Akuuu

Akuuu Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Akuuu, Media/News Company, Yammama, Katsina.

25/06/2023

JIYA BA YAU BA...

Nan fa wasu mutane ne, yayin da su ke ginin rumbu, a garin Toro Dake Jahar Bauchi cikin shekarar 1964.

Allah ya jikan Magabatan mu.

18/05/2023

Sarkin Katsina Muhammad Dikko da tawagarsa Cikin Shekarar 1930. Yayi Sarautar Katsina da ga Shekarar 1906 Zuwa 1944.

Allah Ya Jiƙan magabatanmu

16/05/2023

Shekaru 32 da s**a wuce.

Sheikh Muhammad Kabiru Haruna Gombe kenan Allah yakara rufa asiri, Allah yayi jagora. Ameen.

16/05/2023

Ɗaliban A.B.U. Zariya A Lokacin Zanga-Zangar Adawa Da Juyin Mulkin Farko Da Sojoji S**a Yi. Wanda Aka Kashe Su Sardauna, Da Tafawa Balewa Da Samuel Akintola Da Sauran Su, A Ranar 15 Ga Watan Junairu 1966.

Allah ya jiƙan magabatanmu

16/05/2023

Yadda kwankwaso ya kwashe sa'o i tareda Tunubu a kasar Paris Suna ganawar sirri.

29/04/2023

Labarin Sheikh Ibrahim Inyass Da Wani Barawo.

Watarana Wani Barawo Ya Shiga Gidan Sheikh Ibrahim Inyass (R.A) Yayi Sata

Sai Dai Kash! An K**a Shi, Aka Kai Shi Wajen Shehu (R.A).

Sai Shehu Ya Tambayi Wannan Barawo Kaine Ka Shigo Gida Na?

Sai Barawo Yace:"Eh"

Shehu Yace:"Yaya Sunanka?

Sai Barawo Yace Sunana "MUHAMMADU!"
Nan Da Nan Sai Shehu Yace:"Sunanka
Kenan?

Sai Barawo Yace: "Eh Wallahi Hakane Sunana".

Cikin Mamaki Sai Shehu Yace:"Ai Kai Ba Barawo Bane, Dama Kayan kane Komai Na Gidan Nan Nakane",

Sai Shehu Ibrahim Inyass (R.A) Yasa Aka
Dinga Kwaso Kaya Da Kudi Ana Ta Tarawa Wannan Mutumin, Saboda Kawai Sunan Shi 'MUHAMMADU'.

Allahu Akbar! Shehu Mai ANNABI (S.A.W.) Kenan, Kuma Dama Dabi'arsa Ce Duk Inda A kace ANNABI (S.A.W.), Tofa Indai Shehu Yana Wajen Yanzu Zaka ga Gashin Jikinsa Na Mikewa.

Wasu Muridansa Wanda S**a Zauna Dashi Sunce, Shehu a Koda Yaushe Gashin Jikinsa Baya Kwanciya Saboda Shauki Da Soyayyarsa Ga ANNABI (S.A.W.) Duk Inda Yaga Mai Suna 'MUHAMMADU', Sai Ya Girmama Shi Ya Kuma Bashi Hadiya.

“Source” Fityanul Islam Of Nigeria.

26/04/2023

Sun Zagi Mahaifina, Sun Kone Mun Gida – Rarara Ya Kai Karar 'Yan Kwankwasiyya Wajen Tinubu

26/04/2023

KIN TABA TAMBAYAR SAURAYI BAYAN KA GAMA ZINA DA NI KA KAWO RUWA YA KAKE JI NA A RANKA?

To bari in amsa miki domin bazaki san komaiba injira kk shi ya amsa miki, a duk sanda namiji ya kawo ruwa da abokiyar lalarta ita tana murna tana jin dadin ta faranta masa rai, a tunaninta ai yanzu nasamu wani karin kusanci a zuciyarsa.

Ayya! Kin makara, domin shi da yakawo ruwa babu abinda yake bukata irin ki barshi yayi bacci, ko kwayan zarra na soyayyarki babu ita a zuciyansa a wannan lokaci, domin dama abinda yake nufi da yana sonki yana sha'awankine, kuma ya saukar da sha'awarshi a jikinki yanzu zai lallabeki ya daura ki a machine ki bar dakinsa a lokacinda ke bakiyi niyyan komawaba, hasalima kina son kasancewa da shi a wannan lokacin domin ke kinriga kingama yi masa mafi girman soyayya shi kuma kin gama amfani a wurinsa, zai ce dan Allah ki tafi zamu karasa a charting.

Yana fada miki cewa shi yana da ciwon sha'awa ko sha'awa ta mai yawa ko yayi azumi baya sauka? Formal tactics kenan na 99.9% na maza wurin yaudara da lalata muku rayuwa.

