Hiznim TV NG

Hiznim TV NG Tarbiyya da tatattun labarai don inganta Al-Ummah

02/11/2024

1. Ana samun kuɓuta daga azzaluman Shugabanni da zaluncinau ne idan aka yi haƙuri, aka bi Allah, aka nemi mafita a wajensa, da wannan haƙurin a kan bin Allah ne, Allah ya ɗaura Annabi Musa da mutanensa a kan Fir'auna da Jama'arsa.

(( قَالَ مُوسَىٰ لِقَوْمِهِ اسْتَعِينُوا بِاللَّهِ وَاصْبِرُوا ۖ إِنَّ الْأَرْضَ لِلَّهِ يُورِثُهَا مَن يَشَاءُ مِنْ عِبَادِهِ ۖ وَالْعَاقِبَةُ لِلْمُتَّقِينَ)) ((قَالُوٓاْ أُوذِينَا مِن قَبْلِ أَن تَأْتِيَنَا وَمِنۢ بَعْدِ مَا جِئْتَنَا ۚ قَالَ عَسَىٰ رَبُّكُمْ أَن يُهْلِكَ عَدُوَّكُمْ وَيَسْتَخْلِفَكُمْ فِى ٱلْأَرْضِ فَيَنظُرَ كَيْفَ تَعْمَلُونَ)) A'araf 128-129

2. Cewa da wasu suke yi wai dole ne sai an fito an yaƙi zalunci ko ta wace hanya ce, wannan maganar ƙarya da gaskiya ce a cakuɗe, e, dole ne a kan kowa ya yaƙi zalunci, ya hana ɓarna gwargwadon ikonsa da damarsa, amma ta hanyar da Allah ya tsara ba ta kowace hanya ba, idan kuma mutane s**a ce ba za su bi hanyar Allah ba wajen yaƙar zalunci sai dai hanyar da zuciyarsu ta ƙawata musu, to ba za su taɓa samun mafita ba, dai a ci gaba da ruftawa cikin rami, saboda Allah zai cire hannunsa ne ya bar su da kansu a yi ta gwabzawa tsakanin zalunci da zalunci
((وكذالك نولى بعض الظالمين بعضا بما كانوا يكسبون)) An'am:129

3. Ta kowani gefe, Addinin Musulunci bai bar mu kara-zube ba, yana shar'anta mana manufofi ne tare da hanyar cim ma manufofin a haɗe, k**ar yadda ba ya halatta a sauka daga kan koyarwar shari'a cikin manufofin, k**ar faɗa da shirka da ƙoƙarin tabbatar da Tauhidi, faɗa da zalunci da tabbatar da Adalci, to haka ba ya halatta mutum ya fita daga tsarin shari'a, ya ɗakko hanyar da shari'a ba ta zo da ita ba wajen tabbatar da waɗannan manufofin, duk wanda ya yi haka shi ma ya faɗa cikin ɓarna kuma ba lallai ya samu mafita ba, ba a gyara ɓarna da ɓarna, Bahaushe ya ce kashin kare ba ya taki, jini ba ya maganin ƙishirwa, shi ya sa da Annabi (SAW) yana yi wa sahabbansa wasiyya a kan yadda za su mu'amalanci azzaluman shugawagabanni sai ya ce musu: ((أدُّوا إليهم حقَّهم، واسْأَلوا اللهَ الَّذي لكم.)), ma'ana "ku ku sauke haƙƙinsu da yake kanku, sannan ku nemi naku haƙƙin a wajen Allah" Bukhari: 7052.

4. Zaluncin shugaba ba ya halatta wa talaka zalunci, kowa zai girbi abin da ya shuka ne ranar ƙiyama, ko da kuwa na sama, ko shugaba shi ya koya wa mabiyi ko na ƙasa ɓarna, to wannan ba ya wanke mabiyin daga ɓarnarsa, tare da cewa wanda ya koyar da ɓarna, mai mulki ne shi ko Malami ko Mai gida, yana da kwatakwacin laifin duk wanda ya yi koyi da shi a kai, amma hakan ba ya nufin shi mabiyin ya sha, zububinsa yana nan daram shi ma zai je ya girba, kuma da sannu zai yi nadamar koyi da ya yi da wani a kan ba daidai ba.

((ومن دعا إلى ضلالة كان عليه من الإثم مثل آثام من تبعه لا ينقص ذلك من آثامهم شيئاً".))Muslim:2648

(( إِذْ تَبَرَّأَ الَّذِينَ اتُّبِعُوا مِنَ الَّذِينَ اتَّبَعُوا وَرَأَوُا الْعَذَابَ وَتَقَطَّعَتْ بِهِمُ الْأَسْبَابُ))((وَقَالَ الَّذِينَ اتَّبَعُوا لَوْ أَنَّ لَنَا كَرَّةً فَنَتَبَرَّأَ مِنْهُمْ كَمَا تَبَرَّءُوا مِنَّا ۗ كَذَٰلِكَ يُرِيهِمُ اللَّهُ أَعْمَالَهُمْ حَسَرَاتٍ عَلَيْهِمْ ۖ وَمَا هُم بِخَارِجِينَ مِنَ النَّارِ)) Baƙara: 166-167

