Aku Mai Magana Reporters Hausa

Aku Mai Magana Reporters Hausa An buɗe wannan feji na Aku Mai Magana Reporters Hausa, don wallafa labarai a cikin harshen Hausa.

Ban yi mamakin yadda na ga ana ta yi ma mai girma gwamna jihar Katsina Mal. Dikko Umar Radda fatan ya zama mataimakin sh...
20/06/2025

Ban yi mamakin yadda na ga ana ta yi ma mai girma gwamna jihar Katsina Mal. Dikko Umar Radda fatan ya zama mataimakin shugaban ƙasa ba.

Jiya na ga wani babban mutum daga Arewacin Nijeriya, wanda ba ɗan jihar Katsina ba ne, yana bayanin irin ayyukan alheri wanda mai girma gwamna ya yi ma al'ummarsa cikin shekara biyu. Inda ya bayyana shi a matsayin gwarzon gwamna tun daga shekarar 2023 har zuwa yau.

Shi mai girma gwamna ba wannan al'amarin ke gabansa ba, shi buƙatarsa ita ce Allah ya ba shi ikon cika alƙawarin da ya yi tsakaninsa da Ubangijinsa da wanda ya yi ma al'umma lokacin da ya je neman goyon bayansu. Muna cigaba da addu'a dukkan abin da ya fi zama alheri Allah Ya tabbatar mana da shi amin.

Mu masoyan mai girma gwamna muna godiya da irin wannan ƙauna da ake nuna mana a kodayaushe. Kuma in sha Allahu mai girma gwamna zai cigaba da aiwatar da ayyukan alheri a cikin jiharmu ta Katsina.

Mun gode!
Yusuf Suleiman K/soro

Sanarwa! Sanarwa! Sanarwa!Cibiyar Koyar Da Sana'o'i Da Ƙere-Ƙere Na Zamani (KYCV) Za Ta Yi Bikin Yaye Ɗalibanta.Shugaban...
18/06/2025

Sanarwa! Sanarwa! Sanarwa!
Cibiyar Koyar Da Sana'o'i Da Ƙere-Ƙere Na Zamani (KYCV) Za Ta Yi Bikin Yaye Ɗalibanta.

Shugaban Cibiyar Koyar da Sana'o'i da Ƙere-Ƙeren Zamani wadda aka fi sani da Katsina Youth Craft Village (KYCV) Engr. Kabir Abdullahi K-soro na farin cikin sanar da al'umma cewa makarantar za ta yi bikin yaye ɗalibanta sama da Ɗari Shidda waɗanda da s**a kammala karatunsu a shekarar da ta gabata.

Za a yi bikin yaye ɗaliban ne a ranar 02/07/2025 da misalin ƙarfe 10:00 na safiya idan Allah ya kai mu.

Akwai tsare-tsaren ba da kayan sana'o'i ga ɗaliban da s**a kammala karatunsu a wannan makarantar domin su dogara da kansu.

Bisa ga wannan tsarin ɗalibi ko ɗalibar da ta sami aƙalla kashi 75% na zuwa makaranta su ne kaɗai za su amfana da waɗannan kayan sana'ar, duk ɗalibin da bai sami wannan kason ba ba zai sami tallafin kayan ba.

Kazalika, yayin ba da kayan dole ne ɗalibi ko ɗaliba su zo da wanda zai tsaya masu mahaifi ko mahaifiya ko wani wanda ya isa da su domin yin yarjejeniya cewa duk wanda aka baiwa kayan nan ba zai saida su ba, zai yi amfani da su ne domin neman na kan shi.

Shugaban ƙaramar hukumar Katsina Hon. Isah Miqdad AD Saude ya ziyarci shugaban hukumar kula da "Asusun Bunƙasa Aikin Gon...
17/06/2025

Shugaban ƙaramar hukumar Katsina Hon. Isah Miqdad AD Saude ya ziyarci shugaban hukumar kula da "Asusun Bunƙasa Aikin Gona Na Ƙasa" domin haɓɓaka noma a ƙaramar hukumar Katsina.

