Funtua Online TV

  • Home
  • Funtua Online TV

Funtua Online TV Funtua Online TV — Tushen sahihan labarai da dumi-dumi daga Funtua, jihar Katsina, da muhimman rahotanni daga cikin gida da wajen najeriya. Contact: 08089440666

Funtua TV is the perfect choice for entertainment and news in your local area. With a wide range of programming options including sports, movies, and local news, you'll always have something to watch. And with our high-quality picture and sound, you'll feel like you're right in the middle of the action. But that's not all - we also offer a variety of advertising options to help you reach your targ

et audience. From commercial spots to sponsored programming, we have a solution that will work for you. So why wait? Contact us today to learn more about how Funtua TV can help you connect with your community and grow your business.

08065654928

Ƙungiyar Gidauniyar Uwar gidan kwamishinan muhallin jihar Katsina Hajiya Barista Naja'atu Hamza Sulaiman ta shirya wani ...
19/07/2025

Ƙungiyar Gidauniyar Uwar gidan kwamishinan muhallin jihar Katsina Hajiya Barista Naja'atu Hamza Sulaiman ta shirya wani babban gangamin wayar wa mata kai game da cutar kyanda, kamar yadda Hajiya Zulaihatu Dikko Radda ta bayar da umurni

A yau Asabar 19 July 2025, ƙungiyar Gidauniyar Uwar Gidan Sadaukin Kasar Hausa Hajiya Barista Naja'atu, daga kungiyoyin mata da matasa masu son faɗaɗa tafiyar gidan Wambai, sun shirya wani babban taro na tara dumbin mata don wayar masu da kai game da sha'anin lafiya, musamman rigakafin cutar kyanda.

A lokacin gabatar da jawabin nata, shugabar kungiyar Malama Ladidi Umar ta bayyana cewa sun kira wannan taron ne bisa kiran da Uwar gidan gwamnan jihar Katsina Hajiya Zulaihatu Dikko Radda ta yi na a wayar wa mata kai game da cututtukan ƙananan yara, musamman kan rigakafin da za a yi nan da wata biyu na cutar kyanda ga ƙananan yara

Ita ma a nata jawabin Uwar gigan shugaban karamar hukumar Faskari, ta bayyana muhimmancin rigakafi ga ƙananan yara, inda ta shawarci mata da cewa da zarar an fara gudanar da wannan allura kowace ta tabbatar an yi wa yayanta

Ita kuwa jawabin nata shugabar Gidauniyar Hajiya Barista Naja'atu da Hajiya Rukayya Sani ta wakilta, ta ce ta tara wannan babban gangamin ne domin isar da sakon H.E Hajiya Zulaihatu Dikko Radda da ta umurci a wayar ma mata kai game da amfani da kuma illar rashin yi wa yara rigakafin cutar kyanda

Masana harkar lafiya sun kuma yi wa matan jawabai da s**a shafi ingancin lafiyar ƙananan yara a lokacin gudanar da taron

A lokacin gudanar da taron an kuma shirya yar kwarya-kwaryar addu'a ta nema wa tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari gafara da rahamar Allah, sannan kuma an shirya wa mahalarta taron dirama mai ƙunshe da darasin illar rashin yi wa yara rigakafin cutar kyanda, wanda hakan na sa su da ƴaƴan nasu su zama abin ƙyama a cikin al'umma

Ibrahim M Bawa CEO Katsina Daily News

NELFUND Za Ta Kaddamar da Manhajar Neman Aikin Yi Don Tallafawa Dalibai Duba ƙarin bayani 👇
18/07/2025

NELFUND Za Ta Kaddamar da Manhajar Neman Aikin Yi Don Tallafawa Dalibai

Duba ƙarin bayani 👇

CIKIN HOTUNA: Taron FEC domin karrama tsohon shugaban kasar Najeriya marigayi Muhammadu Buhari wanda iyalan shi s**a hal...
18/07/2025

CIKIN HOTUNA: Taron FEC domin karrama tsohon shugaban kasar Najeriya marigayi Muhammadu Buhari wanda iyalan shi s**a halarta.

Tinubu Zai Je Kano Domin Ta'aziyyar Ɗantata Wannan yau Juma'a 👇
18/07/2025

Tinubu Zai Je Kano Domin Ta'aziyyar Ɗantata Wannan yau Juma'a 👇

Jihohin Arewa Sun Sami Ƙarin Kimanin Kashi 40 cikin Dari a Watanni Hudu na Farkon 2025A rabon kudaden Kwamitin Raba Kuda...
17/07/2025

Jihohin Arewa Sun Sami Ƙarin Kimanin Kashi 40 cikin Dari a Watanni Hudu na Farkon 2025

A rabon kudaden Kwamitin Raba Kudaden Shiga na Tarayya (FAAC) na zangon farko na shekarar 2025, jihohin Najeriya 36 sun raba jimillar Naira Tiriliyan 1.78, wanda in aka kwatanta da Naira Tiriliyan 1.27 da aka raba a zangon farko na 2024, an samu karin kashi 40% cikin dari.