5. Abin da zaluncin kowane mai zalunci, shugaba ne shi ko talaka, yake wajabta mana shi ne komawa ga Allah, da riƙo da hanyar shari'a wajen hana shi zaluncin da neman haƙƙin waɗanda ya cuta, ba wai mu ma mu narke mu zama maha'inta macuta masu yin yadda s**a ga dama ba idan muka yi haka mu ma mun zama irinsu, shi ya sa idan wani maɓarnaci ya zo ya yi zina da matarka ko ƴarka, kai ma ba zuwa za ka yi ka yi zina da matarsa ko ƴarsa ba don ka huce ko ka rama, haka wanda ya maka sata kai ma ba zuwa za ka yi ka masa sata ko ka sa a masa ba, ko ka yi wa wani da sunan kai ma an ma, akwai hanyoyin da shari'a ta gindaya na yadda za a mu'amalanci waɗannan abubuwan wanda idan aka kauce musu sai dai a ƙara wa ɓarnar faɗi memakon a rage ta, haka idan shugabanni sun yi zalunci, ba ya halatta ma duk wani nau'in ɓarna da fitina, da sunan ai su ma manyan haka suke, a'a, kowa kabarinsa daban hisabinsa daban.
((ألا تزر وازرة وزر أخرى)) ((وأن ليس للإنسان إلا ما سعى)) ((وأن سعيه سوف يرى)) Najmi:38-40

6. Ana haƙuri da zaluncin shugabanni ne saboda Allah, kuma saboda haka shari'a ta tsara don neman mafita, kuma a kansa ne Allah yake wa al'uma sak**ako mai daɗi, Allah da kansa yake ɗaukar nauyin kawo wa mutane canji na ƙwarai ta hanyar da s**a yi tsammani ko wadda ba su yi ba, idan s**a koma gare shi, s**a yi biyayya, da haƙuri da Jarabawar da s**a samu kansu a ciki. Allah (SWT) ya ce dangane da da'awar Annabi Muhammad (SAW) da sahabbansa:

(( وَعَدَ اللَّهُ الَّذِينَ آمَنُوا مِنكُمْ وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ لَيَسْتَخْلِفَنَّهُمْ فِي الْأَرْضِ كَمَا اسْتَخْلَفَ الَّذِينَ مِن قَبْلِهِمْ وَلَيُمَكِّنَنَّ لَهُمْ دِينَهُمُ الَّذِي ارْتَضَىٰ لَهُمْ وَلَيُبَدِّلَنَّهُم مِّن بَعْدِ خَوْفِهِمْ أَمْنًا ۚ يَعْبُدُونَنِي لَا يُشْرِكُونَ بِي شَيْئًا ۚ وَمَن كَفَرَ بَعْدَ ذَٰلِكَ فَأُولَٰئِكَ هُمُ الْفَاسِقُونَ)) (55) Nur:55

Imamuɗɗabari ya Ambata a ƙarƙashin wannan ayar cewa ta sauka ne a wani lokaci da sahabbai s**a kai kuka zuwa ga Annabi (SAW) a kan tsananin matsi da tsoro da danniya da suke ciki, suna ji k**ar ba za a fita daga wannan yanayin ba. Cikin wannan ayar sai Allah yake musu alƙawarin in dai s**a riƙe imani da Allah s**a yi aiki na ƙwarai to zai ba su nasara ya Mallaka musu daula su samu amincin yin addininsu, kuma ya maye musu tsoro da aminci. Kamar dai yadda ta ce dangane da sha'anin banu Isra'ila:

(( وَأَوْرَثْنَا الْقَوْمَ الَّذِينَ كَانُوا يُسْتَضْعَفُونَ مَشَارِقَ الْأَرْضِ وَمَغَارِبَهَا الَّتِي بَارَكْنَا فِيهَا ۖ وَتَمَّتْ كَلِمَتُ رَبِّكَ الْحُسْنَىٰ عَلَىٰ بَنِي إِسْرَائِيلَ بِمَا صَبَرُوا ۖ وَدَمَّرْنَا مَا كَانَ يَصْنَعُ فِرْعَوْنُوَقَوْمُهُ وَمَا كَانُوا يَعْرِشُونَ)) A'araf:137

Saboda haka, ba wai wannan cewa a yi haƙurin yana nufin an yarda da abin da suke yi na zalunci ba ne, jifan duk wanda ya ce mutane su yi haƙuri su koma ga Allah da cewa yana kare azzalumai ko ya yarda da abin da suke yi, ita wannan maganar ita ce babbar zalunci, saboda babu adalcin da ya wuce a nusar da mutane a kan tsayawa kan hanyar Allah don da ita kaɗai ne ake iya samun mafita mai ɗorewa.

7. Haka kuma haƙuri ba ya nufin ba za a yi wa shugabanni nasiha ba, ko ba za a yi umarni da kyakkyawa da hani daga mummuna ba, saboda hakan yana kishiyantar zama na ƙwarai da bin Allah, kuma Allah ya game Al'uma da uƙuba idan s**a kasance masu shiru a kan ɓarna, saboda haka wajibi ne musamman ga Malamai su tsaya da wa'azi da karantarwa da umarni da kyakkyawa da hani ga mummuna, gwargwadon yadda shari'a ta tanadar, Annabi (SAW) ya ce:

(( الدِّينُ النَّصِيحَةُ. قُلْنا: لِمَنْ؟ قالَ: لِلَّهِ ولِكِتابِهِ ولِرَسولِهِ ولأَئِمَّةِ المُسْلِمِينَ وعامَّتِهِمْ)) Muslim:55

(( والذي نفسي بيدِه لتَأمرُنَّ بالمعروفِ ولتَنهوُنَّ عن المنكرِ أوليُوشِكَنَّ اللهُ أن يَبعثَ عليكمْ عقابًا منهُ فتدعونهُ فلا يَستجيبُ لكمْ)) Tirmizi:2169

Wanda idan Allah ya zo saukar wa da al'uma uƙuba dalilin shiru a kan ɓarna, ana tseratar da masu hani ne kawai, a azabtar masu zaluncin da masu goya musu baya kai tsaye da masu shiru da miƙa zuciya ga zaluncin.

