
27/07/2025
HAZIƘIN ƊAN MAJALISAR JIHA A ZAMFARA YA RABAWA MUTANE 14 NAIRA MILIYA 10 DON SU KARA JARIN KASUWANCI.
Haziƙin ɗan majalisar dokokin jihar Zamfara Hon. Shamsudden Hassan Basko ya rabawa matasa daga yankin da ya ke wakilta na Talata Mafara ta Arewa, kyautar kuɗi har Naira miliyan 10 don sun ƙara jari a kasuwancinsu.
Matashin ɗan majalisar ya bayyana cewa "bayar da wannan jari ya biyo bayan nazarin da ya yi na na ganin cewa a wannan zamani ba abin da za ka yi wa matashi irin ka koya masa hanyar da zai dogara da kansa. Wanda haka ne ya sa na zaƙalo matasa 14 da na san suna kan kasuwanci amma suna da ƙaramin jari na raba masu waɗannnan kuɗaɗe.
Ɗan majalisar ya ƙara jaddada cewa wasu sun amfana da Naira miliyan ɗaya-ɗaya wasu kuma dubu ɗari biyar-biyar wasu dubu ɗari biyu-biyu.
Ɗan majalisar ya bayyana cewa wannan soman taɓi ne akan ƙoƙarin da ya ke yi na taimakon matasan da su ke yankin nasa. Don haka ya yi kira ga waɗanda s**a amfana da su yi amfani da waɗannan kuɗaɗe domin cigaban kasuwancinsu ta yadda nan gaba za su iya taimakon wasu.
Daga nan ya yi kira ga waɗanda ba su samu ba da su yi hakuri su ma sannu layi zai kawo gare su.
Matasan da s**a amfana ɗin sun bayyana matuƙar jin daɗinsu ga wanann ɗan majalisar tare da roƙon Allah ya ɗaukaka shi. Tare da masa fatan alheri da alƙawarin yi masa biyayya da jam'iyarsa ta APC.