Babu wanda bashi da sha'awa saidai shi sha'awace abokiyar hirarsa, shi kadai ba zuciya labarin sha'awa, da abokai maganar sha'awa, da budurwa a charting maganar sha'awa, a kofar gidanku maganar sha'awa, sannan yace miki soyayya tana bukatar sirri ke kuma da shike baki da mafada kin rasa dattijai, ko kin iya yaudarar iyaye da sunan zuwa islamiyya, hadda, kitso, kawata ta kirani, an yadda da ke an baki dama kin wuce wurin dan iskanki. Tirrr

Nawa ake biyanki? Shine sadakin aurenki ko ladan iskanci? Me zaki saya da shi? Halal ko haram?

Namiji fasiki baya fatan ki gyara shi kullum gaba ta kaishi, wani ko sisi be biya ki hau machine ki biyoshi ya biya bukatarshi, ki tura mishi Kati, ki bashi kudi, kiyi mai girki, kuma ya debeki banza a matsayin banza, wallahi ba soyayya bace azabtar da ke Allah yakeyi da fasiki saboda wani na can yana son ki da aure kina nan kina ba dan iska kanki sadaka fi sabilisshaitan. Sunan dayawa Kuma wlh maza

Ya Allah ya Ubangiji ka tsaremu ka tsaremamu Yan uwan mu da Duk Kanin musulmi

Dr-Nuraddeen Katsiana
08068962793

26/04/2023

Majalissa muke jira ta amince mu rabawa talakawa dubu biyar biyar na ​​cire tallafin man fetur - Zainab Ahmed

26/04/2023
26/04/2023

SANARWAR GAGGAWA GA MATAFIYA MASU BIN HANYAR JOS

Yanzu haka masu rikicin kabilanci na tare hanyar Jos zuwa Abuja da hanyar barikin Ladi zuwa Jos, ana sanar da duk masu bin wa 'yan nan hanyoyin da su kiyaye bin hanyar a yau.

Muna bukatan a yada (Sharing) domin sakon ya isa ga masu bin hanyar. Allah ya kare 'yan uwanmu daga sharrin su. Amin

26/04/2023

Barka
DA
juma.ar

26/04/2023

Wannan itace babbar hanyar zuwa masallacin Manzon Allah s.a.w dake birnin madina. ❤️

Allah yaba kowa ikon zuwa wannan wurin ameen

23/05/2022
23/05/2022

BABBAN MAGANA: Masana sun ce wani makeken dutse da yafi komi girma ya taho a guje zai wuce ta saman duniya ranar Juma'a mai zuwa

Daga Muryoyi

Masana sararin samaniya sunyi hasashen cewa wani makeken dutse da yafi komi tsawo da girma a duniya zai wuce ta saman duniya (Earth) a ranar Juma'a mai zuwa.

Masana sunyi hasashen girman dutsen mai suna 7335 (1989 JA) ya kai tsawon mil 1.1 wato Kilo mita 1.8 kuma yana tafe a guje ya tunkaro Duniyar Earth zai wuce.

Hukumar kula da sararin samaniya wato NASA tace dutsen "mai yuwuwar haɗari ne ga duniya" amma babu tabbas ganin cewa akwai abubuwa da dama da s**a tunkaro duniya amma dai a wannan shekarar wannan dutsen shine mafi girma da zai wuce ta saman duniyar mu.

Muryoyi ta ruwaito NASA tace da fari dutsen zai bawa duniya tazarar mil 2.5 million wato 4 million kilometres wato akalla tazarar nisan dake tsakanin Duniyar Earth da wata sau 10 amma daga bisani zai rika zuwa kusa-kusa da duniya kuma wajajen karfe 2:26 na ranar Juma’a zai yi daf da duniya kana ya wuce a guje gudun da ya ninka gudun fitar harsashin bindiga sau 18.

Me zaku ce?

23/05/2022

Najeriya: Shugaba Muhammadu Buhari ya rattaba hannu kan wata sabuwar dokar kara kudin kira a waya, inda duk wani mai kiran waya ta salula zai biya akalla kobo guda cikin kowace dakika a matsayin harajin da gwamnati ta ce za ta yi amfani da shi ga harkar lafiyar gajiyayyu na kasar.

23/05/2022

A yau Lahadi Honarabul Hajia Zainab Suwuɗi ta bar Jam’iyyar PDP ta koma NNPP inda Shugaban Jam’iyyar na Katsina Alhaji Sani Liti Ƴan Kwani ya amshe su a Offishin Jam’iyyar na Kats…

23/05/2022

AbdulLahi Bn Mubarak ya ce: Wata rana muna zaune da Imam Malik yana karanta mana Hadisin Manzon Allah SallalLahu AlaiHi wa AliHi wa sallam kunama ta harbeshi har sau goma sha shida yana gumi jikinsa na komawa Kore, Amma bai yanke Hadisin da yake karantarwa ba. Bayan Mutane sun tashi na tambayeshi cewa yau Na ga abin Mamaki, Ya amsa man cewa kunama ce take ta harbinsa har sau goma sha shida Amma ya haqura saboda Girmama Hadisin Manzon Allah SallalLahu AlaiHi wa AliHi wa sallam da yake karantarwa.