((فَلَمَّا نَسُوا مَا ذُكِّرُوا بِهِ أَنجَيْنَا الَّذِينَ يَنْهَوْنَ عَنِ السُّوءِ وَأَخَذْنَا الَّذِينَ ظَلَمُوا بِعَذَابٍ بَئِيسٍ بِمَا كَانُوا يَفْسُقُونَ)) A'araf:165

((إنَّه يُسْتَعْمَلُ علَيْكُم أُمَراءُ، فَتَعْرِفُونَ وتُنْكِرُونَ، فمَن كَرِهَ فقَدْ بَرِئَ، ومَن أنْكَرَ فقَدْ سَلِمَ، ولَكِنْ مَن رَضِيَ وتابَعَ)) Muslim:1854

8. A gefe guda kuma, wa'azi da hani a kan ɓarna ba ya wajabta fito na fito da azzaluman da ingiza al'uma a ce su fita su ɗaga musu yatsa ko su ƙwaci haƙƙinsu ƙarfi da yaji, ko a hargitsa al'amura a yi uwar watsi, duk Malami ko mai da'awa ko wani ɗan gwagwarmaya da ya ɗaura al'uma a kan irin wannan hanyar ba shakka zai samu sak**akonsa wajen Allah, kuma zai girbi abin da ya shuka, don shi ma idan fitina ta zo ba za ta ƙyale shi ba. Babban abin da ake buƙata daga Malamai a irin wannan yanayin shi ne su kasance masu kira izuwa ga hanyar Allah, su guji raɓar azzaluman masu mulki da ba su kariya ko neman tuwo a wajensu, su koma gefe su kafa da'awarsu, su gina ta a kan haɗa al'uma da Allah, su karantar da su haƙuri da komawa ga Allah da neman mafita a wajensa, su jira har izuwa lokacin da Allah zai yi ikonsa, wannan ita ce hanyar Annabawan Allah. Shi ya sa Annabi Musa (A.S) bai ingiza mutanensa cewa su fita su gwabza da Fir'auna da mutanensa ba, sai dai ya yi tausar mutanensa da cewa idan sun tabbata a kan hanyar Allah zai kawo musu mafita a ƙarshen lamari, haka Annabi Muhammad (SAW), duk da matsin lambar da ya samu a Makka, har ta kai an kore shi daga garin, ya yi ta ba su haƙuri har ya tarbiyyantar da al'uma ta kafu a kan tauhidi da bin Allah, sannan aka umarce shi da Jihadi. To in dai an kyautata zuciyoyi an bi Allah komai daga baya mai sauƙi ne, wannan kuma yana buƙatar jagorancin Malamai na Allah, wanda shi ne abin da alumarmu ta fi tsananin buƙatuwa gare shi sama da komai, in dai har mafitan muke son samu. Ba wata hanya da za ta iya tseratar mana da Addininmu da duniyarmu idan ba cikakken komawa ga Allah muka samu ba bisa jagorancin Malamai na ƙwarai.

Allah ya ba wa ƙasarmu lafiya da zama lafiya.

Mallam Bahaushe
03/08/2024

02/11/2024

Sheikhanã Ateeq Sulaiman ya rubuta (01. Sept. 2023)

Idan Allah ya albarkaceka da gina karatunka akan ta'sili ingantacce na ilimi to ka godewa Allah.

Wasu yan uwanmu daliban ilimi lamarinsu ze ba ka tausayi gami da ba ka takaici ; wani ze lazimta ma ka dacewa da shi acikin komai a harkar mas'aloli na ilimi , duk da cewa kun sha banban ta fuskar mashayar ilimi , shi abun da ya dauka ilimi shine kiyaye matsayar wani sashe na malamai na zamani acikin mas'aloli na addini , don haka shi harkar iliminsa kullum tana nan acikin fatawowin Malamai na zamani , ba ya da hunkoro akan isa zuwa ga dalilai na mas'lolin addini , kuma ba shi da basira wurin tantance zare da abawa yayin sabanin Malamai acikin mas'aloli na addini .
Kai kuma ka san matsayar malamai na da da na yanzu akan wasu mas'alolin , kuma dede gwargwado ka san dalilai na shari'a akan mas'alolin , kuma kana iya yin nazari na ilimi akan dalilan har ka iya tantance zare da abawa acikin zantukan malamai mabanbanta . To a haka se ka ga wancan 'dalibin na matakin farko se ya yi qoqarin lazimta maka dacewa da shi acikin duk matsayoyansa a harkar ilimi , bisa hujjar cewa wai ai shi madogararsa akan matsayarsa itace wasu malamai na zamani , ze iya wuce iyaka akanka idan ka saba ma sa , idan tsautsayi ya ratsa ze iya jifanka da rena malamai da sauka daga tafarkin magabata !

Wata rana wasu mutum biyu su na magana akan mas'alar ha'de Sallah saboda ruwan sama , ni kuma ina gefe ina sauraronsu , dukkansu madogararsu akan matsayarsu acikin mas'alar shine Shaikh wane ya ce , dukkansu sun dogarane da fatawar wani babban Malami na zamani akan mas'alar , kuma so su ke yi ni ma in dace da su akan matsayarsu da madogararsu , alhali ni alokacin na kiyaye Hadisan da su ka zo akan mas'alar, kuma na kiyaye ingantattunsu da masu rauninsu , kuma na san illolin masu raunin , sannan na san i'itiradat da a ka yi akan manuniyar Hadisan akan mas'alar , sannan kuma na san mazhabobin Malaman Fiqhu akan mas'alar . Amma fa a haka su wadancan mutanen so su ke idan zan yi magana akan mas'alar to in yi magana acikin mas'alar irin yanda su ma su ka yi ; in dace da su ta fuskar matsaya da madogara ! Duk da cewa madogararsu ba madogara bace ta ilimi da shari'a , amma ahaka suke so su lazimtawa waninsu tsayuwa akanta .

