Bilhaqqi Media Links

Bilhaqqi Media Links Media Channel

HAZIƘIN ƊAN MAJALISAR JIHA A ZAMFARA YA RABAWA MUTANE 14 NAIRA MILIYA 10 DON SU KARA JARIN KASUWANCI.Haziƙin ɗan majalis...
27/07/2025

HAZIƘIN ƊAN MAJALISAR JIHA A ZAMFARA YA RABAWA MUTANE 14 NAIRA MILIYA 10 DON SU KARA JARIN KASUWANCI.

Haziƙin ɗan majalisar dokokin jihar Zamfara Hon. Shamsudden Hassan Basko ya rabawa matasa daga yankin da ya ke wakilta na Talata Mafara ta Arewa, kyautar kuɗi har Naira miliyan 10 don sun ƙara jari a kasuwancinsu.

Matashin ɗan majalisar ya bayyana cewa "bayar da wannan jari ya biyo bayan nazarin da ya yi na na ganin cewa a wannan zamani ba abin da za ka yi wa matashi irin ka koya masa hanyar da zai dogara da kansa. Wanda haka ne ya sa na zaƙalo matasa 14 da na san suna kan kasuwanci amma suna da ƙaramin jari na raba masu waɗannnan kuɗaɗe.

Ɗan majalisar ya ƙara jaddada cewa wasu sun amfana da Naira miliyan ɗaya-ɗaya wasu kuma dubu ɗari biyar-biyar wasu dubu ɗari biyu-biyu.

Ɗan majalisar ya bayyana cewa wannan soman taɓi ne akan ƙoƙarin da ya ke yi na taimakon matasan da su ke yankin nasa. Don haka ya yi kira ga waɗanda s**a amfana da su yi amfani da waɗannan kuɗaɗe domin cigaban kasuwancinsu ta yadda nan gaba za su iya taimakon wasu.

Daga nan ya yi kira ga waɗanda ba su samu ba da su yi hakuri su ma sannu layi zai kawo gare su.

Matasan da s**a amfana ɗin sun bayyana matuƙar jin daɗinsu ga wanann ɗan majalisar tare da roƙon Allah ya ɗaukaka shi. Tare da masa fatan alheri da alƙawarin yi masa biyayya da jam'iyarsa ta APC.

Shugaban Kwastam Na Kasa Ya Yaba Wa AC Sanusi Saulawa da Sauransu Kan Ingantaccen AikiKwanturola Janar na Hukumar Kwasta...
24/07/2025

Shugaban Kwastam Na Kasa Ya Yaba Wa AC Sanusi Saulawa da Sauransu Kan Ingantaccen Aiki

Kwanturola Janar na Hukumar Kwastam (CGC), Bashir Adeniyi MFR psc(+) fniia, ya yaba wa jami’ai da dama saboda rawar gani da s**a taka a yayin bikin yaye dalibai na farko na babban kwas na jami’an gudanar da ayyukan Kwastam masu sarkakiya (Senior Executive Course in Complex Customs Operations).

An gudanar da bikin a Cibiyar Kula da Harkokin Duniya ta Najeriya (NIIA) da ke Legas.

Yayin da yake jawabi ga baƙi da jami’an da s**a kammala karatun, CGC Adeniyi ya ambaci musamman Mataimakin Kwanturola na Kwastam, Sanusi Saulawa, tare da wasu jami’an, saboda fitattun ayyukansu.

CGC ya bayyana cewa, "Na samu damar musabaha da yawancin waɗannan mahalarta tun kafin yau. Da yawa daga cikinsu sun nuna gagarumar bajinta a ilimi da ɗabi'a."

Ya ci gaba da cewa wasu mutane musamman "Ita na ɗaya daga cikinsu. Sidi na ɗaya daga cikinsu, kuma Sanusi na ɗaya daga cikinsu. Sanusi ya halarci taron ƙasa da ƙasa da yawa, kuma ya gabatar da laccoci. Lallai, za mu iya cewa muna alfahari da cewa waɗannan su ne shugabannin Kwastam na gaba." Inji shi.

Kungiyar malaman kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Hassan Usman Katsina Polytechnic wato ASUP, tayi taro da mombobinta domin...
23/07/2025

Kungiyar malaman kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Hassan Usman Katsina Polytechnic wato ASUP, tayi taro da mombobinta domin neman hanyoyin da za'a bi don cimma nasarar tsarin albashi na kashi ashirin da biyar da kuma kashi talatin da biyar.

