Gidauniya Tv

Gidauniya Tv Gidauniya Tv, tasha ce wadda aka buɗe domin yaɗa labarai, tsokaci, fashin baƙi kan al'amuran yau

19/07/2025
Kada Ku Sake Yin Amfani da Mutuwar Buhari Don Cimma Manufarku Ta Siyasa — Inji Matasan Arewa, Yayin Gargadi Ga Atiku da ...
19/07/2025

Kada Ku Sake Yin Amfani da Mutuwar Buhari Don Cimma Manufarku Ta Siyasa — Inji Matasan Arewa, Yayin Gargadi Ga Atiku da Nasir El-Rufai

Kungiyar Matasa Ta Arewa (Northern Youth Frontiers) ta bayyana damuwarsu kan yadda wasu 'yan siyasa ke ƙoƙarin amfani da rasuwar tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari domin yaudarar mutane da neman samun goyon bayansu.

A cewar kungiyar, Atiku Abubakar da Nasir El-Rufai sun nuna kamar su abokai ne na Buhari domin su karɓi ƙaunar jama'a, alhali sun shafe shekaru suna adawa da akidu da manufofin Buhari tun yana raye.

Wannan abin da suke yi ruɗi ne, karya ce, kuma cin fuska ne ga marigayin shugaban da ya sadaukar da rayuwarsa ga ƙasar nan.

Kungiyar ta ce waɗannan 'yan siyasa ba su taɓa goyon bayan Buhari ba, kuma yanzu suna ƙoƙarin nuna soyayya ta bogi domin su karɓi ra'ayin mutanen Arewa — musamman bayan mutuwar sa.

“Matasan Arewa ba za su bari a ci zarafin Buhari ba.”

Matasan sun ce ba za su yarda a yi amfani da mutuwar Buhari a matsayin hanyar da za a fake domin yaudarar al’umma ba. Sun kuma roƙi jama’ar Arewa da su yi hankali da siyasar ruɗu da wasu ke ƙoƙarin kawowa a cikin lokaci mai muhimmanci na jimami da girmamawa.

Mutuwar Buhari ba siyasa bace. Lokaci ne na tunani da haɗin kai, ba na neman karɓuwa da nuna ƙarya ba.”

Kungiyar ta ƙara da cewa Atiku da El-Rufai su dakata da wannan salon siyasa, su girmama Buhari, su kuma bar mutanen Arewa su zaɓi gaskiya da amintattu, ba masu nuna soyayya ta ɗan lokaci ba.

Ku dakata da fakewa da mutuwar Buhari. Mutumin da kuka ƙi a raye, ba ku da ikon fakewa da shi bayan ya rasu.

Daga Northern Youth Frontiers, a wani saƙon Gargaɗi daga Matasan Arewa.

Ba Za Mu Lamunci Atiku Da El-Rufai Su Siyasantar Da Mutuwar Buhari Ba, Tare Da Cin Moriyar Mutuwar A Wajen Zaman Makokin...
18/07/2025

Ba Za Mu Lamunci Atiku Da El-Rufai Su Siyasantar Da Mutuwar Buhari Ba, Tare Da Cin Moriyar Mutuwar A Wajen Zaman Makokinsa Ba, Cewar Kungiyar DWI

Kungiyar Democracy Watch Initiative (DWI) ta bayyana matuƙar ɓacin ranta da yadda Atiku Abubakar da Nasir El-Rufai s**a nuna halayen son zuciya da ƙaŕaiŕàyi a lokacin jana’izar tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari. A yayin da mutane ke cikin alhini, su kuma sun sauya jana’izar zuwa wata dama ta siyasa don yaudarar jama’a da neman tagomashi.

Atiku da El-Rufai sun nuna kansu kamar su ne masoyan Buhari na hakika, alhali tarihi ya tabbatar da cewar sun sha s**a da yakar manufofinsa da akidunsa. Wannan yunkuri nasu, ba wai kawai rashin gaskiya ba ne, har ma da rashin mutunta irin gudunmawar da Buhari ya bayar ga ƙasa, da kuma wulakanta ra’ayin al’umma da ke makoki.

