28/08/2026
2027: Zan magance matsalar tsaro cikin shekara guda idan na zama shugaban ƙasa - Atiku
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya yi alkawarin kawo karshen matsalar rashin tsaro a Najeriya cikin shekara guda idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa a zaben 2027.
Tsohon mataimakin shugaban kasar ya bayyana hakan ne a wata hira da BBC Hausa, inda ya ce gwamnatinsa za ta dauki matakan gaggawa domin magance matsalar tsaro da kuma rage yawan matasa da ke shiga aikata laifuka.
Atiku ya ce zai kara yawan jami’an tsaro tare da samar musu da kayan aiki da isasshen kudin gudanar da ayyukansu.
Ya kuma ce gwamnatinsa za ta samar da tallafi ga matasa domin su kafa sana’o’i da kasuwanci, yana mai cewa rashin aikin yi na daga cikin abubuwan da ke jefa wasu matasa cikin aikata laifuka.
“Ba zan dauki fiye da shekara guda ba wajen kawo karshen wannan matsala. Za mu dauki matakan da s**a dace kuma cikin shekara guda za mu kawo karshen rashin tsaro, in Allah ya yarda,” in ji Atiku.
Dan takarar ya kuma bayyana shirin sa na tattaunawa da shugabannin Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) domin farfado da rundunar ECOMOG da kuma kara hadin gwiwar sojojin kasashen yankin.
Ya ce Najeriya za ta iya hada karfi da kasashen Côte d’Ivoire, Saliyo da Laberiya wajen yaki da matsalar tsaro da dawo da zaman lafiya a yankin.
Atiku ya kuma ce bai kamata juyin mulkin da sojoji s**a yi a Nijar ya zama dalilin da zai sa Najeriya ta katse alakar diplomasiyya da kasar ba.
Ya jaddada cewa Najeriya da Nijar suna da dadadden alaka, tare da cewa al’ummomin kasashen biyu suna da kusanci sosai.
Ya kuma yi alkawarin kokarin dawo da Nijar, Burkina Faso da Mali cikin ECOWAS domin samar da hadin kai tsakanin kasashen yankin da kuma taimakawa wajen rage rashin aikin yi.
Daily Nigeria Hausa