HRtv Network

HRtv Network For Updating News and Entertainment.

INEC ta mayar da lokacin zaɓen 2027 kafin AzumiHukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC ta sanya ranar 16 ga Janairu, 2...
27/02/2026

INEC ta mayar da lokacin zaɓen 2027 kafin Azumi

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC ta sanya ranar 16 ga Janairu, 2027, a matsayin sabuwar ranar gudanar da zaɓen Shugaban Ƙasa da na ‘yan Majalisar Tarayya.

Haka kuma, hukumar ta ayyana ranar 6 ga Fabrairu, 2027, a matsayin sabuwar ranar gudanar da zaɓen gwamnonin jihohi da na ‘yan Majalisun Dokokin Jihohi.

A sanarwar da hukumar ta fitar ta bayyana cewa za a gudanar da zaɓen fidda gwani na jam'iyyun daga watan Afrilu zuwa Mayu na 2026

Kotu ta umarci INEC ta yi wa jam'iyyar NDP rijistaBabbar kotun tarayya da ke Abuja ta umarci Hukumar Zabe Mai Zaman Kant...
20/02/2026

Kotu ta umarci INEC ta yi wa jam'iyyar NDP rijista

Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta umarci Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da ta yi rajistar jam’iyyar National Democratic Party (NDP) a matsayin jam’iyyar siyasa kamar yadda jaridar TheCable ta rawaito.

Mai shari’a Mohammed Umar, yayin yanke hukunci a ranar 16 ga Fabrairu, ya ce masu karar sun cika dukkan sharuddan da Kundin Tsarin Mulki da Dokar Zabe ta 2022 s**a tanada domin rajista.

Kotun ta soke wasikar INEC ta ranar 18 ga Disamba, 2025, wadda ta ki amincewa da bukatar rajistar, tare da bayyana ta a matsayin mara inganci.

Alkalin ya umarci INEC ta yi rajistar jam’iyyar nan take, ta kuma ba ta dukkan hakkoki da takardun da ake bai wa jam’iyyun siyasa masu rijista.

Kotun ta kuma ce idan ba a aiwatar da rajistar ba, za a dauki NDP a matsayin wadda aka yi wa rajista bisa tanadin dokar zabe.

A fara duba jinjirin watan Ramadan a ranar Talata - majalisar koli ta addinin musulnci a Najeriya Majalisar koli ta addi...
16/02/2026

A fara duba jinjirin watan Ramadan a ranar Talata - majalisar koli ta addinin musulnci a Najeriya

Majalisar koli ta addinin musulunci a Najeriya (NSCIA) ta bukaci Musulmi a fadin Najeriya da su fara duban jinjirin watan Ramadan 1447 A.H. bayan faduwar rana a ranar Talata, 17 ga Fabrairu, 2026, wadda ta yi daidai da 29 ga Sha’aban 1447 A.H.

A sanarwar da babban sakataren majalisar, Farfesa Is-haq Oloyede ya sanya wa hannu, an ce kwamitin duban wata na kasa tare da hadin gwiwar hukumar kula da sararin samaniya ta Najeriya (NASRDA) za su kula da aikin tabbatar da ganin watan.

Majalisar ta bayyana cewa idan an ga jinjirin watan a daren Talata, Mai Alfarma Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar, Muhammad Sa’ad Abubakar, zai sanar da Laraba, 18 ga Fabrairu, 2026 a matsayin ranar farko ta azumin Ramadan. Idan kuwa ba a ga watan ba, Alhamis, 19 ga Fabrairu, 2026 za ta zama ranar farko ta azumin.

Baya ga batun Ramadan, NSCIA ta nuna damuwa kan abin da ta kira karuwar nuna wariya ga Musulmi da yada labaran da ba su dace ba a kafafen yada labarai. Ta ce Musulmi na fuskantar hare-hare daga masu tada kayar baya da ‘yan bindiga, tare da zargin ana musu kallon da bai dace ba a wasu rahotanni.

Har ila yau, majalisar ta bayyana cewa ta samu koke-koke kan jadawalin zabe da INEC ta fitar, inda aka tsara gudanar da zaben shugaban kasa a lokacin Ramadan, da kuma yiwuwar zaben gwamna a ranar Sallah. Ta ce tana sa ran a sake duba jadawalin.

A karshe, NSCIA ta bukaci Musulmi da su kasance masu hakuri da tsayawa kan imaninsu, tare da amfani da watan Ramadan wajen addu’a, gyaran hali da karfafa zaman lafiya a kasa.