Ya kamata a tuna cewa Atiku ya fara zama babban abokin adawar Buhari tun shekarar 2003, inda ya tsaya takara da shi a zaɓuka da dama. A tarihi, Atiku yana canza jam’iyya bisa la’akari da ribar kansa, ba don wata akida ba. Ya bar PDP ya koma APC lokacin da Buhari ke da tasiri, sannan ya sake komawa PDP da zarar Buhari ya ci zaɓe. Wannan yana nuna halin rashin gaskiya da son zuciya da ke tattare da siyasar Atiku.

A gefe guda kuwa, El-Rufai wanda ya dade yana jinƙayar Buhari da jama’arsa, ya bayyana a jana’iza yana kokarin nuna wata tsantsar goyon baya da ba ta taɓa kasancewa da shi ba. Wannan hanya ce ta neman amincewa da mutanen Arewa cikin lokaci mai rauni da radadi.

Kungiyar DWI tana kira ga al’ummar Najeriya musamman ‘yan Arewa da su kasance masu hankali da fahimta. Kada mu bari wasu yan siyasa su ci moriyar makokinmu da tarihin mutanen kirki kamar Buhari. Ya kamata a tuna da makircin da waɗannan mutane s**a aikata a baya da kuma yadda s**a kasance masu son kansu da rashin kishin kasa.

DWI tana nan daram a kan matsayinta na cewa siyasar yaudara ba za ta samu karbuwa ba. Muna roƙon kowa da kowa da ya mutunta rayuwa da gado da Buhari ya bari – rayuwar gaskiya, tsantseni da kishin kasa.

A ƙarshe, muna tir da yunkurin Atiku Abubakar da Nasir El-Rufai na sauya jana’izar Buhari zuwa dandamalin siyasa. Muna kira da a ci gaba da tuna irin gudunmawar Buhari ba tare da bari wasu su yi amfani da sunansa don biyan bukatunsu na siyasa ba.

Democracy Watch Initiative

Duk Wanda zai Kare Muhammad Buhari Ya bari Sai Munje kiyama A Gaban Allah Ina Jinin Mahaifina da Aka kashe a 2020.Ra'ayi...
15/07/2025

Duk Wanda zai Kare Muhammad Buhari Ya bari Sai Munje kiyama A Gaban Allah Ina Jinin Mahaifina da Aka kashe a 2020.

Ra'ayin Comrd Younusa mukhtar yankara

Sabuwar Jarida Mai Suna "Latest Post "Ku yi Following din shafin jaridar domin samun ingantattun labarai na yankin Arewa...
06/07/2025

Sabuwar Jarida Mai Suna "Latest Post "

Ku yi Following din shafin jaridar domin samun ingantattun labarai na yankin Arewa;

👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

https://www.facebook.com/share/1HkTF3jab3/

" Latest Post " Sabuwar jarida ce da zata dinga kawo muku ingantattun labaran yankin Arewacin Najeriya tare da sharhi fashin baki, wayar dakan al-ummar yankin, kan dukkannin wani abu da ya shige musu duhu.

Haka zalika jaridar zata dinga baku dama wurin isarda sakonninku zuwa ga inda kuke bukatan isarwa cikin sauki.

Muna Addu'ar Allah ya bamu sa'a da Nasara, mu gabatar da ayyukanmu cikin gaskiya da tsoron Allah. Amin

Abun Birgewa: Makarantar Zagami Academy Yankara, ta Gwangwaje Hon.Sirajo Aliyu da lambar Yabo.Daga Comrd Younusa mukhtar...
02/07/2025

Abun Birgewa: Makarantar Zagami Academy Yankara, ta Gwangwaje Hon.Sirajo Aliyu da lambar Yabo.

Daga Comrd Younusa mukhtar yankara.

A safiyar Yau Labara tawagar Makaranta Zagami Academy Dake cikin Garin Yankara, tayi Dirar Mikiya inda takai ziyarar koyan Aikin shugabanci a Karamar hukumar faskari, inda Nan take s**a Mika lambar Yabo ga shugaban karamar hukumar faskari Hon.Sirajo Aliyu Daudawa lambar Yabo data shafi Jinjina bisa yadda yake tafiyar da jagoranci Al'umma cikin salon na Ilimi, Hankali, da Tausayawa ga Al'umma.

Tawagar Dalibai sun Samu Kai ziyarar ne tare da shugaban nasu wato (Principal) Mallam Abba Yusif Abubakar (jakade) tare da sauran mallamai Wanda s**a Bawa Mai Girma Sabon zababben shugaban karamar hukumar faskari Lambar Yabo tare da Jinjina bisa yadda yake ta Kokari a fannin Ilimi domin Samun ingaantaccen Ilimi a Karamar hukumar faskari da sauran Ayyukan Alkairi da Gudumuwa Dake Baiwa Al'umma.