Hakanan wata rana wani shima yana magana akan Hadisin Ibnu Abbas , hadisin da yake magana akan ramakon azumi ga wanda ya mutu , bayan ya kawo hadisin se ya ce : Amma Lajnatud da'ima ta ce azumin alwashi kawai za a rama " !

Ya kawo hadisi gamamme , amma se ya kebanceshi da Lajnatud da'ima !

Yau da cewa ya yi : Mazhabar Hambaliyya , ko Imamu Ahmad , ko wasu magabata su na ganin cewa azumin alwashi ne za a rama amma banda na Ramadana " to da hakan ya dan fi sauqi_sauqi .
Shima wannan se de ka kame baki ka qyaleshi kawai , idan ka ce za ka warware mas'alar to ba lalle bane a tashi lafiya ; yana iya jifanka da rena manyan Malamai , ko ya jefeka da sauka daga hanyar magabata , ko ya ce kana ji da kanka , ko girman kai , lefinka shine : ba ka tunani irin na shi , ba ka tasarrufi irin na shi , kai kuma uzurinka shine : banbancin da ke tsakaninku na ginin hanyar ilimi .

Matsalolin suna da yawa , se de a yi ta haquri da juna.

22/10/2024

Daga shafin Abu Ahmad Ateeq Sulaiman Allah Ya saka mishi da alheri.
hmmm lallai iilimi ba wasan yara ba ne!!!!!

WANI WAJIBI DA BA KASAFAI AKE DAMUWA DA TABBATAR DA SHI BA ( TUNATARWA GARENI 'DALIBIN ILIMI )

Al'umma tanada tsananin bu'katar Malamai 'kwararru a fannonin ilimi , saboda wa'dannan Malaman sune fitilu na wannan Al'ummar ; sune suke haskawa mutane amintacciyar hanya ta Addini da rayuwa , da samuwarsu Al'umma take nagartuwa , da kuma rashinsu Al'umma take halaka ta shiga cikin yamutsi da tashin_tashina acikin Addini da rayuwa .

Ga 'Dalibin da yake fatan ya zama Malami nan gaba , wanda al'umma zata ringa maida al'amuranta zuwa gareshi , to dolene 'Dalibin ya 'daura 'dammara domin bibiyan hanyoyi na gaskiya da zasu sadar da shi zuwaga wannan katafaren matsayi .

'Dalibin ilimi wajibine ya san dukkan littattai ababen dogaro wurin fahimtar dukkan fannona na ilimi , ya tabbatar ya karance wa'dannan littattafan karatu na fahimta domin kaiwa zuwa ga abunda yake fatan isa zuwa gareshi .

Zan 'dan yi ishara zuwa ga wasu fannona wa'danda mu anan Nigeria galibi ba'a koyon fannonan daga littattafai ababen dogaro a wa'dannan fannona :

Fannin lugah da Adab : a wannan fannin ya k**ata 'dalibi ka karanta wa'dannan littattafai k**ar haka :

_ إصلاح المنطق لابن السكيت
_ إصلاح غلط العوام لابن الأعرابي
_ الفصيح لثعلب
_ المثلث لقطرب
_ الصاحبي في فقه اللغة
_ القاموس المحيط
_ قصيدة بانت سعاد
_ المقصورة لابن دريد
_ لامية العرب
_ المعلقات العشر
_ مقامات الحريري
_ جوهرة الأدباء لابن دريد

Wa'dannan littattafai da na ambata , dukkansu littattafaine sanannu awurin Malamai tuntuni , Su ake karantawa da mak**antansu domin fahimtar wa'dannan fannoni .
Idan zai yi ga 'Dalibi , ya haddacesu gaba 'dayansu , ko kuma ya haddace wasu daga ciki , k**ar :

* إصلاح المنطق
* موطأة الفصيح ( نظم الفصيح لثعلب ) * المعلقات العشر
* المقصورة لابن دريد .

Ammafa wa'dancan sauran littattafan wajibine ya yi it'kaninsu , ya lazimcesu 'kwarai da gaske .
Sannan kuma ya bibiyi sharhohinsu bayan ya gama kyautata fahimtar mattaninsu , k**ar Sharhin Mu'allaqat na Ibnul A'araby , da Sharhin Alfasih na Zamakhshary , da dai sharhohi da Malamai Su ka yi ga littattafan .
Kada 'dalibi ya 'bata lokacinsa wurin karanta wasu littattafai wa'danda ba ababen dogaro bane awadannan fannona , k**ar wa'dannan littattafan :

# همزية
# بدماصي
# عشرينية
# طنطراني
Su wa'dannan littattafai da mak**antansu , ba sune ababen dogaro wurin fahimtar lugah na larabci , don haka Kada ka shagaltu da su ka bar abunda yake shine asali awurin Malamai ma'abota ilimi .

Fannin balagah : ka karanta littattafai k**ar :

_ التبيان في علم البيان للزملكاني
_ التبيان في علم البلاغة للطيبي
_موجز البلاغة لابن عاشور
_ تلخيص المفتاح للقزويني
_ مأة المعاني والبيان لابن شحنة الحلبي
_ الجوهر المكنون للأخضري
_ عقود الجمان للسيوطي

Wa'dannan littattafan wajibine ka yi it'kaninsu , sanann kuma ka haddace na haddacewa , k**ar Alfiyyar Suyudy U'kudul Juman .
Sanann kuma ka bibiyi sharhohin Talkhisul Miftah bayan ka yi it'kanin wa'dannan mattanoni .

