DanMasani RADIO

DanMasani RADIO DANMASANI ONLINE GLOBAL RADIO. MUN SHIRYA TSAF DOMIN FADAKARWA, ILIMANTARWA DA KUMA NISHADANTARWA.

Sarkin Katsina ya naɗa sabbin hakimai 6 a masarautar saMasarautar Katsina ta tabbatar da nadin sabbin Hakimai shida, cik...
02/08/2025

Sarkin Katsina ya naɗa sabbin hakimai 6 a masarautar sa

Masarautar Katsina ta tabbatar da nadin sabbin Hakimai shida, ciki har da Muhammad Dikko Umar Radda, ɗan Gwamnan Jihar Katsina, Mallam Dikko Umar Radda, wanda aka nada da sarautar Hakimin Radda.

Sanarwar nadin ta fito ne daga sakataren masarautar Katsina, Alhaji Bello M. Ifo (Sarkin Yakin Katsina), inda ya bayyana cewa an amince da nadin sabbin hakiman a ranar 2 ga watan Agusta, 2025.

Ga jerin sabbin Hakiman da aka tabbatar kamar haka:
1. Alhaji Sanusi Kabir Usman – Hakimin Shinkafi
2. Alhaji Ahmad Abdulmumini Kabir Usman Dan-Majen Katsina (Hakimin Dankama)
3. Sanata Hadi Sirika – Marusan Katsina (Hakimin Shargalle)
4. Alhaji Abubakar Dardisu, FCNA, Mni – Hakimin Muduru
5. Alhaji Gambo Abdullahi Dabai – Dausayin Katsina (Hakimin Dabai)
6. Alhaji Muhammad Dikko Umar Radda (Gwagwaren) Katsina (Hakimin Yadda)

Sanarwar ta ƙare da fatan alheri da zaman lafiya ga sabbin masu sarautar, tare da addu’ar Allah ya ba su nasara a jagorancin al’umma.

“Allah Ya ba mu lafiya da zaman lafiya, amin,” inji Alhaji Bello M. Ifo.

Da Dumi-dumi: Majalissar Sarkin Kasar Katsina ta nada Alhaji Ahmad Abdulmumini Kabir Usman( dan sarkin katsina), a matsa...
02/08/2025

Da Dumi-dumi: Majalissar Sarkin Kasar Katsina ta nada Alhaji Ahmad Abdulmumini Kabir Usman( dan sarkin katsina), a matsayin sabon Dan-Majen Katsina, Hakimim Dankama.

Da Dumi-dumi: 'YanKwankwasiyya sun bai wa Dr. Bello Galadanchi (Dan Bello) Lambar Yabo.Me zaku ce?Hoto: Dala FM Radio
01/08/2025

Da Dumi-dumi: 'YanKwankwasiyya sun bai wa Dr. Bello Galadanchi (Dan Bello) Lambar Yabo.
Me zaku ce?

Hoto: Dala FM Radio

Shugaba Tinubu ya sauke Dr Nasir Gawuna daga mukamin shugaban kwamitin gudanarwar jam’iar Bayero da ke Kano, ya maye gur...
01/08/2025

Shugaba Tinubu ya sauke Dr Nasir Gawuna daga mukamin shugaban kwamitin gudanarwar jam’iar Bayero da ke Kano, ya maye gurbinsa da AVM Saddik Kaita

Sai dai sanarwar fadar shugaban Nijeriyar ta ce har yanzu Dr. Gawuna yana kan mukaminsa na shugaban kwamitin gudanarwar bankin Mortgage na Nijeriya

01/08/2025

Gwamnatin Jihar Katsina ta shirya taron addu'o'i domin godiya ga Allah SWA da kuma neman ƙarin samun nasara akan al'amurran da s**a shafi ɓangaren Tsaro, Tattalin arziƙi dama sauran su.

Taron addu'o'in na gudana a Masallacin Modoi dake nan cikin garin Katsina.

Wannan taron addu'o'i Gwamnatin Jihar Katsina ke shirya shi duk shekara Ɗaya ga Watan 8.


