Aku Mai Magana Reporters Hausa

Aku Mai Magana Reporters Hausa An buɗe wannan feji na Aku Mai Magana Reporters Hausa, don wallafa labarai a cikin harshen Hausa.

Katsina Local Government Council ke da mafi ƙarancin resources a cikin Local Governments (34) na jihar Katsina, amma hak...
23/09/2025

Katsina Local Government Council ke da mafi ƙarancin resources a cikin Local Governments (34) na jihar Katsina, amma hakan ba zai sare mana guiwa ba - Isah Miqdad AD Saude

Kansilolin ƙaramar hukumar Garki a jihar Jigawa sun tsige shugaban majalisarsu tare da zaɓar Hon. Abdulsamad Adam kansil...
13/09/2025

Kansilolin ƙaramar hukumar Garki a jihar Jigawa sun tsige shugaban majalisarsu tare da zaɓar Hon. Abdulsamad Adam kansilan mazabar Garki amatsayin sabon speaker ɗinsu, saboda zarge-zargen rashin gudanar da aiki daidai.

-Freedom Radio Nigeria

26/08/2025
TAKARDAR KORAFI A KAN SHIRIN RUFE MAKARANTUN COMMUNITY COLLEGESAssalamu Alaikum!A madadin al-ummar Kangiwa Word Katsina,...
26/08/2025

TAKARDAR KORAFI A KAN SHIRIN RUFE MAKARANTUN COMMUNITY COLLEGES

Assalamu Alaikum!

A madadin al-ummar Kangiwa Word Katsina, mun rubuta wannan takarda ne don nuna damuwarmu da kuma damuwar al’umma, kan shirin gwamnatin jiha na rufe Community Colleges saboda wasu manyan makarantu na gwamnati irin su, Hassan Usman Katsina Polytechnic da Federal College of Education suna da ƙarancin ɗalibai.

Muna ganin wannan mataki zai jawo matsaloli masu tarin yawa da tsanani ga ilimin a jiha, saboda haka ga wasu daga ciki:

1. Kasa cigaba da karatu – Idan aka tilasta ɗaliban Community Colleges su koma manyan makarantu na gwamnati, tsadar kuɗin sufuri da masauki da kayan karatu zai tilasta fiye da kashi 70 cikin 100 daga cikin ɗaliban jihar su daina karatu.

2. Ƙarin yawan Jahilai – Idan ɗalibai da yawa s**a daina karatu saboda tsadar makarantu da nisa, jahilci zai karu a cikin al’umma.

3. Rashin ingancin Ilimin manyan makarantu – Idan aka tara ɗalibai da yawa a cikin makarantu kaɗan, hakan zai rage ingancin koyarwa da kulawa ga kowane ɗalibi.

4. Sauƙaƙa wa al’umma – Community Colleges suna taimaka wa yankuna masu nisa wajen samun ilimi cikin sauƙi da rahusa. Rufe su zai lalata wannan damar.

Muna roƙon gwamnatin ta sake duba wannan shiri, ta bar Community Colleges su cigaba da aiki tare da inganta su a maimakon rufe su. Haka kuma, a ƙara inganta manyan makarantu na gwamnati domin su ja hankalin ɗalibai cikin adalci, ba tare da tilastawa ba.

Muna fatan wannan ƙorafi zai sami kulawa da amincewa cikin gaggawa.

Nagode.
✍🏼
Ibrahim Isiyaku
(Manager)

Shugaban Karamar Hukumar Katsina Ya Jagoranci Ziyarar Gani-da-Ido a Yankunan da ke Fama da Barazanar Zaizayewar ƘasaDa y...
25/08/2025

Shugaban Karamar Hukumar Katsina Ya Jagoranci Ziyarar Gani-da-Ido a Yankunan da ke Fama da Barazanar Zaizayewar Ƙasa

Da yammacin ranar Lahadi, 24-08-2025, Shugaban Karamar Hukumar Katsina, Hon. Isah Miqdad AD Saude, ya jagoranci wata tawaga ta musamman domin gudanar da ziyarar gani-da-ido a wasu yankuna da ake hasashen ambaliyar ruwa da zaizayewar ƙasa ka iya shafa.

Ziyarar ta kasance wani mataki na gaggawa da nufin tantance halin da ake ciki kai tsaye, tare da gano hanyoyin da s**a dace na ɗaukar matakan kariya na nan take da na dogon lokaci domin kare rayuka, dukiyoyi da kuma bunƙasa tattalin arzikin al’ummomin da abin ya shafa.