A ranar Talata 17/06/2025, shugaban ƙaramar hukumar Katsina Hon. Isah Miqdad AD Saude ya ziyarci shugaban hukumar Kula da Asusun Bunƙasa Noma na ƙasa (NADF) Muhammad Abu Ibrahim a hedikwatar hukumar da ke babban birnin tarayya Abuja.

Da yake gabatar da jawabinsa shugaban ƙaramar hukumar Katsina Hon. Isah Miqdad ya ce mun kawo wannan ziyara ne domin neman haɗin guiwa da kuma neman goyon bayan wanan hukuma domin tallafa mana a cikin ƙudirinmu na bunƙasa noma a ƙaramar hukumar Katsina.

Kuma na tabbata idan wannan hukuma ta tallafawa manomanmu na ƙaramar hukumar Katsina zai taimaka mana wajen bunƙasa tattalin arziƙi tare da samar da aikin yi duba da yawan al'umma da wannan ƙaramar hukuma tamu take da shi dole ne mu samo hanyoyi da kuma dabarun da za mu bunƙasa tattalin arziƙinmu.

Shi ma da yake gabatar da jawabinsa shugaban hukumar kula da Asusun Bunƙasa Noma na Ƙasa (National Agricultural Development Fund) Alh. Muhammad Abu Ibrahim ya fara da nuna godiyar shi bisa wannan ziyara da shugaban ƙaramar hukumar ya kawo ma shi, ya kuma ce ina ba ka tabbacin za mu dubi ƙaramar hukumar Katsina a cikin shirye-shiryenmu na bunƙasa aikin gona.

Daga ƙarshe ya kuma bayyana shugaban ƙaramar hukumar Katsina a matsayin shugaban ƙaramar hukuma daga jihar Katsina da ya fara kawo irin wannan ziyarar aikin a ofishinsa.

Shugaban ƙaramar hukumar ya sami rakiyar sakataren shi na kai Muhammad Yusuf Sudais.

CIGIYA! Jama'a muna cigiyar ƴar uwarmu Hajiya Aisha Lawal Kafinta K/soro, jiya Juma'a ta fito daga gidanta da ke Filin S...
14/06/2025

CIGIYA! Jama'a muna cigiyar ƴar uwarmu Hajiya Aisha Lawal Kafinta K/soro, jiya Juma'a ta fito daga gidanta da ke Filin Samji da marece da niyyar za ta je zumunci a Ƙofar Soro amma har yanzu babu labarinta.

Don Allah mu sanya ta cikin addu'a Allah Ya bayyana ta cikin aminci, idan kuma an samu wanda ya ganta ko ya ji labarinta, to, ya tuntuɓi wannan lambar wayar 08156977777.

Mungode

COLLEGE OF MANAGEMENT AND TECHNOLOGY (C.M.T)Ina al'ummar jihar Katsina musamman ɗalibai masu sha'awar karatun Diploma a ...
14/06/2025

COLLEGE OF MANAGEMENT AND TECHNOLOGY (C.M.T)
Ina al'ummar jihar Katsina musamman ɗalibai masu sha'awar karatun Diploma a Jami'ar Gwamnatin Tarayya da ke Dutsinma (FUDMA)? Za ku iya yin karatunku na Diploma a nan gida Katsina a makarantar College of Management and Technology (C.M.T) da ke cikin makarantar sakandire ta Government Day Kofar Ƴanɗaka Katsina. Inda bayan kun sayi fom ɗin neman izinin shiga makarantar ɗalibai za su iya zaɓar gurbin karatun (Course) da suke so su karanta a wannan ɓangarorin kamar haka:

- Diploma in Social Development
- Diploma in Public Administration
- Diploma in Purchasing Supply
- Diploma in Banking Operations
- Diploma in Business Management
- Diploma in Accounting and Auditing
- Diploma in Entrepreneurship and Innovation
- Diploma in Computer Science
- Diploma in Information Management
- Diploma in Social Studies/Hausa Education
- Diploma in Islamic Studies Education
- Diploma in Computer/Mathematics Education
- Diploma in English/Hausa Language Education
- Diploma in Library and Information Science
- Diploma in Nutrition Science
- Diploma in Integrated Science Education
- Diploma in Health Education

Bayan kammala karatunku a makarantar College of Management and Technology CMT za ku karɓi sakamakon karatu (result) naku kai-tsaye daga Jami'ar Gwamnatin Tarayya (FUDMA).

