10/06/2026
Kungiyar ’Yankwangila Ta Jihar Katsina Ta Gudanar da Taron Shekara, Ta Yi Canji da Cike Gurabu na Shugabanni.
Daga Auwal Isah Musa| Katsina Times.
Kungiyar ’Yankwangila ta Jihar Katsina ta gudanar da taronta na shekara tare da shirya lakcar wayar da kai domin kara wa mambobinta ilimi da kwarewa, inda kuma ta amince da wasu sauye-sauye a tsarin shugabancinta ta hanyar nada sabbin jami’ai da sauya wa wasu mukamai a shiyyoyin Katsina, Daura da Funtua.
Tun farko da yake jawabi maraba a taron, Shugaban Kungiyar, Abdullahi Esha, ya bayyana taron a matsayin wani muhimmin mataki na hada kan mambobi domin nazarin ci gaban kungiyar da kuma tattauna hanyoyin bunkasa ayyukanta.
Ya ce wannan ne karo na farko da aka samu halartar mambobi daga kusan dukkan sassan kungiyar, yana mai bayyana yadda kungiyar ta samu ci gaba tun daga kafuwarta.
“Mun samu gagarumar nasara a wannan tafiya. A lokacin da muka fara, mambobinmu ba su wuce mutum shida zuwa bakwai ba, amma a yau muna da tsakanin mambobi 280 zuwa 300,” in ji Esha.
Ya kara da cewa hadin kai da fahimtar juna da ke tsakanin mambobin kungiyar na daga cikin manyan nasarorin da s**a samu, yana mai jaddada muhimmancin ci gaba da gudanar da irin wadannan taruka domin musayar ra’ayoyi da shawarwari.
“Akwai bukatar mu ci gaba da haduwa domin tattauna matsalolin da ke gabanmu da kuma hanyoyin magance su. Wannan zai tabbatar da dorewar kungiyar har zuwa nan gaba, hatta bayan wadanda s**a assasa ta ba su nan,” ya bayyanar.
Daya daga cikin muhimman abubuwan da taron ya kunsa shi ne gabatar da lakca kan harkokin kwangila da hanyoyin inganta aiki, wadda Q.S. Faisal Ahmad ya gabatar. A cikin lakcar, Faisal, ya yi karin haske kan dabaru da ka’idojin gudanar da ayyukan kwangila, tare da bayyana muhimmancin kwarewa, gaskiya da bin ka’idoji wajen samun nasara a harkar.
Bugu da kari, taron ya kuma yi nazari kan ayyukan kungiyar na shekarar da ta gabata, inda aka tattauna nasarori da kalubalen da aka fuskanta tare da daukar matakan gyara domin kara inganta tafiyar kungiyar.
Sakataren kungiyar, Yakubu Maicanji, ya sanar da amincewa da wasu nade-nade da sauye-sauyen mukamai domin cike guraben da s**a samu gibi da kuma saukaka gudanar da ayyuka a shiyyoyin kungiyar.
Sabbin nade-naden sun hada da: Injiniya Lawal Yunusa daga Shiyyar Funtua, wanda aka nada a matsayin Auditor General, Murtala Shehu daga Shiyyar Daura, wanda aka nada Assistant Secretary, da kuma El-Salisu Kawauri, wanda aka nada Assistant PRO.
Maicanji ya bayyana cewa an yi wadannan gyare-gyare ne domin kusantar da shugabanci ga mambobi a yankuna daban-daban.
“Duba da yanayin da ake ciki yanzu, ba lallai ne a rika tado mutum daga nesa zuwa Katsina domin gudanar da wasu ayyuka na gaggawa ba. Wannan tsarin zai taimaka wajen magance jinkiri da kuma saukaka tafiyar da harkokin kungiyar,” in ji shi.
Taron ya karkare da zaman tattaunawa, bayar da shawarwari da karbar tsokaci daga mahalarta, inda aka jaddada bukatar kara hadin kai, bunkasa kwarewa da kuma samar da sabbin dabarun da za su taimaka wajen karfafa kungiyar da tabbatar da ci gabanta.
A karshe, mahalarta taron sun bayyana gamsuwarsu kan yadda aka gudanar da taron, tare da nuna fatan cewa matakan da aka dauka za su kara habaka ayyukan kungiyar da inganta rayuwar mambobinta.