Kada ka kuskura ka ringa jin cewa _wai_ ka san balagah saboda ka karanta littafin "Albalagatul Wadiha " , maganar gaskiya itace : indai Shi ka karanta ka'dai , to ba zaka san gardi da lagwadan Al'qur'ani da Sunnah ba ta fuskan tadabburin abunda Su ka 'kunsa na ma'anoni .

Daga cikin abunda zai 'kara maka tamakkuni acikin Balagah , karanta littattafan Malaman da su ke bada kulawa wurin fitar da fa'idoji na balagah daga cikin Alqur'ani ko Hadisi , k**ar littattafan Al'allamah A'd'diby acikin Sharhinsa ga Almasabih na Bagawy , da Al'Imam Ashshaukany Acikin Rasa'il dinsa cikin majmu'ul fatawa dinsa( Alfathur rabbany ) , da Ibnu Ashur acikin littattafansa , k**ar littafin Tafsirinsa da littafinsa " Annazrul Fasih " , da Ibnu Hajar cikin Fathul Bary , Da Al'Imam Alkhaddaby acikin Sharhinsa ga Sunan Abi Dawud , da Suyudy acikin wasu ke'bantattu wasiqunsa , k**ar risalarsa akan Ayar Suratul Baqara " الله ولي الذين آمنوا " , da Sharhinsa ga Hadisin Niyyah , da Alkhadib Attiftazany acikin Sharhinsa ga Al'arba'unan Nawawiyyah , da Addufy acikin littafinsa Al'iksir da Sharhin Al'arba'un .

Bibiyan littattafan Malaman da suke bada kulawa ga wannan janibin zai taimakawa 'dalibi wurin amfana da qa'idojin da ya koya daga wa'dancan mattanoni ta yanda zai san yanda ake aiwatar da su akan nassoshi da fitar da fa'idoji daga cikinsu .

Fannin Sarfu : ka karanta littattafai k**ar haka :

_ متن البناء
_ تلخيص لامية الأفعال
_لامية الأفعال
_ أرجوزة التصريف
_ الشافية لابن الحاجب
_ لامية الأفعال مع زيادات البحرق وابن زين
_ القصيدة السجلماسية ( مبلغ الآمال )
_ التسهيل لابن مالك

Anan mafi 'karancin abunda zaka haddace shine Lamiyyatul Af'aal Mai taushihin Bahraq da Ibnu Zain , sauran kuma sai ka yi it'kaninsu .

Fannin Hadisi : dolene ka karanci Alkutubus Sitta a gaban Malami , bayan ka gama da mattanoni na littattafan Hadisan hukunce_ hukunce k**ar littafin Umdatul Ahkam 'karamin da babban , da Bulugul Maram , da littafin Almuharrar na Ibnu AbdilHadi ko kuma littafin Al'ilmam na Ibnu Daqiq .

Shi ilimin Hadisi tekune Wanda bashi da gaci , don haka Shi zaka yita karatune kawai ba ji_ ba gani ; ka sanya aranka cewa sai ka karance dukkan littattafan da s**a tattaro Hadisan Annabi daga dukkan nau'ukansu , tun daga kan masanid zuwa Sihah da Sunan da Jawami'u da dai sauran nau'ukan littattafan da suke 'kunshe da Hadisan Annabi .

Dangane da mus'dalah , kada ka bata lokacinka wurin yawaita karanta littattafansa , ka wadatu kawai da yan kadan wa'danda su ka 'kunshi maqasudin Ilimin , k**ar Nukhbatul Fikar , da Ulumul Hadis na Ibnus Salah , da Alfiyyah ta Suyu'dy da Sharhohinta , k**ar Sharhin Al'allamah Alwallawy 'karamin Sharhinsa da babban .
Sai kuma Annukah na Ibnu Hajar da Zarkashy ga littafin Ulumul Hadis na Ibnus Salah .

Inda zaka fi bawa 'karfi shine littattafan Rijaal da Ilal na Hadisi , ka yawaita karantasu kwarai da gaske , su caku'de da kai tamkar jini da tsoka ; ya zamana idan ka ga Hadisi da Isnadinsa dukkan mazajen Hadisin ka sansu ba tare da buqatar komawa littattafan Rijaal ba a galibin halinka .

Da shagaltu da littafin Sharhin Ilalut Tirmizy na Ibnu Rajab , idan so samu ne ka haddace nazaminsa na Al'Allamah Wallawy ( ألفية علل الحديث )

Idan kanaso ka kware awurin sanin Fiqhun Hadisi da istinbadi acikinsa to ka lazimci littattafai k**ar haka :

1 .إحكام الأحكام لابن دقيق العيد مع حاشية الصنعاني
2. نيل الأوطار للشوكاني
3. الإمام لابن دقيق العيد
4. شرح الإلمام لابن دقيق
5. معالم السنن للخطابي
6. شرح سنن أبي دود لابن القيم
7. فتح الباري لابن رجب وابن حجر
8. المنهاج للإمام النووي
9. شرح مسند الشافعي لابن الأثير
10. التمهيد والاستذكار لابن عبد البر
11. الأجوبة عن المسائل المستغربة لابن عبد البر
12. شرح المصابيح للطيبي .

Bayan haka , ka yi wa kanka al'kawarin cewa : wajibine ka karance dukkan littattafan Ibnu Hajar da Zahaby acikin Fannin ilimin Hadisi ka bajima ko ba da'de .

Idan kanaso ka san sa'bani na Magabata acikin mas'aloli na addini tare da sanin madogaran kowane 'bangare daga Hadisan Annabi , to ka karanta wa'dannan Littattafai :

1. المصنفات
2. الأوسط لابن المنذر
3. التمهيد والاستذكار لابن عبد البر
4. السنن الصغرى والكبرى للبيهقي
5. الخلافيات للبيهقي
6. التحقيق لابن الجوزي مع شرحي ابن عبد الهادي والذهبي .

