Gidauniya Tv

Gidauniya Tv Gidauniya Tv, tasha ce wadda aka buɗe domin yaɗa labarai, tsokaci, fashin baƙi kan al'amuran yau
(1)

05/05/2025

Ikon Allah!

Katafaren ginin gidan alfarma kenan da Kauran Bauchi ya ginawa kansa don jindadinsa yayin da al'ummar Bauchi ke cikin kunci da tsananin talauci.

Shin wane shugaba ke irin wannan?

Katsinawa sun nuna kauna ga Shugaba Tinubu a jiya Juma'a.
03/05/2025

Katsinawa sun nuna kauna ga Shugaba Tinubu a jiya Juma'a.

Ministan Tsaron Nigeria, Mohammed Badaru Abubakar, Ya Karɓi Baƙuncin Wakilin Majalisar Ɗinkin Duniya Kan Harkokin Jinƙai...
30/04/2025

Ministan Tsaron Nigeria, Mohammed Badaru Abubakar, Ya Karɓi Baƙuncin Wakilin Majalisar Ɗinkin Duniya Kan Harkokin Jinƙai

A ranar Talata, 29 ga Afrilu 2025, mai girma Ministan Tsaro na Ƙasa, H.E. Mohammed Badaru Abubakar, CON, mni, ya karɓi baƙuncin Mr. Mohamed Malick Fall, wanda shi ne Wakilin Majalisar Ɗinkin Duniya a Najeriya kuma mai kula da harkokin jinƙai.

Tattaunawar wanda aka gudanar a ofishin Ministan dake Ship House, Abuja, ta mayar da hankali ne kan yadda Najeriya za ta ƙara tallafawa ayyukan jinƙai da Majalisar Ɗinkin Duniya ke gudanarwa a ƙasar.

Wasu Manyan Jiga-Jigan jam'iyyun APC da PDP Sun Kammala Shiryin Sauya Sheka Zuwa SDP a Katsina - Inji Shugaban Jam'iyyar...
16/04/2025

Wasu Manyan Jiga-Jigan jam'iyyun APC da PDP Sun Kammala Shiryin Sauya Sheka Zuwa SDP a Katsina - Inji Shugaban Jam'iyyar, Alhaji Bello Adamu Safana

Jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) reshen Jihar Katsina ta bayyana cewa wasu manyan jiga-jigan jam’iyya mai mulki ta APC da kuma jam’iyyar adawa ta PDP sun kammala shirye-shiryen sauya sheƙa zuwa jam’iyyarsu a jihar.

Shugaban jam’iyyar SDP na jihar, Bello Adamu Safana, ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a yammacin ranar Talata a ofisoshin jam'iyyar dake cikin birnin Katsina.

A cewar sa, za a karɓi waɗannan mutane da ake tsammanin za su sauya sheƙa daga APC, PDP, da sauran jam’iyyu a cikin kankanin lokaci.

Alhaji Bello Adamu Safana ya kuma yi kashedi ga mutane da ƙungiyoyi da ake zagayawa a jihar suna ba mutane muƙamai a faɗin jihar da sunan jam’iyyar adawa ta SDP, inda ya ƙara da cewa dokokin jam’iyyar ba su ba da damar hakan ba.

Ya kuma cigaba da cewa duk wani tsari da waɗanda ba mambobin jam’iyyar ba s**a kafa ba akan doka yake ba, shugaban SDP na jihar ya ce jam’iyyar ba za ta yi jinkirin gurfanar da duk wanda aka samu da laifi ba.

A wani labarin kuma, Alhaji Bello Adamu Safana ya bayyana cewa a halin yanzu jam’iyyar na ba da katin zama ɗan jam’iyya na wucin gadi ne, amma nan da kwanaki 14 masu zuwa, za ta fara ba da katin jam’iyya na dindindin ga mambobin da s**a cancanta.

Me za ku ce kan ajiye mukamin da Dr Hakeem Baba Ahmed yayi?Dr Hakeem Baba Ahmed, shine tsohon mai magana da yawun kungiy...
04/04/2025

Me za ku ce kan ajiye mukamin da Dr Hakeem Baba Ahmed yayi?

Dr Hakeem Baba Ahmed, shine tsohon mai magana da yawun kungiyar Dattawan Arewa, shine za kuji kullum yana kalubalantar Gwamnati a duk inda tayi kuskure a gidajen Rediyo da Television da kafofin sada zumunta.

