DanMasani RADIO

DanMasani RADIO DANMASANI ONLINE GLOBAL RADIO. MUN SHIRYA TSAF DOMIN FADAKARWA, ILIMANTARWA DA KUMA NISHADANTARWA.

Yan bindiga sun kashe wanda su ka yi garkuwa da shi bisa rashin isasshen kuɗi a asusun sa na banki Jami’an rundunar yans...
25/09/2025

Yan bindiga sun kashe wanda su ka yi garkuwa da shi bisa rashin isasshen kuɗi a asusun sa na banki

Jami’an rundunar yansandan jihar Delta sun k**a wasu mutane uku da ake zargi da yin garkuwa da wani mutum bayan sun karɓi kudin fansa na Naira miliyan biyu (₦2,000,000) daga hannun sa, amma duk da haka su ka harbe shi.

Wadanda ake zargin, wato Chukwuebuka Nka, mai shekaru 25, Uche Okechukwu, da Somto Chukwuma, sun harbi wanda s**a sace din a ƙafarsa bayan sun gano cewa ba shi da isasshen kuɗi a cikin asusun sa na banki.

A cewar mai magana da yawun rundunar ƴansandan, Bright Edafe, k**a waɗanda ake zargin ya biyo bayan samun rahoton gaggawa cewa wani matashi an sace shi daga gidansa a Ogwashi-Uku.

Ya bayyana cewa jami’an sun bi sahun masu garkuwa da mutane har zuwa daji a Ogwashi-Uku, inda aka ceto wanda aka sace tare da raunin harbin bindiga.

Edafe ya ce bincike ya kai ga k**a Chukwuebuka Nka da Uche Okechukwu a jihar Anambra, inda aka kuma gano motar wanda aka sace din kirar Toyota Venza.

Ya ƙara da cewa bisa ga amsar da waɗanda ake zargin s**a bayar, jami’an ƴansanda sun kai samame matsuguninsu da ke kauyen Agidiase, Ogwashi-Uku, inda aka k**a na ukun.

Masu laifin sun jagoranci ‘yan sanda zuwa maboyarsu, inda aka gano motar da suke amfani da ita wajen aikata laifuka da kuma wata na’urar da ke tare sabis din sadarwa.

Sarkin Daura Ya Nada Mawakin Siyasa Dauda Kahutu Rarara Sarkin Waƙar Ƙasar Hausa.
25/09/2025

Sarkin Daura Ya Nada Mawakin Siyasa Dauda Kahutu Rarara Sarkin Waƙar Ƙasar Hausa.

Rahotanni dake shigo mana sun tabbatar da  DSS sun k**a Sheikh Lawan TruimphWani Fata Kuke Mashi ?
25/09/2025

Rahotanni dake shigo mana sun tabbatar da DSS sun k**a Sheikh Lawan Truimph

Wani Fata Kuke Mashi ?

Za a rufe kasuwanni a Ibadan domin bikin bada sandar sarauta ga OlubadanZa a rufe dukkan kasuwanni a Ibadan, babban birn...
24/09/2025

Za a rufe kasuwanni a Ibadan domin bikin bada sandar sarauta ga Olubadan

Za a rufe dukkan kasuwanni a Ibadan, babban birnin jihar Oyo, a ranar Juma’a domin ‘yan kasuwa su girmama nadin Olubadan na 44 na Ibadanland, Oba Rasheed Adewolu Ladoja.

Jaridar LEADERSHIP ta rawaito cewa Babban Babaloja na Jihar Oyo, Asiwaju Yekeen Abass, ne ya bayar da umarnin, inda ya bayyana cewa rufe kasuwannin zai kasance alamar girmamawa ga sabon sarki.

Abass ya bayyana cewa dukkan kasuwanni da ke cikin kananan hukumomi goma sha ɗaya na Ibadanland, ciki har da na cikin birni da kewaye, za su dakatar da harkokin kasuwanci a wannan rana.

Babban Babaloja ya taya Oba Ladoja murna a madadin majalisar shugabannin kasuwa, shugabannin yankuna da kuma daukacin al’ummar ‘yan kasuwa a jihar Oyo.

Ya yi addu’ar samun zaman lafiya, wadata da mulki mai tasiri wanda zai kawo cigaba ga Ibadanland da jihar baki ɗaya.

Babban Babaloja ya kuma bukaci dukkan ‘yan kasuwa su halarci bukin nadin a Mapo Hall, inda ya jaddada muhimmancin nuna goyon baya da girmamawa ga sabon sarki na gargajiya.

Sarkin Musulmi ya ayyana Talata 23-09-2025 a matsayin 1 ga watan Rabi’ul Assani 1447AHSarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’...
23/09/2025

Sarkin Musulmi ya ayyana Talata 23-09-2025 a matsayin 1 ga watan Rabi’ul Assani 1447AH

Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar ya sanar da ranar Talata, 23 ga Satumba, 2025 a matsayin ranar farko ta watan Rabi’u Assani 1447 bayan hijirar Annabi (SAW).

Sanarwar ta fito ne daga Farfesa Sambo Wali Junaidu, Wazirin Sokoto, wanda shi ne Shugaban Kwamitin Ba da Shawara kan Harkokin Addini na Majalisar Sarkin Musulmi.