Fannin Qur'ani : ka haddaceshi gaba dayansa , ka karance littattafan da su ka yi bayanin ma'anonin 'dai'daikun ba'kin kalmominsa , k**ar wa'dannan littattafai :

1.غريب القرآن لابن قتيبة
2.مشكل القرآن لابن قتيبة
3. معاني القرآن للفراء
4.معاني القرآن للأخفش
5.مجاز القرآن لأبي عبيدة
6. غريب القرآن لغلام ثعلب

Idan zai yi wu ka haddace manzumar Ibnul Munayyir na Garibul Qur'an ( النظام العجيب في تفسير الغريب )

Daga nan ka kutsa cikin littattafan Attafsiru bil ma'athur gaba dayansu daki_daki .

Fannin Aqidah : ka karance littattafan da suke hikayar mas'alolin da Salaf Su ka hadu akansu daga cikin mas'aloli na Aqidah , k**ar Dahawiyyah , da wasi'diyyah , da lum'atu li'itiqad da sauransu .
Sannan ka tsallaka cikin littattafan da suke ruwaito Aqidar Magabata acikin babuka na Aqidah , k**ar littafin I'itiqadu Ahlussunnah na Lalika'iy , da Al'ibanah na Ibnu Ba'ddah , da Ashshari'ah ta Al'Ajurry , da Assunnah ta Ibnu Abi Asim da sauransu .

Daga nan kuma sai ka zo ka tare akan littattafan Ibnu Taimiyyah gaba 'dayansu wa'danda suke tattaunawa akan Aqida da ilmul firaq , k**ar :

التسعينية
شرح الأصبهانية
الانتصار لأهل الأثر
منهاج السنة
التدمرية
الحموية
الرد على الجهمية
درء تعارض العقل والنقل
مجموع الفتاوى
المستدرك على المجموع الفتاوى
جامع المسائل والرسائل

A 'karshe Ina mana nasiha da ababe k**ar haka :

1. Ka sani cewa koyon ilimin Addini ibadane , don haka ka kyautata niyyarka , kuma ka inganta hanyar nemanka gareshi .

2. Ka yi haquri da talauci da fatara a wannan harkar da ka za'bawa kanka ; zaka yi fama da talauci , zaka rasa abokan hul'da , zaka yi fama da 'yan tsurku , duka wannan jarabawace gareka , ka jajirce akan abunda yake gabanka , yin haqurin samun ladane gareka , kuma daukakane gareka awurin wanda kake yi don shi .

3. Ba lallai bane ka samu cikin abokananka Wanda zai k**a turba irin wannan ; to ka da ka yarda rashin samun abokin tafiya ya darzar da kai daga kaiwa k**ala .

4. Kada ka yarda ka shagaltu da harkan shugabnci ko ya yake , ka haqura da shiga harkoki na jama'a domin ka samu ka tsayarwa da jama'ar wajibin da s**a gagara tsayar da shi .

5. Kada ka yarda ka kar'bi malumtarwar da mutane suke maka , idan ka ru'du da hakan to lallai ka jahilci kanka , kuma baka cancanci hanyar da kake raya cewa ita kake bi ba .

7 . Ka sanya tsoron Allah ya zama jagoranka , ka zama Mai yawan ibada da 'kas'kantar da kai zuwa ga Allah , ka ke'bewa kanka wani lokaci da zaka ringa ganawa da mahaliccinka kana bijiro masa da buqatunka .

8. Ka zama Mai wadatan zuci , ka ringa yarda da ka'dan , kada ka yarda ka zama makwa'daici , Kada ka bada fuskarka ga masu abun duniya .

9. Ka nisanci alaqa da masu ku'di da 'yan Boko , Kada ka yarda wani mai wadata ya gayyaceka gidansa , ka yi haquri da talaucin da kake ciki Kada ka kuskura ka amshi ku'dinsa . Ka da ka amshi wani abun duniya sai daga hannun Wanda kuke harka iri 'daya . Mai ku'di mara ilimi da addini ko ciki 'daya Ku ka fito da shi to ka tsoraceshi kada ka saki jiki da shi .

10 . Ka wadatu da kanka wurin neman abun rayuwarka , idan zai yiwu kar ka zama aqarqashin wani awurin samun abun rayuwarka .

11. Idan Al'amura sun yi maka zafi , ka koma cikin littattafan da s**a rubuta tarihin Malaman Hadisi , acikinsu akwai lallashi da 'karfafawa ga wanda ya k**a wannan hanya .

12. Kar ka auri mace sai wacce Ku ka dace a manufa da tafarki , ko kuma wacce tafi son wannan tafarki sama da yanda take Sonka .

13. Idan kanaso ka fahimci haqiqanin addinin Musulunci bai 'daya , to ka lazimci Littattafan Shaikhul Muhaqqiqin Ibnu Taimiyyah .
14. Ka zama Mai amfanar da Al'ummar da kake rayuwa acikinta daidai gwargwado , ba tare da ka shagaltu ba da abunda zai raunana ingancin hanyar da kake kanta ba.
15. Ka karance dukkan littattafan Allamah Alwallawy , saboda dukkansu littattafaine na ta'asili daga kowane fanni , Su kuma manya_manyan littattafansa k**ar sharhohinsa ga littattafan Hadisi zaka amfana da su wurin fahimtar wasu kura_kurai da Shaukany ya afka acikin wasu mabahis na ilimi , saboda yanda Shi Shaikh Wallawin ya yi ta ta'aqqubin Shaukanin acikin wasu mabahis na ilimi , musamman acikin wagegen Sharhinsa na Sunanun Nasa'iy ( ذخيرة العقبى )

Na rubuta wannan nasiha ne ba don ni na siffantu da dukkan abunda na zayyana ba , a'a na yi hakan ne domin fa'dakarwa gareni a ke'be , da kuma sauran 'yan uwana a game , don haka wannan rubutu da na yi wa'azine gareni wanda duk lokacin da na tuna da Shi zai farkar da ni ya dawo da ni hayyacina .
Allah ya yafe mana .

