Zamani Media Crew

Zamani Media Crew News
Reports
Enlightenment
Entertainment
Photos Videos Editing
Adverts
Documentary
Film Making etc Some Information

Yanzu-yanzu: An naɗa sabon Surveyor General a Katsina. Gwamna Dikko Radda ya naɗa Surv. Saifullahi Umar Masanawa a matsa...
05/11/2025

Yanzu-yanzu: An naɗa sabon Surveyor General a Katsina.

Gwamna Dikko Radda ya naɗa Surv. Saifullahi Umar Masanawa a matsayin sabon Surveyor General na jiha.

Sanarwar ta fito daga ofishin shugaban ma'aikatan gwamnatin jihar Katsina, Alhaji Falalu Bawale inda ya bayyana Surv. Saifullahi a matsayin kwararren a harkar safiyo da kuma tsare-tsare.

Allah yasa a fara a saa ya kuma sa ya zamo alheri ga jihar Katsina.

MS Ingawa
SSA Media and Strategy
Katsina State Government
November 5, 2025

DA ƊUMI-ƊUMI: China ta maida wa Amurka martani kana barazanar da ta yi wa Nijeriya Gwamnatin kasar China ta fitar da gar...
04/11/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: China ta maida wa Amurka martani kana barazanar da ta yi wa Nijeriya

Gwamnatin kasar China ta fitar da gargadi mai karfi kan duk wani yunkuri na tsoma baki cikin harkokin cikin gida na Najeriya, bayan kalaman da shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi na barazanar kai hari da sojoji a Najeriya bisa zargin cin zarafin Kiristoci.

Da take jawabi a wajen taron manema labarai a ranar Talata, Mao Ning, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar China, ta bayyana cewa, Beijing “na goyon bayan gwamnatin Shugaba Bola Tinubu gaba ɗaya yayin da take jagorantar al’ummar Najeriya kan tafarkin ci gaba da ya dace da halin ƙasar.”

“China, a matsayinta na abokiyar haɗin gwiwar Najeriya, tana adawa da duk wata ƙasa da ke amfani da addini ko kare haƙƙin ɗan adam a matsayin hujja don tsoma baki cikin harkokin cikin gida na wata ƙasa ko yin barazanar sanya mata takunkumi ko amfani da ƙarfi,” in ji Mao.

Wadannan kalamai sun biyo bayan martanin ƙasashen duniya kan maganganun Trump da ke haifar da damuwa a diflomasiyya a fadin nahiyar Afirka da ma sauran sassan duniya.

Yadda Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II da mai dakinsa, Hajiya Sadiya Ado Bayero (Giwa Sarkin Kano) s**a gudanar da...
02/11/2025

Yadda Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II da mai dakinsa, Hajiya Sadiya Ado Bayero (Giwa Sarkin Kano) s**a gudanar da bikin cika shekaru 40 da aure.

📸: Jameela Faruk Jamo

Shugaban kamfanin tafiye-tafiye na Zam-Zam Travels & Tours Limited, Alhaji Ghali A. Bello ya rasu.Mun samu rahoton cewa ...
30/10/2025

Shugaban kamfanin tafiye-tafiye na Zam-Zam Travels & Tours Limited, Alhaji Ghali A. Bello ya rasu.

Mun samu rahoton cewa Ghali ya rasu ne sakamakon hàďarin mota akan hanyar zuwa filin jirgin sama na Nnamdi Azikwe da ke Abuja domin tafiya Saudi Arebiya don gudanar da ibadar Umrah.

Allah Ya gafarta masa, Ya kyauta namu zuwan.

An dakatar da shugabar malamai a makarantar firamare bisa bada damar a yi taron siyasa a Anambra An dakatar da shugabar ...
30/10/2025

An dakatar da shugabar malamai a makarantar firamare bisa bada damar a yi taron siyasa a Anambra

An dakatar da shugabar makarantar firamare a ƙaramar hukumar Orumba ta Kudu ta jihar Anambra saboda ta bari an gudanar da taron siyasa a cikin makarantar.

Kwamishiniyar Ilimi ta jihar, Farfesa Ngozi Chuma-Udeh, ce ta bayar da wannan umarni a cikin wata sanarwa da ma'aikatar ta fitar a jiya Laraba a Awka.

Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa ya ruwaito cewa Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Anambra ta fitar da wata sanarwa a ranar 14 ga watan Agusta, inda ta haramta amfani da filayen makarantu don tarurukan siyasa, bikin aure ko addini.

Sai dai kuma Chuma-Udeh ta bayyana cewa an samu shugabar makarantar, Umunze da laifin karya dokar ma’aikatar da ta hana duk wani taro ba tare da izini ba a makarantu.

Ta nuna damuwa kan yadda wannan taron ya katse harkokin karatu da kuma haɗarin da aka jefa ɗalibai a ciki yayin taron.

“Gwamnatin jihar na shirin ɗaukar matakin shari’a kan wadanda su ka shirya wannan taro, wanda ya kawo cikas ga koyarwa kuma ya jefa rayuwar yara cikin haɗari,” in ji Chuma-Udeh.

Rahoton da ke iske mu yanzu na nuni da cewa ana zargin wasu ɓatagari da kashe kwamandan kwamitin kar-ta-kwana kan yaƙi d...
29/10/2025

Rahoton da ke iske mu yanzu na nuni da cewa ana zargin wasu ɓatagari da kashe kwamandan kwamitin kar-ta-kwana kan yaƙi da ƙwacen waya na jihar Kano (Anti Phone Snatching', Inuwa Salisu Sharada a gidan sa.

Allah Ya gafarta masa.

Ƙarin bayani na nan tafe...

Daily Nigerian Hausa

Jonathan ya dakatar da cire tallafin fetur ne saboda tsoron Boko Haram za su iya kai wa masu zanga-zanga hari - Sanusi S...
29/10/2025

Jonathan ya dakatar da cire tallafin fetur ne saboda tsoron Boko Haram za su iya kai wa masu zanga-zanga hari - Sanusi

Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya bayyana cewa tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya dakatar da shirin cire tallafin fetur a shekarar 2012 saboda tsoron cewa ‘yan ta’addan Boko Haram za su kai hari kan masu zanga-zangar.

Zanga-zangar kasa da aka yi a lokacin ta ɗauki kusan makonni biyu, inda ta durkusar da harkokin tattalin arziki a fadin ƙasar.

TheCable ta rawaito cewa Sanusi, wanda shi ne Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN) a wancan lokaci, ya ce an yi kuskuren fahimtar manufar cire tallafin da kuma yadda aka tafiyar da ita a lokacin gwamnatin Jonathan.

Ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin taron Oxford Global Think Tank Leadership Conference mai taken “Better Leader for a Better Nigeria.”

A cewar Sarkin, tsarin tallafin fetur na Najeriya a wancan lokaci ya kasance tamkar “naked hedge” — wato gwamnati ce ke ɗaukar nauyin tabbatar da farashin fetur bai canza ba, komai sauyin farashin man duniya, canjin kudin waje ko ribar bashi.

Ya ce wannan tsari ya tilasta wa gwamnati ta rika karɓar bashin kuɗi masu yawa, ba wai kawai don biyan tallafin ba, har ma don biyan ribar bashin da aka ɗauka don tallafin.

"dan ka kalli tsarin, duk waɗannan kuɗaɗen gwamnati ce ke ɗaukar su. Gwamnati ta kasa ta ɗauki matsayin cewa tana da aljihun da ba ya ƙarewa,” in ji Sanusi.

"Sai muka fara daga lokacin da ake amfani da kudaden shiga wajen biyan tallafi, zuwa lokacin da ake karɓar bashi don biyan tallafi, sannan daga baya muka fara karɓar bashi don biyan ribar bashin da aka ɗauka don tallafin. Wannan ya kai mu ga halin rashin kuɗi (bankruptcy).”

Sabbin Hafsoshin Tsaro sun gana da Ministan tsaro, BadaruMinistan Tsaro na ƙasa, Mohammed Badaru Abubakar ya karɓi sabbi...
28/10/2025

Sabbin Hafsoshin Tsaro sun gana da Ministan tsaro, Badaru

Ministan Tsaro na ƙasa, Mohammed Badaru Abubakar ya karɓi sabbin shugabannin rundunonin tsaro na ƙasa a ofishin sa a yau Talata a Abuja.

