Zamani Media Crew

Zamani Media Crew News
Reports
Enlightenment
Entertainment
Photos Videos Editing
Adverts
Documentary
Film Making etc Some Information

Tinubu na Shirin fara hutun makonni Uku a TuraiShugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu zai bar Abuja a yau, Lahadi, domin fa...
30/08/2026

Tinubu na Shirin fara hutun makonni Uku a Turai

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu zai bar Abuja a yau, Lahadi, domin fara hutun shekara na tsawon makonni uku a Turai, inda birnin Landan na Birtaniya zai kasance zangonsa na farko.

Mai bai wa shugaban kasa shawara na musamman kan yada labarai, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar.

Sanarwar ta ce Tinubu zai koma Najeriya bayan kammala hutun, domin ci gaba da ayyukansa da kuma shirye-shiryen yakin neman zabensa na watan Janairun 2027.

Sashen Tallace Tallacen kamfaninn Zamani Media Crew.Wani labari ne mai taken: "Wata Jarumar Mace ta Kaddamar da Yakin Ne...
29/08/2026

Sashen Tallace Tallacen kamfaninn Zamani Media Crew.

Wani labari ne mai taken: "Wata Jarumar Mace ta Kaddamar da Yakin Neman Zabe a matsayin Kodinetan Matasa a Jihar Katsina."

Duba da yadda ake fadi-tashin ganin mata sun shiga harkar siyasa, gari ya waye da wani labari mai dadi ga mazauna Jihar Katsina, musamman ma matasa da mata, ganin cewa wata gimbiyar matashiya ta fito takarar zama Kodinetar matasa ta jahar Katsina State.

A wani jawabi da ta gabatar inda take zantawa da wakilinmu na kamfanin zamni media, ta bayyana cewa burinta shi ne ta bada tata gudunmuwar da matasa da mata ta hanyar samar da hanyoyin da za su kawo cigaba a cikin matasan.

A karshe, ta bayyana cewa tana matukar bukatar goyon bayan 'yan uwa matasa da ma dukkanin mutanen Jihar Katsina domin ta samu nasarar tafiyar da wannan karagar mulki yadda ya kamata, idan Allah yabata.

Yadda Gwamnan jihar Katsina, Dr Mustapha Inuwa, Dahiru Mangal, Arch Ahmad Musa Dangiwa s**a gana da mataimakin Shugaban ...
29/08/2026

Yadda Gwamnan jihar Katsina, Dr Mustapha Inuwa, Dahiru Mangal, Arch Ahmad Musa Dangiwa s**a gana da mataimakin Shugaban Kasa a Abuja

Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, Dakta Mustapha Inuwa Tare Da Ɗan Takarar Gwamnan Jihar Katsina A Ƙarƙashin Jam...
28/08/2026

Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, Dakta Mustapha Inuwa Tare Da Ɗan Takarar Gwamnan Jihar Katsina A Ƙarƙashin Jam'iyyar PDP, Sanata Yakubu Lado Ɗanmarke A Filin Jirgin Saman Abuja Yau Juma'a

2027: Zan magance matsalar tsaro cikin shekara guda idan na zama shugaban ƙasa - Atiku Dan takarar shugaban kasa na jam’...
28/08/2026

2027: Zan magance matsalar tsaro cikin shekara guda idan na zama shugaban ƙasa - Atiku

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya yi alkawarin kawo karshen matsalar rashin tsaro a Najeriya cikin shekara guda idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa a zaben 2027.

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya bayyana hakan ne a wata hira da BBC Hausa, inda ya ce gwamnatinsa za ta dauki matakan gaggawa domin magance matsalar tsaro da kuma rage yawan matasa da ke shiga aikata laifuka.

Atiku ya ce zai kara yawan jami’an tsaro tare da samar musu da kayan aiki da isasshen kudin gudanar da ayyukansu.

Ya kuma ce gwamnatinsa za ta samar da tallafi ga matasa domin su kafa sana’o’i da kasuwanci, yana mai cewa rashin aikin yi na daga cikin abubuwan da ke jefa wasu matasa cikin aikata laifuka.

“Ba zan dauki fiye da shekara guda ba wajen kawo karshen wannan matsala. Za mu dauki matakan da s**a dace kuma cikin shekara guda za mu kawo karshen rashin tsaro, in Allah ya yarda,” in ji Atiku.

Dan takarar ya kuma bayyana shirin sa na tattaunawa da shugabannin Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) domin farfado da rundunar ECOMOG da kuma kara hadin gwiwar sojojin kasashen yankin.

Ya ce Najeriya za ta iya hada karfi da kasashen Côte d’Ivoire, Saliyo da Laberiya wajen yaki da matsalar tsaro da dawo da zaman lafiya a yankin.

Atiku ya kuma ce bai kamata juyin mulkin da sojoji s**a yi a Nijar ya zama dalilin da zai sa Najeriya ta katse alakar diplomasiyya da kasar ba.

Ya jaddada cewa Najeriya da Nijar suna da dadadden alaka, tare da cewa al’ummomin kasashen biyu suna da kusanci sosai.

Ya kuma yi alkawarin kokarin dawo da Nijar, Burkina Faso da Mali cikin ECOWAS domin samar da hadin kai tsakanin kasashen yankin da kuma taimakawa wajen rage rashin aikin yi.

Daily Nigeria Hausa

25/08/2026

Kai tsaye daga garin Kafin-Soli. Wajen Taron yima Alhaji Suleiman Garba Kafin-Soli murnar shigiwa APC Daga Jamma'iyar ADC

25/08/2026

Jawabin daga bakin Wanda daukacin Al'ummar gari ke Tayawa murnar dawowarshi APC a ward din Kafin-Soli

25/08/2026

DUK a Garin Kafin-Soli inda s**ayi mubayi'a a Jamma'iyar APC daga ADC

25/08/2026

Address

Rong Rod
Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zamani Media Crew posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zamani Media Crew:

Shortcuts

Share