Gobara: Tinubu ya umarci Kashim Shettima ya ziyarci Kano Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya umarci Mataimakinsa, Kashi...
15/02/2026

Gobara: Tinubu ya umarci Kashim Shettima ya ziyarci Kano

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya umarci Mataimakinsa, Kashim Shettima, da ya jagoranci babbar tawagar Gwamnatin Tarayya zuwa Kano domin jajanta wa ’yan kasuwar Singer bisa gobarar da ta lalata dukiyoyi a karshen mako.

Tawagar, wadda za ta tashi daga Abuja gobe, za ta isar da sakon ta’aziyyar Shugaban Kasa ga ’yan kasuwar da s**a yi asarar biliyoyin Naira sakamakon gobarar, wadda ita ce ta biyu cikin makonni biyu a kasuwar.

Bayanin hakan na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasa Tinubu, Bayo Onanuga ya fitar a ranar Lahadi.

Acewar sanarwar, a madadin gwamnati, tawagar za ta kuma yi alkawarin bayar da tallafin kudi domin taimaka wa wadanda abin ya shafa tare da tallafa wa Jihar Kano wajen bude kasuwar cikin gaggawa.

Mambobin tawagar sun hada da Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas; Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin; Sanata Kawu Ismaila; da dan majalisar wakilai Abubakar Kabir Bichi, shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar.

Haka kuma, Ministan Harkokin Jin Kai, Dakta Bernard M. Doro, da Darakta-Janar na hukumar NEMA, Zubaida Umar, na cikin tawagar.

Shugaba Tinubu ya kuma yi waya da Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, inda ya mika ta’aziyyarsa ga ’yan kasuwa da al’ummar jihar bisa mummunar gobarar.

Tinubu ya bada umarnin gudanar da bincike kan gobarar kasuwar Singer Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya jajanta wa ‘ya...
15/02/2026

Tinubu ya bada umarnin gudanar da bincike kan gobarar kasuwar Singer

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya jajanta wa ‘yan kasuwa da al’ummar Jihar Kano kan gobarar da ta tashi a kasuwar Singer a karshen mako.

Gobarar wadda ta fara ne da yammacin ranar Asabar ta ci gaba da ƙonewa har zuwa safiyar Lahadi, inda ta lalata sassa da dama na kasuwar kayan abinci tare da haddasa asara mai yawa ga ‘yan kasuwa.

A cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai , Bayo Onanuga, ya fitar, Shugaban Ƙasar ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici da matuƙar damuwa. Ya ce tun da farko ya tuntubi Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, domin samun cikakken bayani kan yadda lamarin ya faru da kuma matakan da ake ɗauka.

Shugaba Tinubu ya nuna damuwa musamman ganin cewa wannan gobara ta zo kasa da makonni biyu bayan wata gobara ta baya da ta ƙone shaguna da dama tare da dukiyoyi a kasuwar .

Dangane da haka, ya bayar da umarnin a gudanar da cikakken bincike kan musabbabin gobarar kasuwannin da ke yawan faruwa, domin gano dalilai da kuma ɗaukar matakan kariya don hana aukuwar hakan a nan gaba.

Shugaban Ƙasar ya kuma tabbatar wa ‘yan kasuwar da abin ya shafa cewa Gwamnatin Tarayya na tare da su, tare da jaddada aniyar gwamnati na kare rayuka da dukiyoyin al’umma a fadin ƙasa.

Gwamnatin tarayya ta zaɓi Kano don gwajin  noman dabino daga SaudiyyaMa’aikatar Muhalli ta Tarayya ta zaɓi Jihar Kano do...
15/02/2026

Gwamnatin tarayya ta zaɓi Kano don gwajin noman dabino daga Saudiyya

Ma’aikatar Muhalli ta Tarayya ta zaɓi Jihar Kano domin aiwatar da shirin gwaji na wata Manufar Bunƙasa Dabino da King Salman Humanitarian Aid and Relief Centre (KSrelief) ta gabatar.

Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi na Jihar Kano, Dakta Dahir M. Hashim, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a Kano bayan karɓar baƙuncin wakilan KSrelief.

Hashim ya ce an zaɓi Kano ne saboda yanayinta mai dacewa da noman dabino da kuma muhimmancin dabino a al’ada da addini a cikin al’umma.

Ya bayyana cewa shirin zai yi amfani da sabbin dabarun shuka tare da haɗa ƙwararru daga Saudiyya da kuma masana daga Jihar Kano domin tabbatar da zurfin ilimi da musayar ƙwarewa.