Cikin waɗanda s**a halarta akwai Babban Hafsan Tsaro, Laftanar Janar OO Oluyede; Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, Mejar Janar W. Shaibu; Babban Hafsan Sojojin Ruwa, Rear Admiral I. Abbas; da Babban Hafsan Sojojin Sama, Air Vice Marshal S. K. Aneke.

Hadimin Ministan Safwan Sani Imam ya ce Ziyarar ta nuna kudirin Ministan na ƙarfafa haɗin kai da haɗin gwiwa tsakanin rundunonin tsaro domin kare martabar ƙasar da tabbatar da tsaron iyakokinta, bisa jagorancin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

An rufe kotuna a Kaduna yayin da ma’aikatan shari’a s**a fara yajin aikiAn rufe dukkan kotunan jihar Kaduna  a ranar Lit...
27/10/2025

An rufe kotuna a Kaduna yayin da ma’aikatan shari’a s**a fara yajin aiki

An rufe dukkan kotunan jihar Kaduna a ranar Litinin bayan kungiyar ma’aikatan shari’a ta Najeriya (JUSUN) ta fara yajin aiki na sai baba-ta-gani domin neman aiwatar da cikakken baiwa ɓangaren Shari'a ƴancin biyan albashi ga ma'aikatan ta da wasu buƙatu na albashi.

JUSUN ta ce matakin ya biyo bayan gazawar gwamnatin jihar wajen amsa wasikun korafi da ƙungiyar ta aike tun daga watan Satumba.

Bayanan sun nuna cewa kotunan jiha da na tarayya da Shari’a, da na al’ada duk an rufe, yayin da wasu ma’aikata ke taimakawa jama’a wajen samun takardun rantsuwa a wajen kotuna.

Ƙungiyar ta lissafo bukatunta da s**a haɗa da biyan bashin albashi da gyaran matakan albashi, da kuma biyan kudaden hutu da sufuri da s**a taru tun daga 2016.

An ce an yanke shawarar fara yajin aikin ne bayan taron gaggawa da JUSUN ta gudanar a ranar 13 ga Oktoba.

Dalilin da ya sa mu ka soke batun auren Mai Wushirya da Ƴarguda - Hisbah Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa ta...
26/10/2025

Dalilin da ya sa mu ka soke batun auren Mai Wushirya da Ƴarguda - Hisbah

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa ta soke batun auren jarumin Tiktok din nan Ashiru Idris Mai Wushirya da Abashiyya Yarguda bayan sun tabbatar da cewa babu soyayya a tsakanin su.

Idan za a iya tunawa dai a kwanakin baya ne, wata kotun Majistiri ta umarci hukumar Hisbah ta shirya kan auren jaruman biyu bayan an same su da laifin wallafa hotuna da bidiyoyi na badala.

Sai dai, a wata sanarwa da mataimakin Babban Kwamandan hukumar Hisbah ta jihar Kano, Dakta Mujahideen Aminudeen ya aiko wa jaridar Daily Nigerian Hausa ya bayyana cewa bayan an gudanar da gwaje-gwaje, Mai Wushirya da 'Yar Guda sun tabbatar wa da hukumar cewa "Content Creation" kawai suke yi ba wai soyayya ba.

Acewar Dakta Mujahideen, daman sharadi ne a addini cewa sai Amarya da Ango sun amince da junansu kafin a kai ga daura aure.

"Tun kafin a zo maganar Sadaki ma, s**a nuna gaskiya baza su iya ba, mai girma babban kwamanda ya yi la'akari da cewa, a Musulunci Shari'a ake karewa , kuma a shari'a ba a auren dole".

Ya kara da cewa tunda ba soyayya tsakanin Haruna Tiktok din kuma na akwai bambancin halitta tsakanin su, to ta tabbata cewa za a iya rasa wannan batu na aure domin za a iya samun matsaloli bayan auren.

"Mu kuma a Hisbah, so mu ke yi aure ya zama mutu-ka-raba, ba wai a rika samun matsaloli har ta kai ga cin zarafi ba," innji Dakta Mujahideen

Haka kuma, ya ce Hisbah za ta mayar da su gaban kotu domin daukar mataki na gaba.

