Aku Mai Magana Reporters Hausa

Aku Mai Magana Reporters Hausa Domin kawo maku rahotannin da s**a shafi al'umma, dangane da addini da zamantakewa da siyasa da sauran al'amuran rayuwa.

17/02/2026

Taƙaitaccen tarihin zuwan Turawan mulkin mallaka daular Usmaniya tare da masanin tarihi Musa Gambo Ƙofar soro.

A yau Litinin 16/2/2026 mai Martaba Sarkin Katsina ya karɓi ziyarar da Alhaji Muntari Lawal Kofar Soro tare da 'yanuwa d...
16/02/2026

A yau Litinin 16/2/2026 mai Martaba Sarkin Katsina ya karɓi ziyarar da Alhaji Muntari Lawal Kofar Soro tare da 'yanuwa da abokan arziƙi s**a kai masa domin sanya albarka.

Kwanaki biyu da s**a wuce, kwamitin da ya shirya walimar karrama Alhaji Muntari ya kai wa mai Martaba kati domin sanar da shi taron yin walimar inda mai Martaba ya ce idan an kammala walimar a zo baki ɗaya domin shi ma ya sanya albarka musaman da ya ji abubuwan alkhairi da Muntari Lawal ya yi na sama wa al'umma aiki kafin ya yi ritaya.

A cikin jawabin da mai martaba ya yi, ya bayyana cewa faduwa ce ta zo daidai da zama, inda ya ce sun yi council meeting da yan majalissa cewa ba za su ƙara ba da sarauta ga duk mutumin da ya samu dama amma ya ƙi amfani da ita wurin taimakon al"umma ba.

Ya ci gaba cewa irinsu Muntari suke nema domin yi masu karamci da sarautar da ta dace da su.

Daga cikin Waɗanda s**a samu rakiyar sun haɗa da Hon. Hamisu Gambo Ɗanlawan Katsina da Abubakar Mamman Agawa Maharin Katsina da Hon. Aliyu Abubakar Albaba da Sabo Musa da Hon. Saifullahi Mamman Agawa da sauran manyan mutane da sauran 'yan'uwa da abokan arziƙi.

16/02/2026
05/02/2026
03/02/2026

Taƙaitaccen bayani a kan Tafsirul Jalalain da ake gabatarwa a fadar Mai Martaba Sarkin Katsina da wasu wurare a cikin garin Katsina.

Inna Lillahi Wa'inna Ilaihir Raji'un!Allah Ya yi wa Alh. Lawal Idris Bagiwa (Sarkin Fulalin Hamceta) rasuwa, tsohon jami...
21/01/2026

Inna Lillahi Wa'inna Ilaihir Raji'un!

Allah Ya yi wa Alh. Lawal Idris Bagiwa (Sarkin Fulalin Hamceta) rasuwa, tsohon jami'in hukumar kwastom (Custom Officer) a wata asibiti da ke babban birnin tarayya Abuja. Za a gabatar da sallar jana'izarsa da ƙarfe 5:00 na yamma a nan fadar Mai Martaba Sarkin Katsina da ke Ƙofar Soro, Katsina.

Muna roƙon Allah Ya jiƙansa da gafara Ya yi masa rahama, amin Ya Hayyu Ya Qayyum.

Mauludin Shehu Ibrahim Inyass kenan da ya wakana a yau Asabar 17/1/2026 a jihar Katsina, wanda miliyoyin mutane s**a hal...
17/01/2026

Mauludin Shehu Ibrahim Inyass kenan da ya wakana a yau Asabar 17/1/2026 a jihar Katsina, wanda miliyoyin mutane s**a halarce shi cikin ikon Allah an yi lafiya an gama lafiya.

‎Gwamna Radda ya nemi addu'o'in Shehunnai wajen taron Maulud Sheik Ibrahim Inyass, na samun zaman lafiya mai ɗorewa a jihar Katsina sa ƙasa baki ɗaya.

‎Gwamnan ya bayyana hakan a yayin jawabi a wajen taron Maulidin, inda ya bayyana jin ɗadinsa na kasancewar gagarumin bikin Maulidin karo na 40 a jihar Katsina.

‎Manya-manyan Mutane daga fadin duniya s**a halarci taron Maulidina, inda wasu daga cikinsu s**a gudanar da jawabai da addu'o'i daban-daban.

Yau shekaru goma (10) ke nan da yin taron Maulidin Shehu Ibrahim Inyass a jihar Katsina. Cikin ikon Allah yau ma ga shi ...
17/01/2026

Yau shekaru goma (10) ke nan da yin taron Maulidin Shehu Ibrahim Inyass a jihar Katsina. Cikin ikon Allah yau ma ga shi an sake dawowa a jihar ta Katsina domin gudanar da wannan gagarumin taro na murnar haihuwar Shehu Ibrahim Inyass.

Address

Katsina
Katsina
820101

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Aku Mai Magana Reporters Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share