Pen times magazine

Pen times magazine Online magazine;News updates/Reportings/Display of passion, history, tourism and more. we are expert on online news

DCP ABBA KYARI YA MUSANTA MALLAKAR KADARORIN DA NDLEA TA DANGANTA DA SHIDakataccen mataimakin kwamishinan ‘yan sanda, Ab...
05/11/2025

DCP ABBA KYARI YA MUSANTA MALLAKAR KADARORIN DA NDLEA TA DANGANTA DA SHI

Dakataccen mataimakin kwamishinan ‘yan sanda, Abba Kyari, ya musanta mallakar wata kaddara da Hukumar NDLEA ta alakanta da shi a shari’ar da ake yi masa kan zargin kin bayyana dukiyoyi.

A zaman kotu na ranar Talata a gaban Mai Shari’a James Omotoso na Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, Kyari ya ce wasu daga cikin kadarorin da ake gardama mallakar mahaifinsa ne marigayi, wanda yake da “’ya’ya kusan 30”.

Tsohon shugaban rundunar IRT ya ce ya yi mamakin zargin da ake yi masa, yana mai cewa takardun kadarorin suna hannun Ma’aikatar Kasa ta Jihar Borno.

Ya kuma musanta mallakar filin wasan polo da aka danganta da shi a Borno, yana mai cewa ba shi da ikon mallakar irin wannan fili mai girma.

“A dukiya irin wacce ake magana a kanta, ma Aliko Dangote, attajirin Najeriya, ba shi da ita; b***e ni,” in ji shi a gaban kotu.

Kyari ya kara da cewa filin polo tun yana yaro yake wanzuwa, “mu kan je mu buga wasa a can tun can.”

Sai dai ya amsa mallakar wani filin gona da ke kan hanyar Abuja–Kaduna, yana mai cewa ya shafe kusan shekaru goma yana kula da gonar.

YANZU YANZU:Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana dokar ta-baci a kan dukkan manyan cibiyoyin horar da jami’an tsar...
04/11/2025

YANZU YANZU:
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana dokar ta-baci a kan dukkan manyan cibiyoyin horar da jami’an tsaro na ƙasar, yana mai cewa kayayyakin su sun tsufa kuma ba sa biyan bukatar zamani.

A sanarwar da fadar shugaban ƙasa ta fitar, an ce dokar ta-bacin ta shafi Makarantar 'Yan Sanda, Hukumar Tsaro ta Civil Defence, da sauran hukumomin tsaro da ke da alhakin samar da horo ga sabbin jami'ai da na keɓantattu.

Shugaban ƙasar ya umurci gwamnonin jihohi da shugabannin hukumomin tsaro da su mika cikakken rahoton matsalolin da cibiyoyin horarwar ke fuskanta cikin kwanaki 30, domin soma aiwatar da gyare-gyare cikin gaggawa.

Fadar ta ce wannan mataki na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da fuskantar ƙalubale na tsaro a sassan ƙasar, musamman batun rashin isasshen horo na zamani ga jami’an da ke yaki da laifuka da ayyukan ta’addanci.

Hukumomin tsaro na ƙasa da jihohi dai sun fara tantance bukatun da za su mika ga gwamnatin tarayya, domin tabbatar da cewa an gina sabbin cibiyoyi tare da inganta na da.

Za mu ci gaba da kawo muku ƙarin bayani yayin da lamarin ke ƙara ɗaukar sabon salo.

YANZU YANZU:Bayan Shiga Yajin aikin likitochi na Gwamnatin tarayya, Yañzu haka  Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya bayar d...
04/11/2025

YANZU YANZU:
Bayan Shiga Yajin aikin likitochi na Gwamnatin tarayya, Yañzu haka Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya bayar da umarnin gaggauta sulhunta matsalolin da s**a kai ga shiga yajin aikin likitoci masu neman ƙwarewa a Najeriya, tare da tabbatar da komawarsu bakin aiki cikin gaggawa.

YANZU YANZU;Shugaban ƙaramar hukumar Safana a Jihar Katsina ya ƙaddamar da masu ba shi shawara mutum 50, tare da biyan s...
04/11/2025

YANZU YANZU;
Shugaban ƙaramar hukumar Safana a Jihar Katsina ya ƙaddamar da masu ba shi shawara mutum 50, tare da biyan su albashin wannan watan nan ta ke.

A ranar litinin 3/11/2025, shugaban ƙaramar hukumar Safana Hon. Abdullahi Sani Safana (Brazil) ya ƙaddamar da masu ba shi shawarar mutum 50, kamar yadda mai girma Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda ya basu umurni.

Shugaban ƙaramar hukumar ta Safana, bayan ƙaddamar da masu ba shi shawarar, ya biyasu albashin wannan watan nan ta ke naira dubu hamsin, hamsin.

Shugaban ƙaramar hukumar ya yi fatan alheri ga masu ba shi shawarar, tare da jan hankalin su dasu jajirce wajen bada shawarwarin da su ka kamata da zasu taimaka wajen ciyar da ƙaramar hukumar Safana gaba.