فكن رجلا رجله في الثرى ** وهامة همته في الثريا

HUKUNCIN FITAR MACE DA'AWAA taƙaice, fatawowin Sheikh Muhd Nasiruddinil Albani (R) suna nuna cewa, mas'alar fitar mace d...
13/10/2024

HUKUNCIN FITAR MACE DA'AWA

A taƙaice, fatawowin Sheikh Muhd Nasiruddinil Albani (R) suna nuna cewa, mas'alar fitar mace daga gida don koyon karatu da koyar wa, akwai rabewa tsakanin abun da yake asali a gare ta, da abun da aka shar'anta mata, da abun da aka haramta mata.

ASALI GA MACE SHI NE:

- Tabbatarta a gida, ta koyi karatu ta koyar a nan.
- Tarbiyyar yara, da kula da gida shi ne babban aikin mace, da'awa ba ya cikin ayyukanta.
- Neman iliminta yana kasancewa a gida, ko a masallaci, ƙarƙashin malami namiji, ko a wajen da babu cuɗanya tsakanin maza da mata.
- Idan za ta koyar, yana halatta ta koyar a wuraren da aka ambata banda masallaci (Gida, ko wajen da babu cuɗanya tsakanin maza da mata).

ABUN DA AKA SHAR'ANTA MATA NA KARANTARWA

- Kafin ta fara karantarwar, ba makawa sai ta kasance mai ilimi na shari'a da zai zame mata tushe, kada ta shiga da ƙarancin ilimi.
- Ta tara ƙawayenta ko maƙotanta (da za ta karantar) a gidanta ta koyar da su.
- Ko su taru a wani gida sai ta fita ta same su a gidan ta karantar da su.
- Ya kasance wajen karantarwar keɓaɓɓe ne ga mata kaɗai, k**ar makaranta ko cibiya, ko ginin da yake tare da wani masallaci idan ya kasance a keɓance kacokan, irin wannan zai ɗauki hukuncin gida.
- Tana iya halartar darussan malamai a masallatai ko wani wajen.

ABUN DA AKA HARAMTA MATA

- Karantarwa a masallaci.
- Ta yi tafiya zuwa wani gari don da'awa, musamman idan babu muharrami.
- Fifita karantarwa a kan tarbiyyar ƴaƴa da kula da gida.
- Yawaita shige da fice.
- Duk abun da aka haramta wa namiji ita ma ya haramta a gare ta.

DALILIN WANNAN RABEWAR

- Ba'a samu mata ba a zamanin manzon Allah (SAW) da sauran ƙarnuka mafiya falala, suna karantarwa a masallaci, ko suna tafiye-tafiye don karantarwa, tare da samun dalilin tafiyar, da cikan sabubbanta, da rashin samuwar wani cikas da zai hana karantarwar.

Dalilin shi ne:

- Larurar fitar da mata daga jahilci, musamman ma a irin halin da ake ciki a wancan lokacin, sauyi ne daga shirka zuwa tauhidi, (kenan buƙatar karantarwar ta fi tsanani).

Sabuban su ne:

- Samuwar mata malamai, tarihin Nana Ai'sha Allah ya ƙara mata yarda ba ɓoyayye ba ne, wadda ita ce mace mafi ilimi cikin wannan al'ummar.
- Samuwar masallatai. (amma tare da haka waɗannan matan masu tarin ilimi da al'uma ta ƙaru da su irinsu Nana Ai'sha (RA) ba su je suna karantarwa a masallaci ba).

SANNAN

- Annabi (SAW) ya yi aike zuwa garuruwa (don yin da'awa), k**ar yadda ya tura mu'az, da wasu makaranta, amma ba'a taɓa samu ya tura mace ba.
- Cikin hakan akwai wofintar da aikinta na asali, shi ne tarbiyya da kula da gida.
- Cikin hakan akwai saɓa wa asali ga mace, shi ne zamanta a gida, saboda haka ba zai zama daidai ba sai da dalili.
- Yana sa ta k**anceceniya da maza.

SHUBUHA DA AMSARTA

In da wani zai ce: Ai karantarwar mace a masallaci wasila (hanya) ce kawai ta da'awa, su kuma wasa'il, ba nassi ake bi ba manufar da ta sa aka riƙe su kawai ake kallo, saboda haka ba zuwa masallacin ba ne ibadar, koyarwa ne da yaɗa ilimi kawai, amma amfani da masallacin yana matsayin hanya ne na isar da saƙon.

Amsarsa ita ce: Duk wani aiki da musulmi zai yi, sai ya bi hanyar Annabi (SAW) don shi abun koyi ne ba a iya manufofin ba kawai, har da hanyoyin da za su kai mu ga manufofin, saboda haka:

- Ba ya halatta a yanzu mu riƙi wata wasila da Annabi (SAW) ya samu damar ya riƙe ta, amma bai yi ba.

Ga wata ƙa'ida da Ibnutaimiyya ya ambata a littafin iƙtida'us-siraɗil-mustaƙim (278-281), a taƙaice:

- Wasiloli da suke samuwa a kowane waje da lokaci sun rabu gida biyu:

1. Waɗanda aka samu dalilin amfani da su a zamanin Annabi (SAW) amma ba a yi amfani da su ba, farar amfani da su a yanzu bidi'a ne.