DanMasani RADIO

01/08/2025
An Bude Shagon sayar da Kayan Abinchi Mai suna M Dr. Dikko Umar Radda, A Kamfanin A.A MODAA Yunkurin Fadada cigaba na Ka...
01/08/2025

An Bude Shagon sayar da Kayan Abinchi Mai suna M Dr. Dikko Umar Radda, A Kamfanin A.A MODA

A Yunkurin Fadada cigaba na Kamfanin A.A Moda, Dake cikin Garin katsina IBB way, kusa da Green House sun sun Bude Sabbin shago guda 2 na Pharmacy da Provisions wato shagon magani da kayan abinchi
Da aka sama suna Malam Dr. Dikko Umar Radda.

shagon Mlm.Dr.Dikko Umar Raɗɗa wanda ya ƙunshi kayan provision kala daban-daban don samawa jama'a sauƙin sayen kayan masarufi.

A lokacin ƙaddamar da shagon shugaban Kamfanin Alh.Abdul Aa moda ya nuna jin daɗinshi da godiya ga jama'a yadda su ke zuwa sayayyar kaya a AA Moda, tare da kira ga matasa don dogaro da kai.
Shima Uban taron ƙaddamar da shagon mai girma sarkin sulluɓawan katsina Alh.Yazid Abdulkarim Kabir Usman ya yi kira ga matasa da zama na gari masu amana tare da yabo da jinjina ga mamallakin kamfanin na AA moda Alh. Abdul bisa ga ayyukansa na taimakon al'umma da raya ƙasa.

Shima mai girma kwamishina na land Dr.Faisal Umar kaita ya yaba da nuna jin daɗinsa ganin yadda aka sanyawa wannan shago sunan mai girma gwamna Malam Dikko raɗɗa don yin koyi da kyawawan halaye da ayyukansa na raya jiha.

Yanzu haka dai an fara sayar da kayan masarufi da s**a shafi abinci kowane kala,danginsu shinkafa, fulawa,taliya,madara,man girki,sabullai da manshafawa da lemuna da ruwan roba da sauransu a kan farashi mai sauƙi.
Sauran shagunan da aka bude da sunayen manyan Malaman jihar, Yansiyasa da Yankasuwa na katsina sun haɗa da.

Alh.Umar Musa ƴar adua shop

Hrh Dr.Alh Abdulmumini Kabir Usman shop

Hrh Alh.Umar Faruk Umar shop

Alh.Ɗahiru Bara'u Mangal shop

Alh.Abdulkarim Kabir Usman shop

Dr.Alh Lawal Kaita shop

Sheikh Alh.Yakubu Musa Hassan shop

Sheikh Yakubu Yahaya Shop

Sheikh Yahaya Ibrahim masuss**a shop

Sheikh Sharif Abba Muzambilu shop

Daga DanMasani RADIO

Gaskiya ya isa haka, Sanatocin Arewa sun yi allah-wadai da kisan mutane a ZamfaraƘungiyar sanatocin arewacin Najeriya ta...
31/07/2025

Gaskiya ya isa haka, Sanatocin Arewa sun yi allah-wadai da kisan mutane a Zamfara

Ƙungiyar sanatocin arewacin Najeriya ta yi allah wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu fararen hula 35 a ƙaramar hukumar Ƙauran Namoda a jihar Zamfara.

Shafin BBC Hausa ta ruwaito cewa, cikin wani saƙon jaje da ƙungiyar ta aike ranar Laraba a Abuja, shugaban ƙungiyar Sanata Abdulaziz Yar’adua,ya jajanta wa al'ummar yankin musamman iyalan waɗanda lamarin ya shafa.

A farkon makon nan ne ƴanbindiga s**a yi wa su mutanen yankan rago duk kuwa da biyan kuɗin fansa da aka ce iyalansu sun yi domin kuɓutar da su.

Jihar Zamfara na daga cikin jihohin Najeriya da ke fama da ayyukan ƴanbindiga masu sace mutane domin neman kuɗin fansa.

Wasu masu sharhi dai na ci gaba da s**ar gwamnati da masu ruwa da tsaki a harkar tsaron ƙasar kan rashin samar da zaman lafiya a yankin.