Katura Zuwa Group 3 Kachal Domin Al'umma Su Amfana 🙏🏿

22/05/2022

    Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmed Lawan ya ce yana da aniyar ci gaba daga inda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tsaya idan har aka zabe shi a matsayin shugaban Kasar Nijeriya na gaba. Jaridar Leadership Hausa ta rawaito cewa Lawan, wanda shima ɗan takarar shugabancin ƙasa ne a jam’iyar AP...

22/05/2022

….”Muna Hasashen Tallafawa Mutum Miliyan goma a Najeriya” Inji Shugaban Ƙungiyar. Zaharaddeen Ishaq Abubakar @ Katsina City News Ƙungiyar nan mai rajin Motsin Siyasa da Tallafawa…

22/05/2022

Ko kun san ana ta ci gaba da tantance (screening) na wadan s**a cike neman tallafin COVID-19 na RRR Code

Za a iya tuna cewa a kwananin baya mun turo maku codes na kowace karamar hukuma da kuma mazabunta don, kowa ya ga codes din Unguwarsu ya cike neman tallafin a wayarsa karama ta hannu.

To yanzun haka, wannan tallafi mai suna Rapid Response Register a takaice a ce RRR, sun turo da sunayen f*k wadanda s**a cike neman tallafin, a santar da ya cike ta garin da yake.

Ana nan ana ta tantance duk Wanda ya cike kuma sunansa ya fito, ta hanyar shigar da bayanansa (BVN, da NIN, da kuma account number da lambar wayarka gami da codes din da aka tura maka lokacin da ka yi rijistar, in ka mance akwai shi a jikin sunayen da aka turo a wurin tantance ka)

Sai dai har yanzun Katsina Media Post News ba ta sami sunayen gaba dayansu ba a tsarin PDF ba, da za mu iya amfani mu wallafa su kowa ya gani, k**ar yadda muka wallafa codes a rubutunmu na can baya.

Bisa yawan korafin da muke samu, na wadanda ke nesa, da suke son su duba su gani ko akwai sunansu don su zo a yi masu screening din, muke kira ga duk mai PDF dake kunshe da sunayen yan jihar Katsina baki daya da ya tura mana ta layinmu na WhatsApp, 08037823502, ko 07066459525, ko a ta wannan layin 07068099976, domin mu sanya sunayen a tsarin kowace karamar hukuma har kowa ya duba ya ga nasa.

Ibrahim M Bawa CEO Katsina Media Post News

22/05/2022

Hakimin Karfi da ke karamar hukumar Takai a jihar Kano, Abdulyahyah Ilo da aka sace ya samu ‘yanci daga hannun wadanda s**a yi garkuwa da shi a makon da ya wuce

22/05/2022

Na rantse da Allah Duk waɗanda kuke gani suna nuna ɓacin ransu akan an ɗauki doka a hannu, wallahi ba ɗaukan doka ne damuwarsu ba, muturwa ita ce damuwar su, domin ko da kotu aka kai Debora aka yanke mata Hukuncin kisa sai sun fito sun ce hukuncin baiba.

Da yawansu kuma zaka ji magana suke akan kisan Debora, sun manta girman laifin da tayi na batanci ga Manzon Allah.

- Inji Sheikh Tijjani Yusuf Guruntum

22/05/2022

Messi 🆚 Ronaldo goals every year:
2004: 🇦🇷 5 🇵🇹 13
2005: 🇦🇷 4 🇵🇹 15
2006: 🇦🇷 12 🇵🇹 25
2007: 🇦🇷 31 🇵🇹 34
2008: 🇦🇷 22 🇵🇹 35
2009: 🇦🇷 41 🇵🇹 30
2010: 🇦🇷 60 🇵🇹 48
2011: 🇦🇷 59 🇵🇹 60
2012: 🇦🇷 91 🇵🇹 63
2013: 🇦🇷 45 🇵🇹 69
2014: 🇦🇷 58 🇵🇹 61
2015: 🇦🇷 52 🇵🇹 57
2016: 🇦🇷 59 🇵🇹 55
2017: 🇦🇷 54 🇵🇹 53
2018: 🇦🇷 51 🇵🇹 49
2019: 🇦🇷 50 🇵🇹 39
2020: 🇦🇷 27 🇵🇹 44
2021: 🇦🇷 43 🇵🇹 46
We won't see anything like this in football ever again.. 😳⚽

22/05/2022
22/05/2022

Hukumar DSS ta K**a Ƴan Boko Haram da Kayan Haɗa Bama-bamai Zasu Shiga Kano “Rundunar jam’ian farin kaya na DSS reshen jihar kano, tayi nasarar k**a mayaka boko haram 2 cikin karamar mo…

22/05/2022
22/05/2022

Babbar Magana Shin Adam a zango Yace Zai Koma Addinin Kirista Ne Ya Fita Daga MusulunCi Wannan Babbar Magana Ce Wadda Jama'a Suke ta Magana akai.