Taron ƙaddamar da masu bada shawarar ya samu halartar mataimakin shugaban ƙaramar hukumar Hon. Abdullahi Abubakar, shugaban majalisar kansilolin ƙaramar hukumar Hon. Kamaladden Salisu Illela. Da sauran Jami'an Gwamnatin ƙaramar hukumar.

Daga Shafin Mobile Media Crew

INTRODUCTION:Northwest Development Assembly (NWDA) is a platform established by Legislative Aides from the Northwest Sta...
04/11/2025

INTRODUCTION:
Northwest Development Assembly (NWDA) is a platform established by Legislative Aides from the Northwest States of Nigeria.

Its vision is to build a united and progressive Northwest region through accountable leadership and active citizen participation.

The organization aims to promote good governance, strengthen regional development partnerships, and empower communities through advocacy, training, and recognition of excellence. NWDA's core tasks include awarding excellence, youth and leadership training, advocacy and public enlightenment, development dialogue series, documentation, and publications.

The organization seeks to partner with relevant stakeholders to achieve its vision and mission.

LABARI CIKIN HOTUNA:Jiya Litinin 3-11-2025 Mai Girma Shugaban Ƙaramar Hukumar Ɗan-Musa, Hon. Ibrahim Namama Maidabino, Y...
04/11/2025

LABARI CIKIN HOTUNA:
Jiya Litinin 3-11-2025 Mai Girma Shugaban Ƙaramar Hukumar Ɗan-Musa, Hon. Ibrahim Namama Maidabino, Ya Ƙaddamar (Delivery Kids) Guda Diri Ukku, Da Litar Maganin Feshi Guda 1,044. Wanda Za Aba Manoma Kyauta.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Ɗan-Musa, Ya Ƙaddamar Da Wannan (Delivery Kids) Ne Domin Aci Gaba Da Ba Mata Waɗanda S**a Haihu, Kyauta A Asibitocin Ƙaramar Hukumar Ɗan-Musa, Shugaban Ƙaramar Hukumar Ɗan-Musa Honorable Ibrahim Namama Maidabino, Bayan Ya Gama Ganawa Da Kansilolin, Da Al'ummar Da Kuma Tawagar Kungiyar Yan (N.U.T)

Bayan Haka Shugaban Ƙaramar Hukumar Ɗan-Musa Hon. Ibrahim Namama Maidabino, Ya Ƙaddamar Da Bada Maganin Feshi, Kwali Tamanin Da Bakwai, Wanda Yayi Dai-dai Da Litar Maganin Feshi Dubu Ɗaya, Da Dari Huɗu, Da Guda Huɗu, 1,044 Wanda Za'a Rabama Manoma Kyauta A Faɗin Yankunan Ƙaramar Hukumar Ɗan-Musa, Hon. Ibrahim Namama Maidabino, Ya Ƙaddamar Da Wadannan Kaya Ne A Cikin Sakatariyar Ƙaramar Hukumar Ɗan-Musa.

Allah Ya Saka Mashi Da Alkairi, Allah Ya Ci Gaba Da Kara Kawo Mana Ingantaccen Zaman Lafiya Mai Ɗorewa A Yankunan Ƙaramar Hukumar Ɗan-Musa Da Ƙasa Baki Ɗaya.

Daga Shafin Abdulmumin Usman Maidabino

DA DUMI DUMI: Shugaba Tinubu ya bayar da umarnin daina anfani da dalar Amurka wajen sayen tikitin jirgin sama.Ana zargin...
03/11/2025

DA DUMI DUMI: Shugaba Tinubu ya bayar da umarnin daina anfani da dalar Amurka wajen sayen tikitin jirgin sama.

Ana zargin hakan ya biyo bayan tarzomar dake tsakanin Nigeria da kasar Amurika.

Ya kuke kallon wannan mataki

YANZU YANZU:Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!!!Yanzu mu ke samun labarin rasuwar Malam Nata'ala a cikin daren bayan f...
02/11/2025

YANZU YANZU:
Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!!!
Yanzu mu ke samun labarin rasuwar Malam Nata'ala a cikin daren bayan fama da jinya.

Farfesa Sheriff Almuhajir daga jihar Yobe ne ya tabbatar da labarin. Inda ya nuna matuƙar kaɗuwarsa da rsuwar.

DA DUMI DUMI:Sanata Yakubu Lado Dan Marke Ya Ba Da Tallafin Naira Miliyan 220 Ga Masarautar Iyin Kingdom a Jihar EkitiSa...
02/11/2025

DA DUMI DUMI:
Sanata Yakubu Lado Dan Marke Ya Ba Da Tallafin Naira Miliyan 220 Ga Masarautar Iyin Kingdom a Jihar Ekiti

Sanata Yakubu Lado Dan Marke, jagoran talakawan Jihar Katsina, ya bayar da gudunmuwar Naira Miliyan 220 (₦220,000,000) ga Masarautar Iyin Kingdom da ke Jihar Ekiti, tare da tallafin karatu kyauta na tsawon shekaru biyar ga ‘ya’yan masarautar.