Unguwannin da aka ziyarta sun haɗa da Masoya Annabi Quarters da ke kan hanyar Batsari a cikin mazabar Wakilin Yamma II, Rahamawa ‘Yar Yara a Wakilin Kudu III, Mani House a Wakilin Kudu II, Shinkafi da Gezawa a Shinkafi A, Kwado a Shinkafi B, da kuma yankin bayan Sakatariyar ƙaramar hukumar Katsina da ke cikin mazabar Wakilin Gabas I.

A cikin tawagar da ta raka shugaban akwai Sakataren ƙaramar hukumar Katsina, Daraktan Sashen Ayyuka, Shugaban Majalisar Kansiloli wanda shi ma Kansila ne na Shinkafi B, tare da kansilolin Wakilin Yamma II, Wakilin Gabas I da Wakilin Kudu III. Haka kuma, ‘yan jarida da wasu daga cikin masu taimaka wa shugaban sun halarta.

Yayin tattaunawa da al’ummar yankunan, Hon. Miqdad ya tabbatar da cewa gwamnatin ƙaramar hukumar za ta ɗauki matakan da s**a dace tare da isar da rahoton ƙorafe-ƙorafen jama’a zuwa ga hukumomin da abin ya shafa. Ya jaddada cewa ba za su yi kasa a guiwa ba wajen fuskantar ƙalubalen muhalli, domin kare lafiyar al’umma, tsaron dukiyoyinsu da kuma tabbatar da zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki a cikin ƙaramar hukumar.

Zaharaddeen Muazu Rafindadi
Sakataren Yada Labarai na Shugaban Karamar Hukumar Katsina

25/08/25

Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Gawo Professionals Katsina sun sami gurbin buga gasar Nationwide League Division IƘungiyar ta G...
19/08/2025

Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Gawo Professionals Katsina sun sami gurbin buga gasar Nationwide League Division I

Ƙungiyar ta Gawo Professionals ta sami gurbin ne bayan buga gasar Nationwide League Div II wanda aka yi a shiyyar Katsina ta tsakiya.

Ƙungiyar ta sami damar ne sakamkon nasarar da ta samu a yammacin jiya a wasan da ta buga da ƙungiyar United Eagle's da ke jihar Jigawar Nigeria, inda ƙungiyar ta Gawo ta lallasa ƙungiyar da ci biyar da nema.

A yanzu ƙungiyar ta tsallaka zuwa gasar Nationwide League mataki na ɗaya a hukumance.

Audodo LBWK

DA DUMI-DUMINSA! Ƙaramar Hukumar Katsina ta Ƙaddamar da Shirin Tallafin Karatun Gaba da Sakandare 2.0 Kyauta ga MUTANE 1...
14/08/2025

DA DUMI-DUMINSA!

Ƙaramar Hukumar Katsina ta Ƙaddamar da Shirin Tallafin Karatun Gaba da Sakandare 2.0 Kyauta ga MUTANE 100

Ƙaramar hukumar Katsina ƙarƙashin jagorancin Hon. Isah Miqdad AD Saude ta shirya tsaf domin kaddamar da zango na biyu na shirin bayar da tallafin karatu na gaba da sakandare, wanda zai bai wa masu cin gajiyar 100 damar samun tallafin karatu kyauta daga farko har ƙarshe na kakar shekarar karatu ta 2025.

Shirin an tsara shi ne domin bai wa ɗalibai masu ƙaramin ƙarfi, amma suna da duk wata cancanta damar yin karatun National Diploma (ND) da Higher National Diploma (HND) a Hassan Usman Katsina Polytechnic.

ƘA'IDOJIN CANCANTA:

Dole ne mai nema ya kasance ɗan asalin ƙaramar hukumar Katsina.

Shekaru: 18 zuwa 35 kacal ake bukata.

Bayanin Neman Tallafin:

Lokacin nema: Daga Alhamis, 14/08/2025 zuwa Lahadi, 17/08/2025

A nema ta wannan adireshin yanar gizo: https://zfrmz.com/FlryQyMh8IOx34jJtQMy

Ana shawartar duk wani/wata ɗan/ƴar asalin ƙaramar hukumar Katsina da suke da bukatar ƙarin karatu da su shiga ta wannan adireshi na yanar gizo domin tura bayanansu domin samun damar shiga cikin shirin.