Tun ranar da Tinubu ya bashi mukamin mai bashi shawara ya turashi Ofis din Kashim aka daina jin duriyarshi, ya daina cewa komai akan sha'anin kasar.

Yasha caccaka da shagube iri-iri a wurin al-umma, yau da safe kwatsam sai ga sanarwar ya ajiye mukaminshi a jaridar Daily Trust.

Ministan Tsaron Najeriya Ya Kai Ziyara Depot Na Sojojin Najeriya Dake Garin ZariyaMai Girma Ministan Tsaro, Mohammed Bad...
25/03/2025

Ministan Tsaron Najeriya Ya Kai Ziyara Depot Na Sojojin Najeriya Dake Garin Zariya

Mai Girma Ministan Tsaro, Mohammed Badaru Abubakar CON, mni, ya kai ziyarar tantancewa ta yini guda a Depot na Rundunar Sojojin Najeriya da ke Zariya a yau, Talata, 25 ga Maris, 2025.

A yayin ziyarar, Minista da tawagarsa sun samu cikakken bayani daga Kwamandan Depot, Manjo Janar AB Mohammed, kan tsarin aiki, gudanar da ayyuka, da horon da ake bai wa sojoji a cibiyar.

Cikin tawagar Ministan akwai Sakataren Dindindin na Ma’aikatar Tsaro, Ambasada Gabriel Tanimu Adudu; Mai Ba da Shawara Kan Fasaha, Janar AT Jibril (Rtd); da Babban Jami’in Ma’aikata, Birgediya Janar AA Garba.

Mati Ali
PA Media & Publicity to the Hon Minister of Defense.

Tinubu Ya Ƙuduri Aniyar Inganta Tsaro Tare Da Bayar Da Horo Na Musamman Ga Sojojin Najeriya ~ Badaru Ministan Tsaro, Moh...
24/03/2025

Tinubu Ya Ƙuduri Aniyar Inganta Tsaro Tare Da Bayar Da Horo Na Musamman Ga Sojojin Najeriya ~ Badaru

Ministan Tsaro, Mohammad Badaru Abubakar, ya bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu na kokarin samar da kayayyakin yaki na zamani, don inganta jin dadin jami’an tsaro, da basu horo na musamman domin inganta tsaro a Najeriya.

Ya bayyana hakan ne yayin kaddamar da horon Special Operations Force a Jaji, Kaduna, wanda za'a horas da sojoji dabarun yaki na zamani, yakar ta’addanci, leken asiri, da ceto mutanen da aka yi garkuwa da su.

Shirin zai fara da dakaru 800 daga cikin jimillar 2,400 da ake sa ran horaswa, kuma gwamnatin Tinubu ta kuduri aniyar samar da makamai, na’urorin leken asiri, da horas da sojoji kan sabbin dabaru.

Badaru ya jaddada cewa wannan horo zai karfafa tsaro, kare ‘yancin kasa, da kuma tabbatar da zaman lafiya a Najeriya da makwabtanta. Ya bukaci dakarun da ake horaswa su jajirce, domin su zama garkuwa ga kasa.

Mati Ali
PA Media & Publicity to the Hon. Minister

Sabuwar Jam'iyyar Maja Ta Su El-Rufai Da Atiku Yaudara Ce Ba Talakawa Ne A Gabansu BaGamayya ce ta masu neman muƙami da ...
22/03/2025

Sabuwar Jam'iyyar Maja Ta Su El-Rufai Da Atiku Yaudara Ce Ba Talakawa Ne A Gabansu Ba

Gamayya ce ta masu neman muƙami da mulki da neman takara, ba al'umma ko talakawa ne a gabansu ba.

Ya ku al’ummar Arewa, ku dubi halin da ake ciki ku tambayi kanku, shin har yanzu za mu ci gaba da bari wasu ‘yan siyasa su rika amfani da mu don biyan bukatunsu? Yanzu da aka saka dokar ta ɓaci a Jihar Rivers, sai gashi Nasiru El-Rufai da Atiku Abubakar sun hada kansu da wasu domin su caccaki gwamnatin Tinubu.