“A yau mun karɓi wakilan King Salman Humanitarian Aid and Relief Centre (KSrelief), waɗanda ma'aikatar muhalli ta tarayya ta gabatar mana da su dangane da shirin Manufar Bunƙasa Dabino da za a fara aiwatarwa a Jihar Kano.

“An zaɓi Kano ne saboda yanayinta mai dacewa da noman dabino da kuma muhimmancin wannan itaciya a cikin al’ummarmu. Shirin zai yi amfani da sabbin dabarun shuka tare da haɗa ƙwararru daga Saudiyya da kuma masana daga Kano domin tabbatar da zurfin ilimi da musayar ƙwarewa.”

Ya ƙara da cewa, a madadin Gwamnatin Jihar Kano da Mai Girma Gwamna Abba Kabir Yusuf, suna yaba wannan tsari na gaba-gaba, yana mai jaddada cewa itatuwan dabino na da muhimmanci wajen yaƙi da sare dazuzzuka, faɗaɗa shingen itatuwa (shelterbelt), da kuma manufofin da s**a shafi daidaitawa da rage tasirin sauyin yanayi.

Dakta Hashim ya lura cewa shirin ba wai na shuka itatuwa kaɗai ba ne, illa dai wani cikakken aikin raya ƙasa ne da ke da amfani ta fuskar muhalli, tattalin arziki da zamantakewa.

Ya kuma buƙaci tawagar da ta zo da ta tabbatar da haɗa al’umma sosai domin ƙarfafa mallaka da dorewar shirin a nan gaba.

A ƙarshe, ya sake jaddada cewa ma’aikatar a buɗe take ga duk wata haɗin gwiwa mai inganci da za ta ƙarfafa juriya da samar da hanyoyin samun abin yi ga al’umma.

Hotuna: yadda Shugaban mulkin sojin Nijar Janar Abdoulramane Tchiani ya tafi ƙasar Algeriya domin kai ziyarar aiki na kw...
15/02/2026

Hotuna: yadda Shugaban mulkin sojin Nijar Janar Abdoulramane Tchiani ya tafi ƙasar Algeriya domin kai ziyarar aiki na kwanaki biyu.

NEMA ta jagoranci aikin kashe gobarar Kasuwar Singa a KanoHukumar ba da Agajin gaggawa  ta Ƙasa (NEMA) ta jagoranci haɗi...
15/02/2026

NEMA ta jagoranci aikin kashe gobarar Kasuwar Singa a Kano

Hukumar ba da Agajin gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta jagoranci haɗin gwiwar hukumomi daban-daban domin shawo kan gobarar da ta tashi a Kasuwar Singa da ke Jihar Kano a ranar Asabar.

An rawaito cewa gobarar ta tashi da misalin ƙarfe 4:30 na yamma, inda ta shafi wasu sassan kasuwar mai cunkoso, tare da haifar da barazana ga rayuka da dukiyoyi.

A sanarwar da ta fitar, Darakta Janar ta NEMA, Mrs. Zubaida Umar, ta ce an ankar da ofishin ayyukan hukumar na Kano nan take bayan samun rahoton lamarin, inda aka tura tawagar ceto zuwa wurin.

Hukumomin da s**a shiga aikin sun haɗa da Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya da ta Jihar Kano, sassan kashe gobara na kamfanoni masu zaman kansu, Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Kano, da kuma Red Cross ta Nijeriya.

NEMA ta ce ƙoƙarin kashe gobarar ya rage ƙarfin wutar sosai, yayin da jami’an agaji ke ci gaba da aiki domin kashe ta gaba ɗaya tare da hana yaɗuwarta zuwa gine-ginen da ke kusa.

El-Rufai ya musanta hannu a ɓacewar Dadiyata, ya dora zargi kan Gwamnatin GandujeTsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-R...
14/02/2026

El-Rufai ya musanta hannu a ɓacewar Dadiyata, ya dora zargi kan Gwamnatin Ganduje

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya musanta zargin cewa yana da hannu a ɓacewar Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Dadiyata, tare da dora alhakin lamarin kan gwamnatin Kano a zamanin Abdullahi Umar Ganduje.

Idan za a tuna, Dadiyata ya ɓace ne tun ranar 2 ga Agustan 2019, bayan wasu da ba a san ko su waye ba sun ɗauke shi daga gidansa da ke unguwar Barnawa a Kaduna. Tun daga lokacin ba a sake jin duriyarsa ba, duk da kokarin iyalansa da masu fafutukar kare haƙƙin ɗan Adam na neman a gano inda yake.