Zaharaddeen Muazu Rafindadi
Sakataren Yada Labarai na Shugaban Karamar Hukumar Katsina

14/08/2025

  ta Duniya 26-08-2025Za a gudanar da babban bikin Ranar Hausa a fadar mai martaba Sarkin Daura cikin garin Daura. Wanna...
13/08/2025

ta Duniya 26-08-2025

Za a gudanar da babban bikin Ranar Hausa a fadar mai martaba Sarkin Daura cikin garin Daura. Wannan biki za a aiwatar da shi a bisa sahalewar gwamnatin jihar Katsina ƙarƙashin jagoranci fitaccen ɗan-jarida Abdulbaki Jari

22/07/2025
Katsina State Community Development Programme Jerin sunayen wakilan kwamitin Shirin Cigaban Al'umma (CDP) na gundumomi (...
10/07/2025

Katsina State Community Development Programme

Jerin sunayen wakilan kwamitin Shirin Cigaban Al'umma (CDP) na gundumomi (Wards) da ke ƙarƙashin ƙaramar hukumar Katsina (Katsina L.G.A), wanda aka yi wa laƙabi da Community Level Committee (CLC) a Turance.

Ban yi mamakin yadda na ga ana ta yi ma mai girma gwamna jihar Katsina Mal. Dikko Umar Radda fatan ya zama mataimakin sh...
20/06/2025

Ban yi mamakin yadda na ga ana ta yi ma mai girma gwamna jihar Katsina Mal. Dikko Umar Radda fatan ya zama mataimakin shugaban ƙasa ba.

Jiya na ga wani babban mutum daga Arewacin Nijeriya, wanda ba ɗan jihar Katsina ba ne, yana bayanin irin ayyukan alheri wanda mai girma gwamna ya yi ma al'ummarsa cikin shekara biyu. Inda ya bayyana shi a matsayin gwarzon gwamna tun daga shekarar 2023 har zuwa yau.

Shi mai girma gwamna ba wannan al'amarin ke gabansa ba, shi buƙatarsa ita ce Allah ya ba shi ikon cika alƙawarin da ya yi tsakaninsa da Ubangijinsa da wanda ya yi ma al'umma lokacin da ya je neman goyon bayansu. Muna cigaba da addu'a dukkan abin da ya fi zama alheri Allah Ya tabbatar mana da shi amin.

Mu masoyan mai girma gwamna muna godiya da irin wannan ƙauna da ake nuna mana a kodayaushe. Kuma in sha Allahu mai girma gwamna zai cigaba da aiwatar da ayyukan alheri a cikin jiharmu ta Katsina.

Mun gode!
Yusuf Suleiman K/soro

Sanarwa! Sanarwa! Sanarwa!Cibiyar Koyar Da Sana'o'i Da Ƙere-Ƙere Na Zamani (KYCV) Za Ta Yi Bikin Yaye Ɗalibanta.Shugaban...
18/06/2025

Sanarwa! Sanarwa! Sanarwa!
Cibiyar Koyar Da Sana'o'i Da Ƙere-Ƙere Na Zamani (KYCV) Za Ta Yi Bikin Yaye Ɗalibanta.

Shugaban Cibiyar Koyar da Sana'o'i da Ƙere-Ƙeren Zamani wadda aka fi sani da Katsina Youth Craft Village (KYCV) Engr. Kabir Abdullahi K-soro na farin cikin sanar da al'umma cewa makarantar za ta yi bikin yaye ɗalibanta sama da Ɗari Shidda waɗanda da s**a kammala karatunsu a shekarar da ta gabata.

Za a yi bikin yaye ɗaliban ne a ranar 02/07/2025 da misalin ƙarfe 10:00 na safiya idan Allah ya kai mu.

Akwai tsare-tsaren ba da kayan sana'o'i ga ɗaliban da s**a kammala karatunsu a wannan makarantar domin su dogara da kansu.

Bisa ga wannan tsarin ɗalibi ko ɗalibar da ta sami aƙalla kashi 75% na zuwa makaranta su ne kaɗai za su amfana da waɗannan kayan sana'ar, duk ɗalibin da bai sami wannan kason ba ba zai sami tallafin kayan ba.

Kazalika, yayin ba da kayan dole ne ɗalibi ko ɗaliba su zo da wanda zai tsaya masu mahaifi ko mahaifiya ko wani wanda ya isa da su domin yin yarjejeniya cewa duk wanda aka baiwa kayan nan ba zai saida su ba, zai yi amfani da su ne domin neman na kan shi.

Address

Katsina
Katsina
820101

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Aku Mai Magana Reporters Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share