Wannan damarku ce, za ku iya samin takardar shiga makarantar C.M.T ko da ba ku rubuta jarabawar JAMB ba.

Takardar shaida kammala karatun Diploma a makarantar C.M.T, za ta ba ku damar samin Admission a Jami'ar Gwamnatin Tarayya gami da tallafin karatu (Scholarship) daga gwamnatin jihar Katsina.

Tuni makarantar College of Management and Technology (C.M.T) ta fara saida takardar neman izinin shiga makarantar (Admission Form) na shekarar karatu ta 2025/2026.

Za a iya ziyartar makarantar C.M.T da ke cikin makarantar sakandire ta Government Day Kofar Ƴanɗaka da ke a nan cikin garin Katsina.

Ko kuma a tuntuɓe su ta adireshin yanar gizo wato www.cmtkatsina.com.ng

Ko kuma ta lambobin waya:

08036967159
07034519514

Domin Inganta Ayyukansu, Ƙaramar Hukumar Katsina Ta Shirya Taron Wuni Ɗaya Ga Kansiloli, Kansiloli Masu Ofishi (Supervis...
13/06/2025

Domin Inganta Ayyukansu, Ƙaramar Hukumar Katsina Ta Shirya Taron Wuni Ɗaya Ga Kansiloli, Kansiloli Masu Ofishi (Supervisory Councilors) Da Kuma Sauran Masu Muƙaman Siyasa

A ranar Juma’a 13 ga watan Yuni 2025, ƙaramar hukumar Katsina ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙaramar hukumar Hon. Isah Miqdad AD Saude haɗin guiwa da makarantar Ideas and Data, s**a shirya taron wuni ɗaya ga Kansiloli, Kansiloli masu ofishi da Sakataren ƙaramar hukumar da ma sauran masu muƙaman siyasa. Domin ƙara koyar da su dabaru da sha'anin gudanar da mulki.

Da yake gabatar da jawabin buɗe taron, shugaban ƙaramar hukumar Katsina Hon. Isah Miqdad AD Saude, ya bayyana an shirya taron ne domin ƙara zaburar da su da kuma horas da su domin su samu ilimin gabatar da kyakkyawan shugabanci sabo da ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya kuma yi kira ga masu muƙaman da su taimaka wajen gabatar da ayyukan raya ƙasa a yankunan su da ɗan abun da suke samu ko ya yake ba tare da cewa dole sai sun jira ƙaramar hukumar ba, ya kuma yi bayanin irin hanyoyin da ya bi wajen bunƙasa kuɗin shigar ƙaramar hukumar da kaso mai tsoka cikin ƙasa da wata biyu.

Daga ƙarshe ya yi kira gare su da su tsaya su maida hankali domin fahimtar abun da za'a koyar da su.

Babban Sakataren hukumar Cigaban jihar Katsina kuma shugaban makarantar Ideas and Data Dakta Mustapha Shehu, ya gabatar da lakcar shi a kan shugabanci, salon shugabanci da kuma dabarun gabatar da shi na wannan ƙarnin da muke ciki.

Duk a cikin ƙasidar ta shi ya kuma yi masu bayanin irin salo da wasu daga cikin sanannun shugabannin ƙasashen duniya s**a yi amfani da su wanda ya sa s**a samu nasara a lokacin mulkinsu.

A ta shi lakcar Associate Professor Ahmed Adamu, ya gabatar da lakcar ne a kan yadda za su yi amfani da damar su domin yin ayyukan da za su ajiye tarihin da ko bayan ba su nan za a ga wani abu da s**a yi wanda zai sanya a riƙa tunawa da su.