Bisa bayanin da Hon. Ghali Salisu Bakori, mashawarci na musamman ga Sanata Lado Dan Marke ya bayyana, an ce daga cikin wannan adadi, Naira Miliyan 200 Sanatan ne ya bayar kai tsaye ga masarautar, yayin da Naira Miliyan 20 ya bayar a madadin ‘yan uwa da abokan arziki.

Sanata Lado ya kuma bayyana cewa tallafin karatun zai gudana ne a karkashin gidauniyarsa mai suna Lado Development Foundation (LDF), domin bai wa dukkan yaran da ke son yin karatu a masarautar damar karatu kyauta tun daga matakin firamare har zuwa jami’a.

Wannan kyauta ta zo ne bayan nadin da Masarautar Iyin Kingdom ta yi masa a matsayin “A’are Atuluse of Iyin Ekiti,” yayin da mai dakinsa Hajiya Zainab Sani Abacha ita ma aka nada a matsayin “Yeyere Atuluse of Iyin Ekiti.”

Masarautar ta bayyana cewa ta girmama Sanata Lado Dan Marke da wannan sarauta ne saboda jajircewarsa, taimako da sadaukarwarsa wajen gina al’umma, ba tare da la’akari da kabila ko bambancin siyasa ba.

Hon. Ghali Salisu Bakori
Mashawarci na Musamman ga Sanata Yakubu Lado Dan Marke

YANZU YANZU: Mai Baiwa Shugaban Kasa Shawara kan Sadarwar Tsari, Daniel Bwala, ya bayyana cewa Shugaban Kasa Bola Ahmed ...
02/11/2025

YANZU YANZU:
Mai Baiwa Shugaban Kasa Shawara kan Sadarwar Tsari, Daniel Bwala, ya bayyana cewa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da Shugaban Amurka Donald Trump za su gana a cikin ‘yan kwanaki masu zuwa domin tattaunawa kan zargin “kisan kiyashin addini” da ake cewa ana yi wa Kiristoci a Najeriya.

A wata sanarwa da ya fitar, Bwala ya ce ganawar za ta mayar da hankali kan yakar ta’addanci, hanyoyin tashin hankali, da kuma nazarin kungiyoyin da ake zargi da aikata ayyukan ta’addanci a sassa daban-daban na ƙasar. Ya ce:

> “Shugaba Tinubu da Shugaba Trump suna da burin karfafa hadin gwiwa wajen yaki da ta’addanci. Ganawar za ta yi nazari kan ko hare–haren sun shafi Kiristoci kaɗai ko kuma al’umma gaba ɗaya.”

A cewar Bwala, zargin da ya taso daga wasu hukumomi da kungiyoyin kasa da kasa game da hare-haren kan Kiristoci ya jawo damuwa mai yawa, musamman daga Amurka, wacce ta zargi Najeriya da rashin daukar matakin da ya dace. Sai dai gwamnatin Najeriya ta dage cewa batun ya ta’allaka ne kan ta’addanci, ba bambancin addini ba.

Har yanzu ba a bayyana takamaiman ranar ganawar ba, sannan ajandar cikakke na tattaunawar bai fito fili ba. Duk da haka, Bwala ya tabbatar da cewa za a gudanar da taron ko dai a Fadar Shugaban Kasa ta Abuja ko kuma a White House a Amurka.

DA DUMI DUMI: Tawagar Hadin Kai ta ziyarci Sheikh Ibrahim Zakzaky a gidan sa dake Abuja. Tawagar Hadin Kai ƙarƙashin jag...
02/11/2025

DA DUMI DUMI:
Tawagar Hadin Kai ta ziyarci Sheikh Ibrahim Zakzaky a gidan sa dake Abuja.

Tawagar Hadin Kai ƙarƙashin jagorancin Imam Prof. Ibrahim Maqari da Sheikh Nur Khalid ta dira a gidan jagoran Harkar IMN, Sheikh Ibrahim Zakzaky, domin gudanar da ziyarar hadin kai da tattaunawa kan hanyoyin da za su kawo daidaito da fahimtar juna tsakanin ‘yan uwa musulmi.

Sheikh Zakzaky wanda aka fi sani da mai son zaman lafiya, an bayyana cewa yana ta jiran irin wannan tawaga wadda za ta taimaka wajen dinke ƙaramin ɓaraka domin kaucewa babba, tare da farfado da zumunci tsakanin malamai da mabiya.

Wasu daga cikin jama’a sun bayyana ziyarar a matsayin sabuwar alama ta haɗin kai da sabuntawar tattaunawa tsakanin manyan malamai a ƙasar.

“Sai yanzu tawagar da nake jira ta iso,” in ji Sheikh Zakzaky cike da farin ciki.

Alamu sun nuna wannan ziyarar na iya zama sabon babi a kokarin haɗa kan musulmi a Najeriya.

02/11/2025

Wache shawara gareku ga Nigeria da Yan Nigeria musamman akan Yunkurin da America keyi na kawo mata hari

Address

Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Pen times magazine posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Pen times magazine:

Share

Category