Zamani Media Crew

  • Home
  • Zamani Media Crew

Zamani Media Crew News
Reports
Enlightenment
Entertainment
Photos Videos Editing
Adverts
Documentary
Film Making etc Some Information

***JAJE***Shugaban Ƙungiyar Dikko Project Movement, Dr. Musa Yusuf Gafai na jajantama Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko...
21/07/2025

***JAJE***

Shugaban Ƙungiyar Dikko Project Movement, Dr. Musa Yusuf Gafai na jajantama Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa PhD CON FNAH da Al'ummar Jihar Katsina baki ɗaya dama na Najeriya akan wannan iftila'in haɗarin Mota daya rutsa da Gwamnan Jihar Katsina dama wasu Muƙarraban Gwamnati.

Ƙungiyar a madadin Shuwagabannin ta na Jiha dana Ƙananan Hukumomi 34 dake a Jihar nan suna jajantama Gwamna Raɗɗa akan wannan.

Hakanan kuma suna addu'ar Allah SWA ya tsare gaba.

Da fatan Allah SWA ya bamu lafiya da zama lafiya, ameen...

Sa Hannu
Dr. Musa Yusuf Gafai
Shugaban Ƙungiyar Dikko Project Movement

Ganduje na barar addu'ar ƴan Najeriya, jikinsa yayi tsanani yanzu haka an mayar da shi ɓangaren gaggawa na ƙwararrun lik...
20/07/2025

Ganduje na barar addu'ar ƴan Najeriya, jikinsa yayi tsanani yanzu haka an mayar da shi ɓangaren gaggawa na ƙwararrun likitoci a asibitin birnin Landan.

Surikin Gwamna Dikko Radda, Ahmad Uthman Ya Zama Gamjin Katsina Mai martaba sarkin Katsina Alhaji Abdulmuminu Kabir Usma...
20/07/2025

Surikin Gwamna Dikko Radda, Ahmad Uthman Ya Zama Gamjin Katsina

Mai martaba sarkin Katsina Alhaji Abdulmuminu Kabir Usman ya amince da naɗa haziƙin matashin nan mai rajin kare muhalli kuma surikin gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda, Alhaji Ahmad Uthman sarautar "Gamjin Katsina".

Bayanin hakan na kunshe a cikin wata takardar amincewar ba da sarautar, wadda mai martaba sarkin Katsina, Alhaji Abdulmuminu Kabir Usman ya sanya wa hannu.

Takardar ta kara da cewa nan gaba za a sanar da sabon Gamjin Katsina, Alhaji Ahmad Uthman Muhammad, ranar da za a yi bikin naɗi, Allah ya ba mu lafiya da zaman lafiya.

Allah Ya Taya Riƙo, Sabon Gamjin Katsina!

Tsohuwar Yar takarar gwamna a Adamawa Haj Aishatu Binani ta yanki mambaship na Jam'iyyar ADC
19/07/2025

Tsohuwar Yar takarar gwamna a Adamawa Haj Aishatu Binani ta yanki mambaship na Jam'iyyar ADC

Tsohon sakataren Gwamnatin jihar Katsina kuma jagoran jam'iyyar ADC na jihar Dr. Mustapha Inuwa tare da Alhaji Atiku Abu...
19/07/2025

Tsohon sakataren Gwamnatin jihar Katsina kuma jagoran jam'iyyar ADC na jihar Dr. Mustapha Inuwa tare da Alhaji Atiku Abukakar G.C.O.N tsohon Mataimakin Shugaban Kasa abaya. Kuma Wanda yayi Takarar shuganxhin kasa karo daban daban a garin Daura acikin jihar Katsina.

Wajen ta'aziyyar rasuwar tsohon shugaban kasar Najeriya Muhammadu Buhari.

Allah Ya jikansa da Rahama

Jigo  kuma uba a jam'iyyar P.D.P Alhaji Kabir Yusuf safana, ya bayyana ficewarsa a jam'iyyar ta P.D.P tare da magoya bay...
19/07/2025

Jigo kuma uba a jam'iyyar P.D.P Alhaji Kabir Yusuf safana, ya bayyana ficewarsa a jam'iyyar ta P.D.P tare da magoya bayanshi Baki daya tare da ayyana komawar su sabuwar tafiyar hadaka ta jam'iyyar African democratic party (A.D.C)., ya kuma yi Kira ga daukacin al'ummar karamar hukumar safana da jihar katsina dama Nigeria baki daya da mu dage da addu'ar Allah ya kawo mamu zaman lafiya. Amin

Sanata Henry Seriake Dickson yace; A jiya na bi sahun takwarorina wajen halartar wani taron bita na kwamitocin hadin gwi...
19/07/2025

Sanata Henry Seriake Dickson yace; A jiya na bi sahun takwarorina wajen halartar wani taron bita na kwamitocin hadin gwiwa na Majalisar Dokoki kan Ilimi, inda muka tattauna kan kalubalen da ke tattare da ilimin firamare, musamman kan batun gyara da aka yi wa dokar karatun UBE.