Ina s**a kasance lokacin da ake kashe al’ummar mu a Kaduna, Katsina, Zamfara, Kebbi da Sokoto? A lokacin da aka yi ta satar mutane, garkuwa da su, da hallaka iyayenmu da ‘ya’yanmu, ina ku ke? El-Rufai, kana gwamnan Kaduna, lokacin da garkuwa da mutane ya zama ruwan dare a jiharka, ba ka taba yin taron manema labarai domin nuna damuwarka ba. Atiku, lokacin da kake cikin gwamnati a baya, ba ka taba kokarin kawo mafita ga Arewa ba.

Amma yau da aka cire gwamnan Rivers, sai gashi kun fito kuna ihun adalci! Shin, lokacin da kuka ke mulki Atiku yana mataimakin shugaban kasa, ba kun cire gwamnonin jihohi kamar Bayelsa da Plateau ba? El-Rufai da Atiku, lokacin da kuka ke mulki a zamanin Obasanjo, har gwamnonin jihohi uku kuka tsige! To me yasa a lokacin hakan ya zama daidai, amma yanzu da Tinubu ya yi, sai ku ce rashin adalci ne? To menene banbancinku da shi Tinubu ɗin, ko dan shi daga Kudancin Najeriya yake, ku kuma daga Arewa?

Shin me kuka yi lokacin da aka cire tallafin man fetur? Me yasa baku taba yin magana ba lokacin da aka jefa talaka a cikin wahala? Domin kun san cewa baku ne za ku sha wahalar ba, shiyasa kuka yi shiru. Amma yanzu da bukatarku ta taso, sai gashi kun fara taron manema labarai da shirye-shiryen kafa wata jam’iyyar maja.

Atiku da El-Rufai, kuna son sake hada wata jam’iyyar maja domin me? Ba ku ne kuka kafa APC ba? Ba ku ne kuka ce ita ce mafita ga Najeriya ba? Yanzu da ku ka gaza cimma burin ku, sai ku dawo kuna kokarin yaudarar mutane da wata sabuwar jam’iyyar?

Ya ku ‘yan Arewa, muna gane wasan waɗannan mutanen, ka da mu sake bari su yi amfani da mu don biyan bukatunsu karshe su watsar damu. Mun koyi darasi daga baya, kuma wannan karon, ba za mu bari su yi amfani da mu ba!

Ra'ayin Comr Haidar H Hasheem

Haɗin Gwiwa Don Cigaban Kasa:Maigirma Ministan Tsaro ya gana da Ministan Kudi domin inganta hadin kai tsakanin ma’aikatu...
21/03/2025

Haɗin Gwiwa Don Cigaban Kasa:

Maigirma Ministan Tsaro ya gana da Ministan Kudi domin inganta hadin kai tsakanin ma’aikatun gwamnati don inganta tattalin arzikin kasa da tsaro

Mai Girma Ministan Tsaro, H.E. Mohammed Badaru Abubakar, CON, mni, ya kai ziyarar girmamawa ga Mai Girma Ministan Kudi, Mista Adebayo Olawale Edun, a ofishinsa da ke Ma’aikatar Kudi ta Tarayya, Abuja, a yau Juma’a, 21 ga Maris, 2025. Taron ya mayar da hankali ne kan karfafa hadin gwiwar ma’aikatu don ci gaban kasa.

Najeriya Za Ta Samar Da Sabbin Dabarun  Kwarewa Kan Tsaro, Noma da Hadin Gwiwar Soji da Bangladesh – BadaruMinistan Tsar...
21/03/2025

Najeriya Za Ta Samar Da Sabbin Dabarun Kwarewa Kan Tsaro, Noma da Hadin Gwiwar Soji da Bangladesh – Badaru

Ministan Tsaron Najeriya, Mai Girma Mohammed Badaru Abubakar CON, mni, ya bayyana cewa Najeriya za ta raba kwarewa da Bangladesh a bangaren tsaro, noma da hadin gwiwar soji.

Wannan hadin gwiwar zai ba da damar shigar da jami’an soja cikin wasu sassan da ba na yaki ba, kamar noma, gine-gine, da ci gaban ababen more rayuwa.

Manufar wannan tattaunawa ita ce tabbatar da cewa jami’an soja suna da ayyukan da za su rika yi a lokutan da ba a fuskantar yaki, wanda hakan zai taimaka wajen bunkasa tattalin arzikinsu da kuma ci gaban kasa gaba daya.