Mallamawan Katsina Hakimin Ɓatagarawa Alhaji Muhammad Dalhatu Dikko ya nada manyan mutane 31 sarautu daban-daban Mallama...
26/10/2025

Mallamawan Katsina Hakimin Ɓatagarawa Alhaji Muhammad Dalhatu Dikko ya nada manyan mutane 31 sarautu daban-daban

Mallamawan Katsina Hakimin Ɓatagarawa Alhaji Muhammad Dalhatu Dikko ya naɗa manyan mutane maza da mata mutum 31 a sarautu daban-daban, saboda irin gudunmawar da suke bayar wa ga ci gaban ƙaramar hukumar.

Daga cikin wadanda aka naɗa akwai Dakta Habibu Ɗanɗagoro a matsayin Matawallen Mallamawan Katsina, Shugaban Ƙaramar Hukumar Ɓatagarawa Hon. Yahaya Lawal Kawo a matsayin Ci garin Mallamawan Katsina da Matarsa Hajiya Aisha a matsayin Uwar Marayun Mallamawan Katsina, da kuma Babangida Sani Ƙwa Dallatun Mallamawan Katsina da sauran su.

A jawabin sa, Gwamnan jihar Malam Dikko Umaru Raɗɗa wanda ya samu wakilcin Mataimakin sa Alhaji Faruk Lawal Joɓe ya bayyana cewa akan rokon da aka yi na taimakawa wajen kawo ƙarshen matsalar zaizaiyar ƙasa, yace tuni Gwamnati ta dauƙi mataki domin magance hakan.

Alhaji Faruk Lawal Joɓe wanda ya samu wakilcin Babban Sakataren Ofishin Malam Mannir Aliyu, yace gwamnatin mai ci tuni ta ɓullo da shirin baiwa al'umma damar su fadi abinda suke so gwamnati ta yi masu.

Ya bayyana cewa, gwamnati za ta ƙara ƙaimi domin ganin kowane yanki na jihar ya ci gaba, domin tabbatar da dai-dai to da raba dai-dai na dukiyar al'umma.

Ya taya su murna kan sarautar da s**a samu , sai ya yi kira a gare su da su yi amfani da damar wajen ciyar da yankunan su da alummomin su a matakin gaba.

A nashi jawabin, Mallamawan Katsina Hakimin Ɓatagarawa Alhaji Muhammad Dikko ya ce masarautar ta zaɓo su tare da basu sarautar kasancewar irin gudunmawar da suke bayar wa ga cigaban al'umma.

A cewar sa, Ƙaramar Hukumar ta samu gagarumin ci gaba da s**a haɗa da samun jami'ar Umaru Musa Yar'adua da Asibitin Ƙashi da hanyoyi da masana'antu da sauran su.

Yanzu Haka!Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umaru Raɗɗa, PhD,CON, yana jagorantar muhimmin taro akan tsaro a gidan gwam...
24/10/2025

Yanzu Haka!

Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umaru Raɗɗa, PhD,CON, yana jagorantar muhimmin taro akan tsaro a gidan gwamnati domin nazarin halin tsaron jihar da kuma ci gaban ayyukan jami’an tsaro a yankunan da abin ya shafa.

Shugabannin hukumomin tsaro wanda s**a haɗa da Sojoji, Sojan Sama ƴan Sanda, jami'an tsaron farin kaya DSS, jami'an hukumar shige da fice, sai manyan jami’an gwamnati, da kuma shugabannin ƙananan hukumomi na yankunan da ake fama da matsalar tsaro.

Hakazalika, manyan malaman addini da wakilan masarautu na Katsina da Daura sun halarci taron, don ƙara haɗa kai da al’umma wajen magance matsalolin tsaro.

Taron ya mayar da hankali ne kan ci gaba da fatattakar ƴan ta’adda, ƙarfafa haɗin guiwa tsakanin jami’an tsaro, inganta tattara bayanan sirri, da ƙarfafa rawar da al’umma zasu taka wajen magance matsalar

Ana sa ran Gwamna Raɗɗa zai fitar da sabbin matakai domin tabbatar da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyoyin al'umma a faɗin jihar.

Address

Rong Rod
Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zamani Media Crew posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zamani Media Crew:

Share