MISALAI

- Keɓancewa mata wajen sallarsu daban daga na maza a masallatai, akwai dalilin yin hakan a zamanin Annabi (SAW) da damar yi, amma bai yi haka ba, a zamaninsa a inda maza suke salla a nan mata suke yi, to ƙirƙirar rabawan a yanzu bidi'a ne.

- Yin amfani da ilimin taurari wajen irga kwanakin wata, akwai Ilimin taurari a zamanin manzon Allah (SAW), kuma akwai dalilin yin amfani da shi da damar yi, amma bai yi amfani da shi ba, saboda haka ƙirƙirar amfani da shi a yanzu don irga wata bidi'a ne.

2. Waɗanda dalilin da zai sa a yi amfani da su a zamanin Annabi (SAW) bai faru ba, irin waɗannan sai a duba.

- Idan dalilin ƙirƙiro wannan wasilar shi ne gazawar musulmai wajen ɗabbaƙa addini, (sai a ƙirƙiro wata hanya don dawo da su kan hanya da Annabi (SAW) bai yi amfani da ita ba), to wannan bai halatta ba.

- Idan kuma ba dalilin kasawar musulmai ba ne ya sa aka ƙirƙiro ta, kawai saɓanin waje ne da zamani ya haifar da shi, to a nan duk wasilar da ta taimaka a kan wata gaya da aka shar'anta halattacciya ce (Misali: amfani da lasifika wajen kiran salla), wannan nau'in su ake kira Masalihul Mursala.

ILZAMI

- Idan za a halatta karantarwar mace a masallaci ko tafiya garuruwa yin da'awa, da sunan wasila ce kawai ta ilmantarwa, to hakan zai wajabta a wanke abubuwa da yawa da malamai s**a yi wa hukuncin bidi'a wanda kuma ba wanda ya ke inkarin cewa bidi'o'i ne, saboda masu yinsu suna da damar cewa "ai ba mu riƙe su a matsayin ibada ba, a matsayin wasila muka riƙe su na yin wata ibada da take da asali".

MISALAI

- Abdullahi ɗan mas'ud ya ga wasu mutane sun yi halƙa a masallaci sun riƙe tsakuwowi, ɗaya daga cikinsu yana basu umarni ya ce ku yi tasbihi adadi kaza, ku yi kabbara adadi kaza..., sai ya tsawatar musu ya musu Inkari yana cewa: ko dai kuna kan hanyar da ta fi ta Annabi Muhammad (SAW) ko kuma kun ƙirƙiro hanyar ɓata, a wata riwayar ya ce, lallai kun zo da baƙar bidi'a (Ibnu waddah:22, Musannaf:3/222). To da bidi'a tana shiga gayat ne kawai na shari'a banda wasa'il, da waɗannan sun samu bakin cewa ai taruwan da muka yi da tsakuwowin da muka ɗauka ba shi muka riƙa a matsayin ibada ba, muna yin hakan ne don mu samu nishaɗin yin zikirin, amma kasancewar ba a gayar s**a yi bidi'a ba bai sa abun da s**a yi ya fita daga zargi ba.

- Haka masu yin maulidi suna iya cewa ba taron maulidi muka riƙa a matsayin ibada ba, muna yi ne a matsayin hanyar tunatar da mutane sirar Annabi (SAW) da koyar da su soyayyarsa.

Fassara daga littafin "Hukuncin fitar mace da'awa daga fatawowin Shaikh Albani" na malama s**aina, ƴar Muhd Nasiruddinil Albani, Allah ya musu rahama, P49-54

TAƘAICEWA (Mallam Bahaushe)

- Shari'a ta umarci mata da yin wa'azi da karantarwa k**ar yadda ta umarci maza, sai dai wa'azi da karantarwar mace ya bambanta da na miji, na namiji a sake yake babu wani ƙaidi, na mace kuma akwai nau'ika na togaciya a ciki.

- Asali ga mace shi ne ta zauna a gida ta kula da gida tarbiyyar yara, ta yi karatu da karantarwarta a cikin gidan, amma yana halatta idan da buƙata ta je ɗaukar karatu a masallaci ko wani waje daga malami namiji amintacce, ko mace, a wajen da yake na mata zalla kuma ba shige da ficen maza ko cuɗanya da maza a wajen.

- Ba ya halatta mace ta karantar a masallaci ko ta dinga tafiye-tafiye don wa'azi da karantarwa, don ba a samu haka ba a zamanin Annabi (SAW) tare da cewa akwai mata masu ilimi da suke karantarwa amma ba a musu majalisi a masallaci ba, kuma ba su fita ko an tura su yawon da'awa ba, tare da cewa an yi ta tura maza garuruwa, haka ba su yi majalisi a masallaci ba tare da cewa maza suna yi.

- Duk wata shubuha da za a kawo don halatta waɗannan abubuwan ba karɓaɓɓiya ba ce, dalili shi ne Annabi (SAW) bai aiwatar da hakan ba saboda ba Musulunci ba ne, haka sahabbai da tabi'ai ba su yi ba, kuma kowane mai yin bidi'a yana da irin waɗannan hujjojin.

- Wajibi ne koyi da Annabi (SAW) ba a cikin manufofin shari'a ba kawai, har a cikin hanyoyin cimma manufofin, duk abun da aka ƙirƙiro daga baya da ya saɓa wa shiriyar manzon Allah (SAW), bidi'a ne.

Allah ya sa mu dace.

Mallam Bahaushe

Address

Daura Road Katsina
Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hiznim TV NG posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hiznim TV NG:

Share