Gwamna Dikko Radda Ya Yi Kyakkyawan Albishir Ga Wadanda S**a Hardace Al-Qur'ani A Jihar KatsinaGwamnatin Jihar Katsina t...
23/09/2025

Gwamna Dikko Radda Ya Yi Kyakkyawan Albishir Ga Wadanda S**a Hardace Al-Qur'ani A Jihar Katsina

Gwamnatin Jihar Katsina ta lashi takobin daukar nauyin karatun wadanda s**a hardace Al-Qur'ani domin su yi karatun likitanci da ungozoma a makarantun gaba da sakandire.

Gwamna Dikko Umaru Radda ne ya tabbatar da wannan albishir a lokacin wani taron masu ruwa da tsaki akan yadda za'a inganta harkar karatun tsangaya a Jihar Katsina.

Hukumar Kula Da Kididdiga ta Jihar Katsina(Katsina State Bereau of Statistics) ce ta shirya taron tattaunawar da ya gudana a dakin taro na Hukumar Kula da Ma'aikatan Kananan Hukumomi ta Jihar Katsina.

Kamar yadda Gwamna Radda ya bayyana, Gwamnatin shi zata dauki nauyin mahardata Al-Qur'ani daga farkon karatun su har karshe, a fannin likitanci(Medicine) da kuma Ungozoma(Midwifery).

Daga cikin Malaman Addinin Musulunci da s**a gabatar da Kasidu a yayin taron sun hada da Sheikh Professor Ali Isah Pantami da Sheikh Dr.Aminu Ibrahim Daurawa da dai sauran su.

Sun magantu akan kyakkyawan tsari da ya k**ata a yi wa makarantun tsangaya, domin kyautata jin dadin dalibai don ganin tsarin ya yi dai-dai da zamanin da muke ciki.

22/09/2025

Ku kalli Ruhoto na musamman akan yadda zagayen mauludi ya gudana a jiya lahadi 21/09/2025

Online Radio

Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya k**a hanyar zuwa birnin New York da ke Amurka, domin halartar taron Majalisa...
21/09/2025

Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya k**a hanyar zuwa birnin New York da ke Amurka, domin halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 80. Za a fara taron daga ranar Litinin 22 ga watan Satumba 2025.

(Hoto:Fbk/Kashim Shettima)

Sojojin Saman Nijeriya sun kashe ‘yan ta’adda fiye da 25 a wani samame da s**a kai da cikin dare a yankin Bula na Jihar ...
21/09/2025

Sojojin Saman Nijeriya sun kashe ‘yan ta’adda fiye da 25 a wani samame da s**a kai da cikin dare a yankin Bula na Jihar Yobe da Banki a Jihar Borno da ke arewa maso gabashin ƙasar.

DA DUMI-DUMI: Ta leko ta koma - Daktar da aka bawa Rarara ta bogi ce domin ba daga jami’ar mu bane - inji Jami’ar Europe...
21/09/2025

DA DUMI-DUMI: Ta leko ta koma - Daktar da aka bawa Rarara ta bogi ce domin ba daga jami’ar mu bane - inji Jami’ar European - American University

Daga Ayau News

Jami’ar European American University ta ce bata bawa mawaki Rarara Dakta ba wasu ne kawai s**a wanke shi a Abuja

A sanarwar da jami’ar ta fitar ta ce itama a kafafen yada labaran Najeriya ta ga labarin cewa wai ta karrama Mawaki Dauda Kahutu Rarara da wasu mutane a Najeriya

"to wannan ba gaskiya bane kuma duk mai son tabbatar da labarin zai iya ziyartar shafinmu ya duba, zai ga jerin sunayen mutanen da muka karrama..." inji sanarwar jami’ar

Rahoton Ayau News
Follow us => Ayau News => Taskar Labarai

Wataran Fa Rarara Zai Iya Zama Gwamnan Katsina, Don Babu Ruwan Allah Da Mawaki Ne Ko Ba Mawaki Ba, Cewar Amina Amisco Ad...
20/09/2025

Wataran Fa Rarara Zai Iya Zama Gwamnan Katsina, Don Babu Ruwan Allah Da Mawaki Ne Ko Ba Mawaki Ba, Cewar Amina Amisco Adamu

Rariya

Jami'ar European American da ke Jamhuriyar Panama ta karrama mawaki Dauda Kahutu Rarara da digirin digirgir bisa irin gu...
20/09/2025

Jami'ar European American da ke Jamhuriyar Panama ta karrama mawaki Dauda Kahutu Rarara da digirin digirgir bisa irin gudunmawar da yake bayarwa wajen raya al’adu da tallafawa matasa.

Taron wanda aka gudanar a Abuja ya samu halartar gwamnoni, ministoti da sauran manyan ƴan siyasa.

Wanne fata zaku yi masa?

Address

No. B27. Khalil Raman Shopping Complex. High Court Roundabout. Daura Road Katsina
Katsina
820221

Opening Hours

Monday 10:00 - 18:00
Tuesday 10:00 - 18:00
Wednesday 10:00 - 18:00
Thursday 10:00 - 18:00
Friday 10:00 - 18:00
Saturday 09:00 - 17:00
Sunday 09:00 - 17:00

Telephone

+2348080806872

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DanMasani RADIO posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to DanMasani RADIO:

Share