A ranar talata 22/07/2025 kungiyar ta shirya taron wanda ta saba yi duk shekara, da yake jawabi shugaban kungiyar comrd. Nasiru Umar Gidado ya bayyana makasudin taron inda yace akwai bukatocin kungiyar wanda an rubuta ma gwamnati lokaci zuwa lokaci ammandai haryanzu shiru babu wani bayani daga gwamnati.

Ya kara da cewa wannan karin albashin ba wai yana nufin sabon tsarin albashi ba ne A'a tsari ne wanda yake kara darajar tsarin albashin manyan makarantu a fadin kasa baki daya wanda kuma tuni wasu Jihohin kasar nan sunfara amfana da wannan tsarin.

Daga karshe yayi kira ga gwamnatin Jihar Katsina akan ta bi wannan koke nasu domin aiwatar da wannan tsarin, saboda yanzu haka wasu makarantun wadanda suke amfana da wannan tsarin sun fara zawarcin malamai acikin wannan makaranta mai albarka.

Ana tsaka da taron sai shugabanin kungiyar da mombobin s**a aminta da yin tattaki zuwa ofishin shugabar hukumar gudanarwar makarantar da Kuma shugaban makarantar domin nuna rashin jindadin su akan ko in kula da gwamnati ta nuna kan waddanan bukatun nasu.

Da ta ke nata jawabin shugabar gudanarwar makarantar Hajiya. Indo Muhammad tace Jihar Katsina tana zama ta daya a bangaren Karin albashi kowa ya sani bamu daukar na karshe to amman wannan karon bansan dalili ba kuma gashi wasu Jihohin har sun ruga mu amfana da wannan tsarin.

Ta kara da cewa duk da haka zatayi korin ganin sun isa wajen shugaban ma'aikata na Jahar Katsina domin ganin an cimma matsaya akan wannan bukata da suke nema, ta kuma yi kira ga mambobin dasu kara hakuri bisa wanda s**a yi domin ganin an samu nasara.

RAI BAKON DUNIYA.TSOHON SHUGABAN 'KASAR NIGERIA MUHAMMAD BUHARI YA RASU BAYAN FAMA DA RASHIN LAFIYA A LONDON.
13/07/2025

RAI BAKON DUNIYA.

TSOHON SHUGABAN 'KASAR NIGERIA MUHAMMAD BUHARI YA RASU BAYAN FAMA DA RASHIN LAFIYA A LONDON.

Matashin bayan rubuta takardar ajiye aiki, ya faɗi wahalar da ya yi ga sanatan na kusan shekaru 20.    Wannan Hadimi ya ...
04/07/2025

Matashin bayan rubuta takardar ajiye aiki, ya faɗi wahalar da ya yi ga sanatan na kusan shekaru 20.
Wannan Hadimi ya Kyauta Kuwa..?
Ku Aje Mana A Comments Section.

Buba Galadima ya ce tururuwar neman Rabiu Kwankwaso da ake alama ce da shi ya fi dacewa ya mulki Najeriya. Karanta cikak...
04/07/2025

Buba Galadima ya ce tururuwar neman Rabiu Kwankwaso da ake alama ce da shi ya fi dacewa ya mulki Najeriya. Karanta cikakken rahoton a sashen sharhi.

SUBHANALLAH: Yanzu Muke Samun Labarin Ɗaya Daga Cikin Motocin Da S**a Ɗauki Matasa 'Yan Asalin Jihar Katsina Zuwa Oshogb...
04/07/2025

SUBHANALLAH: Yanzu Muke Samun Labarin Ɗaya Daga Cikin Motocin Da S**a Ɗauki Matasa 'Yan Asalin Jihar Katsina Zuwa Oshogbo Jihar Osun Kudancin Najeriya Ta Samu Haɗari A Tsakanin Abuja Da Lokaja, Amman Lamarin Ya zo Da Sauki,

Matasa (105) Da Shashen Bunƙasa Ayyukanyi Na Jihar Katsina Ya Dauki Nauyin Kaisu Wajen Karbar Horo Matsayin Sabbin Jami'an Tsaron Sojin Najeriya Karo Na 89.

Yayin Da Muke Tattaunawa Da Mai Baiwa Gwamnan Jihar Katsina Shawara Akan Samar Da Ayyukanyi Hon. Malam Yau Ahmad Nowa Dandume Ta Wayar Salula, Ya Tabbatar Mana Da Cewa Matasan Suna Samun Kulawa Asibiti Bayan Haka An Sake Tura Wata Motar Mallakin Gwamnatin Jihar KSTA Wadda Zata Kwashe Su Domin Tafiya Inda Ake Bukata.

Suna Bukatar Addu'oinku!..…..

Kuyi Share....

Karadua Post

03/07/2025

Address

Katsina

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Bilhaqqi Media Links posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Bilhaqqi Media Links:

Share