Tattaunawar hadin gwiwar ta gudana ne yayin ziyarar girmamawa da Mansur Rahman, Jakadan Bangladesh a Najeriya, ya kai a Ship House, Abuja. Taron ya jaddada damar da ke akwai na amfanuwa daga irin wannan musayar kwarewa tsakanin kasashen biyu.

Minista Badaru ya jaddada cewa wannan hadin gwiwa a fannin tsaro da noma zai ba wa jami’an soja damar yin ayyukan da za su bunkasa basirarsu da kuma ci gaban al’ummarsu.

A nasa jawabin, Jakadan Bangladesh, Mansur Rahman, ya nuna goyon bayansa ga wannan tsari, yana mai cewa shigar da jami’an soja cikin ayyukan farar hula zai taimaka wajen dorewar ci gaba da daidaiton tattalin arziki. Ya kuma bayyana cewa hadin gwiwar bangaren tsaro na iya taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa tattalin arziki na Najeriya.

Wannan hadin gwiwa yana nuni da jajircewar Ma’aikatar Tsaro wajen kirkiro sabbin dabaru da za su inganta rayuwar jami’an soji da kuma ci gaban Najeriya gaba daya.

Mati Ali
PA Media & Publicity to the Hon. Minister

Ba Zamu Lamunci Bita Da Ƙullin Da Hukumar EFCC Ta Ke Yiwa Gwamnan Bauchi Ba - BATAFitacciyar Kungiyar Nan BATA Ta Caccak...
21/03/2025

Ba Zamu Lamunci Bita Da Ƙullin Da Hukumar EFCC Ta Ke Yiwa Gwamnan Bauchi Ba - BATA

Fitacciyar Kungiyar Nan BATA Ta Caccaki Hukumar EFCC Kan Binciken Zargin Badakala Na Kimanin Biliyan 70 A Gwamnatin Jihar Bauchi

Kungiyar Bauchi Accountability and Truth Awareness Front (BATA) ta soki hukumar EFCC kan binciken da take yi a kan wasu jami’an gwamnatin Bauchi, tana zarginta da amfani da binciken a matsayin wata makarkashiya ta siyasa.

K**a Alhaji Sirajo Mohammed Jaja, Babban Akanta na Jihar Bauchi, ya haifar da cece-kuce, inda BATA ta bayyana binciken zargin almundahanar Naira biliyan 70 a matsayin yunkurin da aka shirya don rage darajar gwamnatin Gwamna Bala Mohammed.

“Wannan ba maganar gaskiya ba ce, siyasa ake yi,” in ji Lawal Sani Ningi, Shugaban BATA. Kungiyar ta zargi EFCC da tsara wannan bincike a daidai lokacin da ake fuskantar manyan batutuwan siyasa a jihar, abin da ke kawo shakku kan sahihancin binciken.

Gwamna Bala Mohammed na Cikin Kaka-Nika-Yi

BATA ta nuna damuwa kan yadda EFCC ta ke kokarin danganta binciken da Gwamna Bala Mohammed. Kungiyar ta bayyana wannan mataki a matsayin wata dabara da za ta kau da hankalin jama’a daga ci gaban da gwamnan ke samu a bangaren mulki, gina abubuwan more rayuwa da jin dadin al’umma.

“Gwamnan ya kasance mai kishin jama’a, kuma wadannan zarge-zarge marasa tushe na kokarin hana mutane ganin nasarorinsa,” in ji Ningi.

Kungiyar ta jaddada cewa, yaki da cin hanci da rashawa dole ne a gudanar da shi bisa adalci da gaskiya. Ta zargi EFCC da kasa gabatar da kwakkwaran shaidar da ke tabbatar da zargin da take yi, tana mai cewa binciken ya dogara ne kacokan kan zato da jita-jita.

Kira Ga Adalci da Farkar da Jama’a

BATA ta bukaci EFCC da ta yi aiki bisa ka’idojin adalci da gaskiya, tana rokon hukumar da ta sake duba hanyoyin da take bi. Kungiyar ta kuma yi kira ga al’ummar Bauchi da su kasance masu lura tare da gujewa yaudarar jita-jita.

“Mutanen Bauchi sun cancanci shugabanni da za a auna su bisa ayyukansu na jin dadin al’umma, ba tare da tsoma siyasa a lamarin su ba,” in ji kungiyar.