Ya kuma yi kira ga shugaban ƙaramar hukumar da ya samar da wani shiri da zai riƙa bibiyar ayyukan masu muƙaman, domin sanin irin ƙoƙarin da suke yi ga al'ummarsu.

Masana da dama a kan sha'anin gudanar da mulki ne s**a gabatar da lakcoci a wurin.

An rantsar da sabon shugaban ƙaramar hukumar Bakori bayan rasuwar Hon. Aminu Dan-Hamidu. A ranar Laraba 11/6/2025 gwamna...
12/06/2025

An rantsar da sabon shugaban ƙaramar hukumar Bakori bayan rasuwar Hon. Aminu Dan-Hamidu.

A ranar Laraba 11/6/2025 gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Radda Phd CON, wanda ya sami wakilcin sakataren gwamnatin jihar Katsina Barista Hon. Abdullahi Garba Faskari ya rantsar da Hon. Abubakar Musa Barde a matsayin sabon shugaban ƙaramar hukumar Bakori.

Hon. Abubakar Musa Barde ya zamo sabon shugaban ƙaramar hukumar Bakori, bayan kwana ɗaya da rasuwar tsohon shugaban ƙaramar hukumar Hon. Aminu Dan-hamidu wanda Allah ya yi ma rasuwa rana Litinin 09/06/2025.

Da yake gabatar da jawabin gwamnan jihar Katsina, ta bakin barista Abdullahi Garba Faskari ya nuna alhini na rashin marigayi Hon. Aminu, inda ya bayyana shi a matsayin babban rashi ga al'ummar ƙaramar hukumar Bakori.

Wakilin gwamnan ya yi addu'ar Allah Ya jiƙan Hon. Aminu da rahama, Allah Ya sa aljannace makomarsa, ya kuma yi addu'a ga iyalai da yan uwan mamacin.

Daga ƙarshe ya buƙaci sabon shugaban da ya zamo mai amana tare da jajircewa a kan al'amurra wajen yin aiki tukuru, ya kuma yi kira da ya zauna da kowa lafiya don cigaban ƙaramar hukumar Bakori.

Shi ma da yake zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan ya sha rantsuwa sabon shugaban Hon. Abubakar Musa Barde ya bayyana cewa" In sha Allah zai ɗora daga inda mai gidan na shi ya tsaya wajen ganin ƙaramar hukumar Bakori ta cigaba.

Kazalika ya bayyana cewa" dukkan wasu abubuwa da marigayin ya ɗauko zai ida su ba zai kauce ba, ya kuma tabbatar ma al'umma ƙaramar hukumar Bakori cewa" dukkan wanda marigayi yake mu'amula da su shi ma zai yi mu'amula da su domin cigaban ƙaramar hukuma.

Bikin rantsuwar wanda ya gudana a fadar gwamnatin jihar Katsina ya sami halartar shugaban ma'aikatan fadar gwamnatin jihar Katsina Hon. Abdulkadir Nasir Andaje, shugaban ma'aikatan jihar Katsina, Alh. Falalu Bawale, kwamishina ta ma'aitakar Shari'a Barista Fadila Dikko Kurfi.

Hon. Abdulkarim Al'ameen Modibbo (Secretary na Ƙaramar Hukumar Katsina  Sarkin Malaman Magajin Garin Katsina) ya zama sh...
02/06/2025

Hon. Abdulkarim Al'ameen Modibbo (Secretary na Ƙaramar Hukumar Katsina Sarkin Malaman Magajin Garin Katsina) ya zama shugaban Sakatarori na Jihar Katsina baki ɗaya.

A zaman da s**a yi a ranar Lahadi 01/06/2025 a nan ƙaramar hukumar Katsina Hon. Abdulkarim Al'ameen Modibbo Secretary na ƙaramar hukumar Katsina ya zama shugaban Sakatarori na Jihar Katsina baki ɗaya.