22/05/2022

An gaishe ku Delegates....

Sune mutane na farko da suke fara sayarda yancin su kafin daga bisani mata da ake bawa Omo da sabulu su biyu baya, sai Talakawa masu karɓan N500.

Ya Ubangiji cikin kayan marmarin Ka zaɓa mana na ƙwarai wanda ba zai samu gudawa ba, idan kuma tsintsiyar ce Ubangiji Ka sa ba ƙarasa share mu zata yi ba, idan kuma lemar ce Ya Ubangiji Ka sa ba sai mun taro ruwa ba ta ɓalle.

Daga Yaseer Gombe

22/05/2022

Jam'iyyar NNPP ta kwatanta dan takarar shugabancin kasa a karkashin ta, Kwankwaso a matsayin "ma'aikin Ubangiji" wanda yake son yakar yunwa da hadaa kan kasa.

22/05/2022
22/05/2022
22/05/2022

Babban Bankin Najeriya, CBN, ta ce nan ba da dadewa za a nemi naira ta takarda a rasa, yana mai shawartar mata da maza yan kasuwa su yi rajista da e-Naira. The

22/05/2022

ALAMAR MUNAFUNCI

Ka iya posting Happy birthday

Ka iya posting Happy Jumma'a

Ka iya posting Happy marriage

Ka iya posting NYSC CAMP

Ka iya posting new bouncing baby/boy

Ka iya posting Dan sisyasa a shafin ka

Ka iya posting new buy

Ka iya posting Happy graduation
E.T.C

Amma anci mutuncin MANZON ALLAH S.A.W. kayi shiru wai dan saboda kanada friends wanda ba musulmai ba.

Akwai Alamar munafunci a tare dakai.

Allah ka rabamu da munafunci.

~ Isma'il Bawa

22/05/2022

Hukumar hana almundahana da yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa watau EFCC ta bankado gidajen Akanta Janar na tarayya, Ahmad Idrs, guda goma sha bakwai (17).

22/05/2022

2023: Yi Wa Nijeriya Aiki Tukuru Tare Da Lalubo Hanyar Da Talakawa Za Su Samu Sauki Daga Matsanancin Halin Da Jam'iyyar APC Ta Jefa Kasar Ciki Shi Za Mu Sa A Gaba, Idan Na Zama Shugaban Kasa, Cewar Kwankwaso

Daga Malama Aisha Usman Golden (Uwa Mafi Uba )

Dan takarar shugaban kasa karkashin Jam'iyyar NNPP mai alamar kayan marmari Engr Rabi'u Musa Kwankwaso ya ce “idan Allah ya bamu nasara a zaben 2023 akwai guraren da zan toshe kudin gwamnati ya samu zama a yi wa talakawa aiki, ba sai an dorawa talaka bakin haraji ko an cire tallafin Gwamnati ba”.

Ya ce tsadar rayuwa da ake fama da ita na faruwa ne sak**akon yadda gwamnatin APC tasa matsanancin haraji akan kamfanoni da daidaikun mutane masu sana'oi da suke sarrafa kayan masarufi da kuma cire duk wani tallafi da talaka ke amfana kai tsaye daga gwamnati. K**ar tallafin man fetir da na gas, aikin hajji da kuma karya darajar naira.

Maimakon ta toshe hanyoyin da kudin gwamnati ke zirarewa don a gudanar da aiyyuka do talaka zai amfana batare da an takura rayuwarsa ba.

“Da yardar Allah idan muka kafa gwamnati za mu toshe irin wadannan guraren da dukiyar gwamnati ke zirarewa wasu tsirarun mutane na azurta kawunansu da shi mu yi wa kasa aiki kowa ya amfana.!Amma sai idan talakawa sun yadda zamu samu damar haka”, inji Kwankwaso.

22/05/2022

RA'AYI: Ya K**ata A Sanyawa Matan Arewa Dokar Taɓaci Na Yi Wa Kansu Kayan Lefe Da Kuma Kayan Ɗaki, Domin a Sauƙaƙa Wa Maza a Sha'anin Aure

–Ra'ayin Murjanatu Diri

Address

Yammama
Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Akuuu posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share


Other Media/News Companies in Katsina

Show All