Arewa maso Yamma ce ta fi samun ƙarin kuɗaɗen da kaso mafi girma daga Naira Biliyan 196.4 a Zangon Farko na 2024 zuwa Naira Biliyan 294.2 a Zangon Farko na 2025, ƙarin kaso 49.8% cikin ɗari. Arewa maso Gabas ta samu ƙari daga Naira Biliyan 177.3 zuwa Naira Biliyan 240.6, ƙarin kaso 35.7% cikin ɗari. Sannan Arewa ta Tsakiya ta samu ƙarin kaso 30.2% cikin ɗari, daga Naira Biliyan 196.3 zuwa Naira Biliyan 255.7.

Wannan cigaba ya biyo bayan irin sabbin matakai da tsare-tsaren da Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke ɗauka don inganta tattalin arzikin ƙasa, ƙarin kuɗaɗen shiga da kuma inganta rayuwar yan Najeriya a matakai daban-daban.

Ana sa ran gwamnatocin Jihohi Najeriya zasu yi amfani da wannan karin kudade wajen ƙara ingantattun hanyoyi, asibitoci, makarantu, ruwan sha da sauran abubuwan jin dadin rayuwa.

17/07/2025

Hi everyone! 🌟 You can support us by sending Stars.

Whenever you see the Stars icon, you can send us Stars.

Hauhawar Farashin Kaya Ya Ragu Da Kashi 22.22% A Watan Yuni 2025 —NBSHukumar Kididdiga ta Kasa (NBS) ta bayyana cewa hau...
17/07/2025

Hauhawar Farashin Kaya Ya Ragu Da Kashi 22.22% A Watan Yuni 2025 —NBS

Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS) ta bayyana cewa hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya ta sauka da kaso 22.22 cikin dari a watan Yuni 2025, daga 22.97% da aka samu a watan Mayu. Wannan rahoto ya fito ne daga sabon rahoton Hauhawar farashi “Inflation Report” da kuma rahoton farashin masu sayan kaya “Consumer Price Index (CPI)” da hukumar ta fitar a Abuja, wanda ke nuna ci gaban da aka samu a fannin tattalin arziki bayan sabunta ma’aunin kididdiga daga shekarar 2009 zuwa 2024.

Rahoton ya nuna cewa a bangaren hauhawar farashin abinci, an samu raguwar kashi 18.90 cikin dari daga shekarar da ta gabata, inda adadin ya sauka daga 40.87% a Yuni 2024 zuwa 21.97% a Yuni 2025.

Jihar Zamfara ce ta fi samun saukin hauhawar farashi da 9.90%, sai Yobe da 13.51% da Sokoto da 15.78%.

Hukumar NBS ta bayyana cewa sabunta tsarin kididdigar CPI da aka yi ya taimaka wajen dacewa da yanayin tattalin arzikin zamani. Babban Jami’in Kididdiga na Kasa, Adeyemi Adeniran, ya ce wannan sabuntawa na nufin inganta gano sahihin bayanai ta hanyar sabunta kayayyakin da ake amfani da su, da kuma karin wasu bangarorin kasuwa da hanyoyin tattara bayanai don a sami cikakken fasali na yadda tattalin arzikin kasa ke tafiya.

An Binne Gawar Marigayi Buhari A Gidan Sa Dake Daura, Jihar Katsina. An binne gawar tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhar...
15/07/2025

An Binne Gawar Marigayi Buhari A Gidan Sa Dake Daura, Jihar Katsina.

An binne gawar tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a gidansa da ke Daura, jihar Katsina, a safiyar yau, cikin jimami da addu’o’i daga iyalansa, shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, gwamnoni, ministoci, da dubban jama’a daga sassa daban-daban na ƙasa da waje.

Jana’izar marigayin ta samu halartar mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima, tsohon mataimakin shugaban ƙasa Yemi Osinbajo, shugaban ƙasar Guinea Bissau Umaro Sissoco Embaló, da Firayim Ministan Jamhuriyar Nijar, Ali Lamine Zeine.

Sauran manyan baki sun haɗa da shugabannin rundunonin tsaro, shugabannin masana’antu, Ministoci, tsofaffin gwamnoni, wakilin shugaban ƙasar Chadi, malamai, da fitattun mutane daga cikin gida da waje. Kafin binne gawar, dakarun haɗin gwiwar sojoji sun gudanar da harbe-harben ban girma sau 21 a matsayin girmamawa ta ƙarshe ga marigayin.