BATA ta jaddada goyon bayanta ga Gwamna Bala Mohammed da sauran jami’an jihar, tana mai alkawarin ci gaba da fafutukar ganin an samu gaskiya da adalci a tafiyar da shugabanci.

Wannan cece-kuce na kara tayar da muhawara kan rawar da siyasa ke takawa a yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya, inda da dama ke tambayar ko ana yin adalci ko kuma ana amfani da wannan yaki don biyan bukatun wasu ’yan siyasa.

Ka Nesanta Kanka Da Rikicin Siyasar Wike ~ Gargadin CNG Ga Tinubu Gamayyar Kungiyoyin Arewa (CNG) ta bukaci Shugaba Bola...
19/03/2025

Ka Nesanta Kanka Da Rikicin Siyasar Wike ~ Gargadin CNG Ga Tinubu

Gamayyar Kungiyoyin Arewa (CNG) ta bukaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya tabbatar da cewa rikicin siyasa da ke tattare da Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, bai shafi tafiyar da mulkinsa ba.

Wannan kiran ya biyo bayan dakatar da Gwamnan Jihar Ribas da mataimakinsa da Shugaba Tinubu ya yi a daren Litinin.

A cikin wata sanarwa da Shugaban CNG na Ƙasa, Jamilu Aliyu Charanchi, ya sanyawa hannu, kungiyar ta bayyana cewa dabarun siyasar Wike ba su wakiltar muradin al’ummar Jihar Ribas ko na yankin Niger Delta gaba ɗaya ba, illa son zuciya da rashin son zaman lafiya.

Muna kira ga Shugaba Tinubu da ya fahimci cewa ayyukan Wike sun fi karkata ne ga burin kansa fiye da muradun jama’a.

Yana da matuƙar muhimmanci a tabbatar da bin ƙa’idojin dimokuradiyya da doka, maimakon yin biyayya ga ɗan siyasar da ke neman moriyar kansa,” in ji Charanchi.

CNG ta bayyana matsalar da Wike ke jefa siyasar Najeriya a ciki a matsayin babbar gwaji ga jagorancin Tinubu. Kungiyar ta ce hanyar da za a bi don rage tasirin Wike ita ce samar da haɗin kai da aiki tare domin gina kyakkyawar makoma.

Duniya na sa ido don ganin irin matakan da Shugaba Tinubu zai ɗauka wajen tabbatar da shugabanci nagari da kuma cika burin ‘yan Najeriya,” in ji sanarwar.

Kungiyar ta kuma yi kira ga masu ruwa da tsaki, ciki har da ƙungiyoyin fararen hula, ‘yan siyasa da jama’a, da su fifita zaman lafiya da dimokuradiyya a maimakon tada zaune tsaye.

Wannan rikicin ya zama gargaɗi ga kowa da kowa cewa ya kamata mu fifita tattaunawa da fahimtar juna a maimakon rikici da rarrabuwar kai,” CNG ta ƙara da cewa. Ta kuma gargaɗi Shugaba Tinubu da ya yi hattara kada ya bari alaƙarsa da Wike ta haifar da barazana ga zaman lafiyar ƙasa.

Ba za mu yarda burin mutum guda ya jefa ƙasar nan cikin rudani ba. Muna shirye mu goyi bayan duk wani mataki da zai inganta zaman lafiya da jin daɗin ‘yan Najeriya,” in ji sanarwar.

CNG ta jaddada cewa rikicin da ke faruwa na iya yin illa ga tsaron ƙasa da tattalin arziƙi.

Ayyukan mutum guda bai kamata su zama abin da zai rinjayi alkiblar ƙasa gaba ɗaya ko su hana aiwatar da manufofin da za su amfanar da jama’a,” CNG ta jaddada.

Sanarwar ta kuma yi nuni da rawar da Wike ya taka a gwamnatin tsohon Shugaba Goodluck Jonathan, inda ta zargi dabarunsa na siyasa da haddasa matsalolin da s**a kai ga faduwar Jonathan a zaɓe.

Shugaba Tinubu dole ne ya kasance a cikin shiri, musamman ganin yadda al’umma ke sanya ido kan matakan da zai ɗauka dangane da halin da ake ciki a Jihar Ribas,” in ji kungiyar.

Address

Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Gidauniya Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Gidauniya Tv:

Share