Kamar yadda kowa ya sani, na sha bayyana ra’ayi na a zauren majalisar dattijai so da dama kan bukatar karfafa ilimin boko da rage adadin yaran da ba sa zuwa makaranta a kasar nan.

Har ila yau, na jaddada bukatar tattaunawa kan hanyoyin karfafawa da bunkasa iyawa ta fuskar neman ilimin harsuna, al'adu, da wayewar da ke da muhimmanci wajen fadada tunanin 'yan Nijeriya.

Saboda haka, na yi magana ne na goyon bayan ilimin Larabci ko Addinin Musulunci ga Musulmi, wadanda su ne babban tushen albarkatun kasa, da kuma ilimin Faransanci, a matsayinsa na guda daga cikin harsunan da ake koyarwa a kasa, ya kamata a karfafa, inganta su kamar yadda ake yiwa karatun Boko.

Zai kasance cikin maslahar ƙasarmu mu wadata yaran ƙasar nan da ilimin harsuna, al'adu, da wayewa gwargwadon iko don shirya su don yin gogayya da takwarorinsu na duniya.

Kamar yadda nake fada a kowane dandali, saka hannun jari a fannin ilimi ya kamata ya zama babban fifiko ga kowa a cikin gwamnati - shugaban kasa ko gwamna, kamar yadda na yi a matsayin Gwamna na tsawon shekaru takwas, ko da a lokacin koma bayan tattalin arziki, ba'a dakatar da tsare-tsaren ilimi, fannin ilimi yana bukatar a kara karfafa shi, tare da mai da hankali kan inganta cibiyoyi da tsari mai kyau na ilmantar da malamai, da kuma samar da manufofi masu kyau wajen zuba kudade domin tallafawa ilimin.

MURNA: Fitaccen Mawakin Siyasa A Najeriya Alhaji Dauda Kahutu Rarara, Ya Samarwa Daya Daga Cikin Masu Taimaka Mashi A Ka...
19/07/2025

MURNA: Fitaccen Mawakin Siyasa A Najeriya Alhaji Dauda Kahutu Rarara, Ya Samarwa Daya Daga Cikin Masu Taimaka Mashi A Kafafen Sadarwa Zamani (Social Media) Malam Mubarak Dabai Mukami Na (Senior Legislative Aide)

A Ofishin Kakakin Majalisar Wakilai Hon. Tajuddeen Abbas.

Allah Ya Sanya Alkhairi, Ya Allah Ya Taimaki Matasan Najeriya!

Karaduwa Post

Shugaban Kasa Bola Tinubu Ya Amince Da Naɗa Babban Ɗan Tsohon Shugaban Kasa Na Mulkin Soja, Muhammad Ibrahim Badamasi Ba...
18/07/2025

Shugaban Kasa Bola Tinubu Ya Amince Da Naɗa Babban Ɗan Tsohon Shugaban Kasa Na Mulkin Soja, Muhammad Ibrahim Badamasi Babangida A Matsayin Shugaban Hukumar Gudanarwar Bankin Manoma Na Najeriya

Allah Ya Taya Riƙo!

DA DUMI DUMI: jiya Al'ummar jihar Kano Sunyi Kwanan farin ciki Saboda Zuwan Shugaban ƙasa Bola Tinubu jihar Kano, inji f...
18/07/2025

DA DUMI DUMI: jiya Al'ummar jihar Kano Sunyi Kwanan farin ciki Saboda Zuwan Shugaban ƙasa Bola Tinubu jihar Kano, inji fadar shugaban ƙasa

Tun jiya Mutane a jihar Kano S**a kasayin Bacci Saboda Sunji Sanarwar cewa Bola Tinubu Zai shiga jihar Kano a Yau juma'a

Ɗan Takarar Sanatan Shiyyar Katsina A Zaɓen Da Ya Gabata, Alhaji Surajo Aminu Makera Ya Fice Daga Jam'iyyar PDP Zuwa Jam...
18/07/2025

Ɗan Takarar Sanatan Shiyyar Katsina A Zaɓen Da Ya Gabata, Alhaji Surajo Aminu Makera Ya Fice Daga Jam'iyyar PDP Zuwa Jam'iyyar Haɗaka Ta ADC A Katsina

An gudanar da taron addu'o'i ga tsohon shugaban Najeriya, marigayi Muhammadu Buhari a taron majalisar zartaswa a fadar s...
17/07/2025

An gudanar da taron addu'o'i ga tsohon shugaban Najeriya, marigayi Muhammadu Buhari a taron majalisar zartaswa a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Shugaba Bola Tinubu ne ya jagoranci taron addu'o'in kuma taron ya samu halarcin iyalan marigayin da ministoci da sauran manyan ‘yan siyasa a Najeriya.

📸 - Gwamnatin Najeriya

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zamani Media Crew posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zamani Media Crew:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share