25/09/2025
Yan bindiga sun kashe wanda su ka yi garkuwa da shi bisa rashin isasshen kuɗi a asusun sa na banki
Jami’an rundunar yansandan jihar Delta sun k**a wasu mutane uku da ake zargi da yin garkuwa da wani mutum bayan sun karɓi kudin fansa na Naira miliyan biyu (₦2,000,000) daga hannun sa, amma duk da haka su ka harbe shi.
Wadanda ake zargin, wato Chukwuebuka Nka, mai shekaru 25, Uche Okechukwu, da Somto Chukwuma, sun harbi wanda s**a sace din a ƙafarsa bayan sun gano cewa ba shi da isasshen kuɗi a cikin asusun sa na banki.
A cewar mai magana da yawun rundunar ƴansandan, Bright Edafe, k**a waɗanda ake zargin ya biyo bayan samun rahoton gaggawa cewa wani matashi an sace shi daga gidansa a Ogwashi-Uku.
Ya bayyana cewa jami’an sun bi sahun masu garkuwa da mutane har zuwa daji a Ogwashi-Uku, inda aka ceto wanda aka sace tare da raunin harbin bindiga.
Edafe ya ce bincike ya kai ga k**a Chukwuebuka Nka da Uche Okechukwu a jihar Anambra, inda aka kuma gano motar wanda aka sace din kirar Toyota Venza.
Ya ƙara da cewa bisa ga amsar da waɗanda ake zargin s**a bayar, jami’an ƴansanda sun kai samame matsuguninsu da ke kauyen Agidiase, Ogwashi-Uku, inda aka k**a na ukun.
Masu laifin sun jagoranci ‘yan sanda zuwa maboyarsu, inda aka gano motar da suke amfani da ita wajen aikata laifuka da kuma wata na’urar da ke tare sabis din sadarwa.