Babban hafsan tsaro na ƙasa, Janar Christopher Musa, shi ne ya karanta tarihin rayuwar Buhari, inda ya bayyana rasuwarsa a matsayin babban rashi ga Najeriya da iyalansa. Ya ce marigayin soja ne nagari mai cikakken kwazo, gaskiya, da kishi, wanda ya sadaukar da rayuwarsa ga hidimar ƙasa da kyakkyawan shugabanci.

A lokacin da aka iso Daura da gawar, dubban jama’a ne s**a taru suna Kabbara da addu’ar rahama ga marigayin. Iyalansa sun samu damar duban gawarsa na ‘yan mintoci kaɗan don yin addu’ar karshe kafin a rufe shi kabarinsa.

Marigayi Muhammadu Buhari ya shugabanci Najeriya a matsayin shugaban soja daga 1984 zuwa 1985, sannan ya sake komawa mulki ta hanyar zabe a 2015, kuma aka sake zaɓensa a 2019. Mulkinsa ya shahara da yaƙi da cin hanci, manyan ayyuka raya kasa, da kuma shan ƙalubale a fannonin tsaro da ci gaban tattalin arziki.

📸 Labari Cikin Hotuna | An Kammala Bizne Marigayi Muhammadu Buhari a DauraAn kammala binne gawar marigayi tsohon shugaba...
15/07/2025

📸 Labari Cikin Hotuna | An Kammala Bizne Marigayi Muhammadu Buhari a Daura

An kammala binne gawar marigayi tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a garin Daura, jihar Katsina.

Jama’a da dama sun halarci jana’izarsa, inda aka yi masa salla sannan aka kai shi makwancinsa.

Live Update — Funeral of Former President BuhariAt the funeral prayer ground, there is a large turnout of high-ranking g...
15/07/2025

Live Update — Funeral of Former President Buhari

At the funeral prayer ground, there is a large turnout of high-ranking government officials, international dignitaries, and diplomatic delegations.

The atmosphere is solemn, with people arriving steadily to pay their final respects.

📸 News in Photos – Buhari Body Arrives in KatsinaThe body of former President Muhammadu Buhari arrived at the airport in...
15/07/2025

📸 News in Photos – Buhari Body Arrives in Katsina

The body of former President Muhammadu Buhari arrived at the airport in Katsina State.

President Bola Ahmed Tinubu, Buhari’s family, and other leaders came with him.

Many people were there to show respect and say goodbye.

Tinubu Ya Kafa Kwamitin Da Zai Ja Ragamar Jana’izar Tsohon Shugaba BuhariShugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya kafa kwamiti...
15/07/2025

Tinubu Ya Kafa Kwamitin Da Zai Ja Ragamar Jana’izar Tsohon Shugaba Buhari

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya kafa kwamiti na musamman domin tsara jana’izar bangirma ga tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a ranar Asabar.

Kwamitin na musamman wanda Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume ke jagoranta, ya ƙunshi ministoci da manyan jami’an tsaro da masu bada shawara na fadar shugaban kasa.

An dora wa kwamitin alhakin tsara jana’iza wadda ta dace da matsayin marigayin shugaban, wanda ya jagoranci Najeriya har sau biyu tsakanin 1983–1985 da kuma 2015–2023.

Mambobin kwamitin su ne guda 17 kamar haka:

1. Sanata George Akume – Shugaban kwamitin

2. Ministan Kuɗi da Tattalin Arziki

3. Ministan Tsare-tsaren Kasafin Kuɗi

4. Ministan Tsaro

5. Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama'a

6. Ministan Ayyuka

7. Ministan Cikin Gida

8. Ministan FCT

9. Ministan Gidaje da Ci gaban Birane

10. Ƙaramin Ministan Lafiya da Walwala

11. Ministan Al’adu da Tattalin Arzikin Kirkira

12. Mai ba wa Shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro (NSA)

13. Mai ba wa Shugaban kasa shawara kan tsare-tsare

14. Babban Mataimaki na Musamman kan harkokin siyasa

15. Sufeto Janar na ‘Yan sanda

16. Darakta Janar na DSS

17. Babban Hafsan Tsaro (Chief of Defence Staff)

Ofishin Babban Sakataren Gwamnati (General Services Office – GSO) zai kasance ofishin gudanarwa na kwamitin.

Shugaba Tinubu ya kuma bayar da umarni ga dukkan ma’aikatu da hukumomi na gwamnati da su buɗe rajistar ta’aziyya a ofisoshinsu domin bai wa al’umma damar mika gaisuwa.

An kuma buɗe rajistar kasa a Ma’aikatar Harkokin Waje da Cibiyar Taro ta Bola Ahmed Tinubu da ke Abuja domin jakadun ƙasashen waje da sauran jama'a.

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Funtua Online TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Funtua Online TV:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share