14/08/2026
Muhammad Gambo Fagada (Gambu mai waƙar ɓarayi)
Muhammadu Gambu ya kasance Makadi ne mai fasahar gaske. Kuma wakokinsa cike suke da balaga da azanci da salon magana. Duk da karin harshensa ya yi matukar tasiri cikin wakokinsa, amma wannan bai hana manazarta da masu sha’awar wakokinsa fahimta tare da nazartarsu ba.
Mawaƙin ya shahara da waƙoƙin ɓarayi, a lokacin da yake waƙa, to sai dai ya tuba da waƙoƙin na ɓarayi a shekarar 2009 a yayin da aka yi wani gagarumin bikin cikarsa shekara 60 a duniya, a Jami’ar Usman Danfodiyo da ke Sakkwato.
An haifi Alhaji muhammad Gambo wanda da akafi sani da Gambu a garin fagadan dake karamar hukumar Jega a jihar Kebbi a Najeriya. Gambu tun tasowar yarintarsa yana da rashin ji ga kuma rashin tsoro.
Asalin sunan Gambu shi ne Muhammad Gambo, tun a wancen lokacin wasu kan kirashi da Gambu kasancewar rashin iya fadin sunan Gambo din kai tsaye.
Mahaifin Gambu shahararren Malami ne, yayin da shi kuma Gambu ba ruwansa da son gadon maihaifin nasa don haka nema Gambu kan dauki kayan harbinsa a kullum ya tafi Jeji harbin Tsuntsaye da kuma sauran namun Daji.
Duk lokacin da Gambu ya samo naman dajinsa sai ya taho gari ya saidawa da masu c**a, haka kuma shi ma a nan zaiyi zamansa.
Gambu ya fara mu’amala da barayi ne a wurin yin c**a, kasancewar duk lokacin da Gambu yayiwo farauta to a gurin yake zama har zuwa dare. Wannan dalilin ne yasa Gambu ya fara sanin barayi masu tare Hanya, da masu fasa shaguna da dai sauransu.
Gambu kan ambaci Kulu a cikin wakokinsa ne saboda ita Kulu itace matarsa ta farko da mahaifiyarsa ta aura masa, don haka yake sonta tare da mutunta ta kasancewar mahaifiyarsa ce ta zaba masa ita.
Alhaji Gambu ya rasu ranar Laraba 18 ga watan agusta 2016, ya rasu yana da kimanin shekaru 67 a duniya. Yabar mata 4 da “Yaya da kuma jikoki masu yawa. Ya rasu ne a garin Maiyama na Jihar Kebbi, yayin da a ke kan hanyar kai shi asibiti.
Muhammadu Cisse