29/10/2025
Jonathan ya dakatar da cire tallafin fetur ne saboda tsoron Boko Haram za su iya kai wa masu zanga-zanga hari - Sanusi
Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya bayyana cewa tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya dakatar da shirin cire tallafin fetur a shekarar 2012 saboda tsoron cewa ‘yan ta’addan Boko Haram za su kai hari kan masu zanga-zangar.
Zanga-zangar kasa da aka yi a lokacin ta ɗauki kusan makonni biyu, inda ta durkusar da harkokin tattalin arziki a fadin ƙasar.
TheCable ta rawaito cewa Sanusi, wanda shi ne Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN) a wancan lokaci, ya ce an yi kuskuren fahimtar manufar cire tallafin da kuma yadda aka tafiyar da ita a lokacin gwamnatin Jonathan.
Ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin taron Oxford Global Think Tank Leadership Conference mai taken “Better Leader for a Better Nigeria.”
A cewar Sarkin, tsarin tallafin fetur na Najeriya a wancan lokaci ya kasance tamkar “naked hedge” — wato gwamnati ce ke ɗaukar nauyin tabbatar da farashin fetur bai canza ba, komai sauyin farashin man duniya, canjin kudin waje ko ribar bashi.
Ya ce wannan tsari ya tilasta wa gwamnati ta rika karɓar bashin kuɗi masu yawa, ba wai kawai don biyan tallafin ba, har ma don biyan ribar bashin da aka ɗauka don tallafin.
"dan ka kalli tsarin, duk waɗannan kuɗaɗen gwamnati ce ke ɗaukar su. Gwamnati ta kasa ta ɗauki matsayin cewa tana da aljihun da ba ya ƙarewa,” in ji Sanusi.
"Sai muka fara daga lokacin da ake amfani da kudaden shiga wajen biyan tallafi, zuwa lokacin da ake karɓar bashi don biyan tallafi, sannan daga baya muka fara karɓar bashi don biyan ribar bashin da aka ɗauka don tallafin. Wannan ya kai mu ga halin rashin kuɗi (bankruptcy).”