Sauran waɗanda aka zaɓa sun haɗa da Hon. Abdurrashid Nuhu Yashe (Sec. Kusada LG) a matsayin Vice Chairman.

Hon. Mustapha Bello Tsauri (Sec. Kurfi LG) a matsayin Secretary General.

Hon. Abubakar Umar Nasarawa (Sec. Ƙafur) a matsayin Treasurer.

Hon. Ilyasu Shu'aibu (Sec. Daura) a matsayin P.R.O.

Hon. Barr. Muhammad Adam (Sec. Dutsinma) a matsayin Legal Adviser.

Bayan haka Hon. Isah Miqdad A.D Saude Chairman na ƙaramar hukumar Katsina kuma Secretary General na (ALGON) ya yi kira ga Sakatarorin da su kasance masu biyayya ga Chiyamoninsu, kuma su san aikinsu, tare da zaɓar shuwagabannin da za su iya taimaka masu gami da biyayya ga mai girma gwamna. A ƙarshe zaɓaɓɓen Chairman na Forum (Sarkin Malamai) ya tabbatar ma sauran mambobin cewa zai yi aiki tsakaninsa da Allah tare da kare dukkan muradun mai girma gwamna. Sarkin Malamai ya kuma kira ga dukkan sauran membobin da su kasance masu biyayya ga Chiyamoninsu domin shi ne matakin cigabanmu tare da samin nasarori.

Taron ya samu halartar sama da Sakatarori 25 tare da uzurin sauran waɗanda ba su sami halata ba.

Aku Mai Magana Reporters Hausa

Taron maraba da sababbin ɗalibai (Orientation) na Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya (Department of Nigerian Languages) a ...
30/05/2025

Taron maraba da sababbin ɗalibai (Orientation) na Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya (Department of Nigerian Languages) a Tsangayar Nazarin Halayyar Ɗan-Adam (Fucalty of Humanities) Jami'ar Umaru Musa Yar'adua da Katsina. Wanda Ƙungiyar Ɗaliban Hausa (Hausa Students Union) s**a gudanar a ƙarƙashin uban ƙungiya Ass. Prof. Abdul Rahman Ado.

Taron ya sami halartar manyan malamai da s**a haɗa da Farfesa Mustapha Shu'aibu Safana da Aliyu Idris PhD da Ass. Prof. Bishir Abu Sabe da Surajo Ibrahim PhD da Abdulkadir Ɗan-Alhaji PhD da Muhammad Zaharadden Bello PhD da Zainab Isah PhD da sauran shugabannin kungiyoyin ɗalibai.

14/05/2025

SHIRIN "DAGA GARIN KATSINA" 003

Shiri ne da hukumar shafin jaridar "AKU MAI MAGANA REPORTERS HAUSA" ke ɗaukar nauyin kawo maku.

TARIHIN GIDAN YARIMA KATSINA (1870).

Gidan Yarima da ke unguwar Yarima Katsina, Sarkin Katsina Ibrahim ne ya gina shi a cikin shekarar 1870. Sarkin Katsina Ibrahim ya gina ma ɗan shi mai suna Yarima Abubakar wannan gida, a lokacin shi Abubakar yana riƙe da sarautar Yarima kamin ya zama Sarkin Katsina a cikin shekarar 1887. A wannan gida na Yarima Abubakar ya rinƙa zama. Babban gida ne wanda ke tsakanin unguwar Alkali da unguwar Sararin Kuka. Ita dai wannan sarauta ta Yarima sarauta ce ta ƴaƴan sarki tun lokacin Sarakunan Haɓe. Kalmar Yarima an aro ta ne daga ƙasar Borno da ke nufin babban ɗan sarki mai jiran gado.