Da yake magana a wata hira da ARISE TV, El-Rufai ya ce Dadiyata ba mai s**ar gwamnatin Kaduna ba ne, sai dai yana s**ar gwamnatin Kano ne, yana mai cewa shi ɗan tafiyar Kwankwasiyya ne daga Kano.

Ya kuma bayyana cewa bai san Dadiyata ba sai bayan faruwar sacewar.

Tsohon gwamnan ya ƙara da cewa, bayan wasu bincike da aka gudanar, an samu bayanin cewa waɗanda ake zargin sun sace Dadiyata sun fito ne daga Kano. A cewarsa, idan akwai wanda ya kamata a tambaya dangane da ɓacewar tasa, to gwamnatin Kano ta wancan lokaci ce ta fi dacewa da amsa tambayoyin.

Haka kuma, El-Rufai ya yi zargin cewa shekaru uku bayan faruwar lamarin, wani ɗan sanda da aka tura daga Kano zuwa Jihar Ekiti ya yi ikirarin cewa an aiko su daga Kano domin su sace Dadiyata, kuma daga bisani ya nuna nadamar abin da ya faru.

Har zuwa yanzu, babu wata hukuma da ta fitar da cikakken bayani kan inda Dadiyata yake ko halin da yake ciki.

Hajjin 2026: Maniyyata 1,253 sun yi gwajin lafiya da allurar rigakafi a Kano Hukumar jin daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta ...
14/02/2026

Hajjin 2026: Maniyyata 1,253 sun yi gwajin lafiya da allurar rigakafi a Kano

Hukumar jin daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala aikin gwajin lafiya da yi wa maniyyata allurar rigakafi domin shirye-shiryen Hajjin bana, inda adadin su ya kai 1,253.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Sulaiman Dederi, ya fitar, hukumar ta bayyana cewa wannan aiki na daga cikin shirye-shiryen da ake ci gaba da yi domin tafiyar Hajjin bana.

A cewar Dederi, an gudanar da gwajin lafiyar ne a Asibitin sansanin Alhazai (Hajj Camp Clinic), inda aka duba lafiyar maniyyata daga kananan hukumomi 20 na fadin Jihar Kano.

Ya ce an yi aikin ne domin tabbatar da cewa dukkanin maniyyata suna cikin koshin lafiya tare da samun cikakken rigakafi bisa ka’idojin lafiya na kasa da kasa da ake bukata wajen gudanar da aikin Hajji.

Da yake jawabi bayan kammala aikin, shugaban tawagar likitocin da s**a kula da gwajin, Dakta Aminu Da’u, ya tabbatar da nasarar kammala gwajin ga mahajjata 1,253.

Ya jaddada muhimmancin gwajin lafiya da allurar rigakafi wajen kare lafiyar mahajjata da tabbatar da jin dadinsu a duk tsawon lokacin gudanar da aikin Hajji.

Dakta Da’u ya kara da cewa ana gudanar da aikin cikin tsari da matakai domin bai wa dukkanin wadanda s**a yi rajista damar cin gajiyar shirin a fadin jihar.

Ya kuma tabbatar wa jama’a cewa kwararrun ma’aikatan lafiya ne ke gudanar da aikin cikin kulawa da kwarewa.

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sake jaddada kudurinta na tabbatar da tafiyar Hajji mai nasara ba tare da wata matsala ba, tare da bai wa lafiyar, tsaro da jin daɗin mahajjata fifiko.

Ana sa ran ci gaba da aikin gwajin lafiya da allurar rigakafi ga sauran mahajjata kamar yadda jadawalin ya tanada.

Jawabin shugaban kasar Najeriya Janar Murtala Muhammad a wajen taron kungiyar hada kan kasashen Afrirka (OAU) a birnin A...
13/02/2026

Jawabin shugaban kasar Najeriya Janar Murtala Muhammad a wajen taron kungiyar hada kan kasashen Afrirka (OAU) a birnin Adis Ababa na kasar Ethiopia (1976)

Mai Taken AFRIKA Ta Kawo Karfi.

Wannan jawabin martani ne ga wata wasika da Shugaban Kasar Amurka Gerald Ford da ke adawa da kungiyar MPLA mai goyon bayan rusashshiyar kasar tarayyar Soviet, wacce tafi karfin iko a kasar Angola. Mutanen Afirka ta kudu su na fada 'tare da bangarorin adawa ga MPLA. Janar Murtala ya nuna adawa ga burin Shugaba Ford tare da 'Yan Afirka ta Kudu, da kuma adawa da kudurin hana kasashen Africa magana a kan makomar su.

