zagon kasa, amma wannan lokaci ne da ya k**ata mu hada kai zuwa wata kungiya daya,” in ji Mista Shettima.

Mataimakin shugaban kasar ya jaddada cewa wasu ’yan siyasa na da burin su jefa Najeriya cikin rikici saboda gazawar da s**a yi na kwace mulki a zaben da ya gabata.

“Suna da niyyar jefa kasar nan cikin wani hali na rashin zaman lafiya. Wadanda ba za su iya samun mulki ta hanyar akwatin zabe ba, maimakon su jira har zuwa 2027, sun yi matukar bakin ciki,” Mista Shettima ya jaddada.

Ya kara da cewa, “Dole ne mu sanya kasar nan ta yi aiki. Dole ne mu wuce siyasa. A yanzu muna fuskantar gwamnati. Abin bakin ciki, har yanzu wasu daga cikin ‘yan kasarmu suna cikin yanayin siyasa.

"Su ne masu aikata ta'addanci, suna ba da shawarar cewa Najeriya ta bi hanyar Lebanon. Najeriya za ta shawo kan guguwar."

Mista Shettima bai ambaci sunayen ‘yan siyasar da ya zarga da jefa kasar nan cikin rudanin tattalin arziki da kuma yiwa gwamnatin Shugaba Bola Tinubu zagon kasa ba.

Address

Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Nasara Clique Media Team posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Nasara Clique Media Team:

Share