Tarihi ya nuna cewa baya ga gidan Korau, watau Gidan Sarkin Katsina na yanzu, babu wani gida na ƙasaita a Katsina kamar gidan Yarima. Wannan dalilin ne ma yasa, lokacin da Turawan mulkin mallaka s**a zo Katsina a cikin shekarar 1903 a ƙarƙashin jagorancin Lord Lugard aka saukar da su a gidan Yarima don a girmama su. Kuma a cikin wannan gidan ne aka yi yarjejeniya da Turawan Ingila a kan ba za a yi yaƙi dasu ba. Turawan mulkin mallaka sun ci gaba da mulki tare da Sarkin Katsina Abubakar tun daga shekarar 1903 har zuwa shekarar 1905, inda aka samu matsala da shi Sarki Abubakar, Turawan Ingila sun tuɓe Sarki Abubakar a cikin shekarar 1905, inda s**a tafi dashi Ilori daga baya s**a dawo da shi Kano, ya rasu a Kano a cikin shekarar 1940.

Bayan tuɓe Sarki Abubakar sai aka naɗa ƙanen mahaifin shi watau Malam Yero, a cikin shekarar 1905, shi ma Yeron a cikin shekarar 1906 Turawan mulkin mallaka s**a tuɓe shi. Wannan ne ya kawo ƙarshen mulkin Sarakunan Dallazawa a Katsina.

Daga Yeron ne sai aka ɗauko Durɓi Muhammadu Dikko aka ba shi riƙon Sarautar ( Acting Emir) a cikin shekarar 1906, a cikin shekarar 1907 ne aka tabbatar ma shi da Sarautar Katsina bayan an naɗa shi kuma aka ba shi Sandar Girma. Sarkin Katsina Dikko shi ne Sarki na farko daga cikin zuriyar Fulani SULLUBAWA.

Bayan an tuɓe Sarakunan Dallazawa sai babban ɗan Sarki Abubakar watau Yarima Abdulkadir ya tara zuriyar Dallazawa ya tafi da su gonar mahaifin shi da ke Kauyen Tarkama cikin ƙasar KAITA ya ci gaba da noma da kiwo a wajen.

A lokacin da Lord Lugard ya kawo wata ziyarar ran-gadi a Katsina, sai ya tambayi Yarima Abdulkadir aka ce ma shi yana wani kauye a cikin ƙasar KAITA mai suna Tarkama, sai Lugard yasa aka kira shi ya tambayeshi shin wace Sarauta yake rike da ita yanzu, Yarima Abdulkadir yace ba shi da Sarauta. Sai Lord yasa Sarki Dikko da Turawan mulkin mallaka s**a yanka ma shi ƙasa a cikin ƙasar Ƴanɗaka a wani gari da ake ce ma Tsatkiya, a ba shi hakimin wajen da Sarautar Yariman Katsina. Shi ne daga baya ya dawo da hedikwatar shi a Safana. To tun daga wannan lokacin idan Yarima Abdulkadir ya zo taron SALLAH KARAMA ko BABBA a gidan Yarima yake sauka. Sai gidan Yarima ya ci gaba da ansa sunan shi da Gidan Yarima.

A halin yanzu gidan Yarima yana ɗaya daga cikin manyan gine-gine masu tarihi a Katsina, domin a wannan gidan ne aka fara saukar da Lugard Lugard, lokacin da Turawan mulkin mallaka s**a zo Katsina a cikin shekarar 1903.

Alh. Musa Gambo Kofar soro🖊️

Amadadina da Iyalaina muna taya Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina Mal. Dikko Umar Radda PhD murnar zaɓo Hon. Isah Miqdad a...
13/05/2025

Amadadina da Iyalaina muna taya Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina Mal. Dikko Umar Radda PhD murnar zaɓo Hon. Isah Miqdad a matsayin wanda aka zaɓa domin tallafawa da jagorantar al'amuran nagartattun al'ummar ƙaramar hukumar Katsina.