Janar Murtala Ramat Muhammad yace:

Ya Shugaba, lokacin da nake tunanin muguntar mulkin wariyar launin fata, zuciyata ta zubar da jini, kuma na tabbata zuciyar duk wani mai jini a jika na Afirka ta zubar da jini. Maimakon hada kai da sojojin da ke gwagwarmayar neman 'Yancin kai, da kuma nuna wariyar launin fata, wasu' 'masu tsara manufofi a Amurka a bayyane s**a yanke shawarar cewa 'ya fi dacewa da kasarsu don kiyaye fifikon fararen fata fiye da kananan Gwamnatoci a Afirka.

Afirka ta girma, ba zai yiwu Afirka ta sake karbar umarni daga hannun kowacce kasa ba! Komai karfin ta. Arzikin mu yana hannunmu. An dade ana wasa damu, na tsawon lokaci. Ana daukar mu kamar wasu wawaye wadanda basu san abinda su ke so ba.

Da dadewa sun dauki Afirka a matsayin waye abokin ka waye kuma abokin gabar ka?. Lokaci ya yi da za mu rinka yanke shawarar' makomar mu da kan mu.

An kashe Janar Murtala Ramat Muhammad Kwanaki 34 Bayan Yin Wannan Jawabin.

Wani ɗan Najeriya ya yi zargin an tilasta masa shiga rundunar sojin RashaAbubakar Adamu, wani ɗan Najeriya, ya roƙi gwam...
13/02/2026

Wani ɗan Najeriya ya yi zargin an tilasta masa shiga rundunar sojin Rasha

Abubakar Adamu, wani ɗan Najeriya, ya roƙi gwamnatin tarayya da ta gaggauta ɗaukar matakin dawo da shi gida daga ƙasar Rasha, bayan ya yi zargin cewa an yaudare shi aka shigar da shi rundunar sojin Rasha da sunan ba shi aikin gadi.

A cewar jaridar yaƙi da ta’addanci ta Zagazola Makama, lauyoyin Adamu sun sanar da hukumomin Najeriya halin da yake ciki a Rasha.

Lauyoyinsa sun bayyana cewa Adamu ya tafi Moscow da bizar yawon buɗe ido wadda Ofishin Jakadancin Rasha da ke Abuja ya ba shi a ranar 16 ga Oktoba, 2025, inda aka yi masa alƙawarin aikin sintiri.

Sai dai bayan isarsa Rasha, an ƙwace takardun tafiyarsa tare da tilasta masa sanya hannu kan takardun shiga soja da aka rubuta gaba ɗaya da harshen Rasha, ba tare da mai fassara ba.

Daga baya Adamu ya gano cewa an shigar da shi cikin rundunar sojin Rasha.

A cewar lauyoyinsa, a halin yanzu yana maƙale a sansanin sojin Rasha bayan tura shi yankunan yaƙi a Ukraine.

A ranar Alhamis, Hukumar Leken Asirin Tsaro ta Ukraine ta ce ta gano gawarwakin ’yan Najeriya biyu a yankin Luhansk, waɗanda ake zargin suna yaƙi a ɓangaren Rasha a yaƙin da ke gudana.

An bayyana sunayen ’yan Najeriyar da s**a mutu a matsayin Hamzat Kazeem Kolawole mai shekaru 42 da Mbah Stephen Udoka mai shekaru 38, waɗanda s**a rasu a ƙarshen watan Nuwamba 2025, watanni kaɗan bayan shiga rundunar sojin Rasha.

A wani bincike da CNN ta gudanar kwanan nan, an bayyana yadda ake zargin an yaudari ’yan Afirka daga Ghana, Najeriya, Kenya da Uganda zuwa Rasha da sunan ba su ayyukan farar hula kamar direbobi ko masu gadi.

Rahoton ya ce da zarar sun isa Rasha, ana zargin an tilasta musu shiga aikin soja tare da ba su ƙarancin horo kafin a tura su sahun gaba.

A ranar Talata, Andrey Podyelyshev, jakadan Rasha a Najeriya, ya musanta rahotannin tare da nisanta gwamnatin Kremlin daga shirin daukar ma’aikata da ake zargi.

Address

IBB Way
Katsina
820231

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when HRtv Network posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to HRtv Network:

Share