Gwamnatin Tariya ta sanar da lokacin kammala aikin titin jirgin-ƙasa na Kaduna zuwa Kano Gwamnatin Najeriya ta ce za a k...
31/07/2025

Gwamnatin Tariya ta sanar da lokacin kammala aikin titin jirgin-ƙasa na Kaduna zuwa Kano

Gwamnatin Najeriya ta ce za a kammala aikin titin jirgin ƙasa daga Kaduna zuwa Kano a cikin shekarar 2026 mai zuwa, kamar yadda Ministan Sufuri Sa'idu Ahmed Alkali ya bayyana.

Da yake magana yayin wani taron tuntuɓa tsakanin 'yan ƙasa da gwamnati da ke gudana a jihar Kaduna da ke arewacin ƙasar, ministan ya ce lokacin da Shugaba Tinubu ya hau mulki kashi 15 cikin 10 na aikin kawai aka kammala.

"Amma zuwa yanzu an kammala kashi 53 cikin 100," in ji shi cikin wata sanarwa da ma'aikatar yaɗa labarai ta fitar a yau Laraba.

A 2024 gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa ta samu rancen kuɗin da za ta kammala aikin daga wani bankin kasuwanci na ƙasar China, abin da ministan ya jaddada a yau din.

Shugaban ƙungiyar gwamnonin Arewa kula gwamnan jihar Gombe, Inuwa Yahaya ne ya baiyana haka a taron tattaunawa tsakanin ...
29/07/2025

Shugaban ƙungiyar gwamnonin Arewa kula gwamnan jihar Gombe, Inuwa Yahaya ne ya baiyana haka a taron tattaunawa tsakanin gwamnati da al'umma na kwanaki biyu da ke gudana a jihar Kaduna.

Gwamnan ya ce Tinubu ya cika alƙawuran da ya ɗauka kuma ya na cigaba da cikawa ma.

DA DUMI-DUMI: SDP Ta Kori El-Rufa'i, Ta Haramta Masa Alaka da Jam'iyyar Na Tsawon Shekaru 30Jam’iyyar SDP ta sanar da ko...
28/07/2025

DA DUMI-DUMI: SDP Ta Kori El-Rufa'i, Ta Haramta Masa Alaka da Jam'iyyar Na Tsawon Shekaru 30

Jam’iyyar SDP ta sanar da korar El-Rufai daga cikin jam’iyyar tare da sanya masa haramcin shiga ko hulɗa da jam’iyyar na tsawon shekaru 30.

Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC) na SDP ya bayyana cewa wannan matakin ya yi dai-dai da kundin tsarin mulkin jam’iyyar, akidarta, manufa, da dokokin gudanarwa. Haka kuma matakin na bin tsarin mulkin tarayyar Najeriya da dokar zaɓe da ke bai wa kowace jam’iyya ‘yancin tsara membobinta.

A wata sanarwa daga mai magana da yawun jam’iyyar, Araba Rufus Aiyenigba, jam’iyyar ta ja kunnen ‘ya’yanta da su guji hulɗa da El-Rufai da duk wasu da ke da ra’ayi ko halaye da s**a sabawa muradun jam’iyyar.

Sanarwar ta ce:

“An haramta wa El-Rufai neman zama mamba, ko hulɗa da jam’iyyar, ko amfani da sunan SDP, tambari, alama ko wani abu da ke da nasaba da ita. Haka kuma ba zai iya bayar da gudunmawa, ko tallafawa ayyukanta na tsawon shekaru 30, farawa daga yau.”

Sanarwar ta Kara da cewa, ya kamata a lura cewa El-Rufai ya shiga jam’iyyar SDP ne bayan ficewarsa daga APC. Sai dai kuma, El-Rufai yana daga cikin fitattun shugabannin hadakar ‘yan adawa da s**a zabi African Democratic Congress (ADC) a matsayin dandamali domin shiga zaɓen 2027 mai zuwa.

Menene ra'ayinku?

Address

No. B27. Khalil Raman Shopping Complex. High Court Roundabout. Daura Road Katsina
Katsina
820221

Opening Hours

Monday 10:00 - 18:00
Tuesday 10:00 - 18:00
Wednesday 10:00 - 18:00
Thursday 10:00 - 18:00
Friday 10:00 - 18:00
Saturday 09:00 - 17:00
Sunday 09:00 - 17:00

Telephone

+2348080806872

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DanMasani RADIO posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to DanMasani RADIO:

Share