Hakazalika, ina taya Hon. Isah Miqdad murna domin samo Hon. Abdullahi Abubakar Yar'adua a matsayin ɗaya daga cikin zaɓaɓɓun kansiloli da kuma Saifullahi Mamman Agawa a matsayin ɗaya daga cikin kansilolin sa-ido daga Kangiwa Ward domin tallafa masa wajen yi wa al'ummar ƙaramar hukumar Katsina hidima, samun waɗannan mutanen alheri ne. Allah ya albarkaci ɗaukacin al'ummar yankin kangiwa, ƙaramar hukumar Katsina, jihar Katsina da Nijeriya baki ɗaya - Muhyyiddin Abdulkarim

SHIRIN "DAGA GARIN KATSINA" 002Shiri ne da hukumar shafin jaridar "AKU MAI MAGANA REPORTERS HAUSA" ke ɗaukar nauyin kawo...
06/05/2025

SHIRIN "DAGA GARIN KATSINA" 002

Shiri ne da hukumar shafin jaridar "AKU MAI MAGANA REPORTERS HAUSA" ke ɗaukar nauyin kawo maku.

GIDAN MASARAUTAR KORAU (1348)

Gidan Korau, shi ne babban gidan sarautar Katsina wanda Sarkin Katsina Muhanmadu Korau ya gina a cikin shekarar 1348. Har ya zuwa yanzu tarihin Katsina ba zai taɓa kammaluwa ba, sai da gidan Korau. Gidan Korau, ya zama abin alfari a tarihi da kuma al'ada ga Katsinawa. Yana ɗaya daga cikin manyan gina-gine na gidajen masarautun ƙasar Hausa da s**a haɗa da: Daura, Kano, Zazzau, Gusau, Haɗeja da sauransu.

Gidan zagaye yake da wata babbar ganuwa da ake kira da "Ganuwar Gidan Korau", wadda aka yi ma ƙofofi biyu watau Ƙofar Soro da kuma Ƙofar Bai. Ita Ƙofar Soro ita ce ƙofar da ake bi a shiga gidan Korau. Ita kuma Kofar Bai ita ce ƙofar da ke bayan gidan Korau, watau ƙofar baya.

An gina gidan Korau da kayan gini na gargajiya da s**a haɗa da: Tubali, kwaɓaɓɓar ƙasa, ƙyami, jangargari, asaberi, makuba da sauransu. Tun daga shekarar 1348 har zuwa yanzu ginin gidan Korau yana nan yadda yake.

Tun daga sarakunan Haɓe da s**a fara da sarki Muhammadu Korau 1348 da sauran sarakunan da s**a biyo bayan shi kamar Ali Murabus, Karya Giwa, Tsaga Rana Magajin Haladu da sauransu, duk a gidan Korau da ke Kofar soro s**a zauna. Lokacin da masu jihadi s**a ci Katsina da Yaƙi a cikin shekarar 1806, sarakunan Dallazawa sun zauna a gidan Korau tun daga Ummarun Dallaje 1806 har zuwa Yero 1906. A cikin shekarar 1906 Sarkin Katsina Muhanmadu Dikko ya amshi mulki daga hannun Fulani Dallazawa, ya zama Sarkin Katsina na farko daga zuriyar Fulani Sullubawa shi ma a gidan Korau ya zauna, wanda ya zuwa yanzu zuri'ar Sullubawa a ƙarƙashin jagoranci Sarkin Katsina Abdulmumini Kabir Usman suna zaune a gidan Korau.

A halin yanzu gidan Korau yana daga cikin manyan gidajen sarautar ƙasar Hausa, wanda masu ziyara ko ƴan yawon buɗe ido daga ƙasashe daban-daban suke ziyara.

Kamar yadda aka yi ganuwar gidan Korau domin tsaro, to haka mafi yawan mayaƙan sarki a cikin farfajiyar gidan Korau suke zaune domin ba da tsaro. Gidan Magayaƙi da gidan Turaki da gidan Sarkin Lihidi da sauran waɗanda manyan mayaƙa ne na sarki.

Haka kuma, manyan kayan sarautar gargajiya na Katsina suna gidan Korau da s**a haɗa: Tukunyar Karfe da Takobi Gajere da Takobi Bebe. Shi kuwa Gwauren Tambari yana ajiye ne gidan Sarkin Tambura.

Alh. Musa Gambo Kofar soro.🖊️

Address

Katsina
Katsina
820101

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Aku Mai Magana Reporters Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share