Makarantar ta Zagami Academy Yankara, ta Yaba Masa sosai tare da mataimakin sa Hon.Isiyaku wada faskari, matuka tare da yi Masa Addu'a cigaba da irin wadannan Ayyukan Alkairi da yake yi ma Al'umma babu dare, babu Rana, Sannan Daliban sun Samu kyakyawar tarba da masauki na musamman da Kuma nuna Masu Hanyoyin da Ake Gudanar da shugabanci a matsayin su na Dalibai kuma (Manyan Gobe) insha Allah

Daga
Comrd younusa Mukhtar (Mai zamani)

Abun birgewa.Wurin cin abinci a sararin samaniya da ke a kasar Armenia. Akwai irin shi a Wasu Kasashen kamar Dubai. Yaus...
28/06/2025

Abun birgewa.

Wurin cin abinci a sararin samaniya da ke a kasar Armenia. Akwai irin shi a Wasu Kasashen kamar Dubai. Yaushe za mu samu irin wannan a kasar mu.

Allah Ya Jiƙanƙa Da Rahma, Alhaji Aminu dantata ya rasu yana da shekaru 94 a duniya
28/06/2025

Allah Ya Jiƙanƙa Da Rahma, Alhaji Aminu dantata ya rasu yana da shekaru 94 a duniya

27/06/2025

Wani ATTAJIRI ya bawa LIMAN 1 Million domin fentin MASALLACI da saka SOLAR, LIMAN kuma ya sayo MASARA ya rabawa MASALLATA! Me za ku ce 🤔

Ku shirya a wannan shafin namu za mu yi irin wannan giveaway din 👇 masu goyon baya su danna mana like👍.
26/06/2025

Ku shirya a wannan shafin namu za mu yi irin wannan giveaway din 👇 masu goyon baya su danna mana like👍.

Ra'ayin Comrd Younusa mukhtar yankara  Muna Kira ga Hon.Hamza Sule Wambai daya Amsa Kiran Al'ummar Funtua Zone Dan Allah...
26/06/2025

Ra'ayin Comrd Younusa mukhtar yankara

Muna Kira ga Hon.Hamza Sule Wambai daya Amsa Kiran Al'ummar Funtua Zone Dan Allah domin irinsa Al'umma suke Bukatar a wannan Lokacin domin fitar dasu Daga Halin da Suke cikin a wannan Lokacin.

Muna Masu kara kira da Babbar Murya ga Commissioner Muhali na Jahar Katsina da ya Dubi Girman Allah ya Tsaya takarar senator a shekarar 2027 domin kowa yasan irin Taimako da yake yi ma Al'umma babu dare, babu Rana Kullum Fadi Tashi yake wajen Kare Mutuncin Al'umma Yankun Nan funtua Zone

Munsan shi Mutum ne Mai Tausayi da Karbar koken Al'umma Muna Fatan ya Duba irin Halin Tausayi da Al'umma Suke ciki ya Tausaya Masu ya Tsaya takarar senator domin kawo cigaba Iri Iri da zasu kawo cigaba da Al'umma zasu Samu saukin Rayuwa ko Kuma mu Maka shi koto idan Bai Karbi koken Al'umma wannan shine.

Ra'ayin.
Comrd Younusa Mukhtar Yankara

Kalaman shugaban ƙasar Amurka Donald Trump ya ba mutane mamaki inda aka jiyo shi yana cewa "Lallai Isra'ila ta daku Sosa...
25/06/2025

Kalaman shugaban ƙasar Amurka Donald Trump ya ba mutane mamaki inda aka jiyo shi yana cewa "Lallai Isra'ila ta daku Sosai a hannun Iran musamman a yan kwanakin ƙarshen nan". Ana ganin Kalaman ba za su yiwa shugaban ƙasar Isara'ila daɗi ba saboda yanda yake nuna cewa ba su wani yi asara ba a yaƙin su da Iran.

Tun Ba yanzu ba dae ana ganin shugaban ƙasar Amurka Donald Trump a matsayin mutum wanda ba a sirri da shi. Da zarar ya fito waje yake sakin baki.

Address

Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Gidauniya Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Gidauniya Tv:

Share