STAR RTV HAUSA

STAR RTV HAUSA Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from STAR RTV HAUSA, News & Media Website, Katsina.

Bamu Taba Yin Sanatan Da Ya Kula Da Rayuwar Mu Ba Kamar Audu Soja - Cewar Laftanal Hudu UsmanMataimaki na Musamman ga Gw...
08/03/2025

Bamu Taba Yin Sanatan Da Ya Kula Da Rayuwar Mu Ba Kamar Audu Soja - Cewar Laftanal Hudu Usman

Mataimaki na Musamman ga Gwamna Dikko Radda akan masu bukata ta musamman Laftanal Hudu Usman(Rtd) ya bayyana cewa basu taba samun sanatan da ya kula da rayuwar su ba kamar Sanata Abdul'aziz Musa Yar'adua.

Laftanal Hudu Usman mai ritaya ya furta hakan ne a lokacin kaddamar da tallafin sana'oi da kekunan guragu da sanatan ya samar ga masu bukata ta musamman.

Wadanda s**a amfana da tallafin su sama da 50 an zabo su ne daga Kananan Hukumomi 11 na Shiyyar Katsina ta Tsakiya.

Kayayyakin da sanatan ya samar a matsayin tallafin sana'oin sun hada da Kekunan Dinki da Injinan Murza Taliya da Kekunan Guragu gami da tallafin kudi ga dukannin wadanda s**a amfana.

Laftanal Hudu Usman wanda ya wakilci Gwamna Dikko Radda a wurin taron,ya bukaci wadanda s**a amfana akan su yi kyakkyawan amfani da tallafin.

Accuracy News Hausa ta tsinkaye shi yana mai kira garesu akan su sakawa karamcin ta hanyar yin addu'a ga samun nasarar Sanatan da sauran shuwagabanni.

Tunda farko wakilin Sanatan wanda kuma shine Shugaban Hukumar KASSAROTA Major Yahaya Rimi mai ritaya ya ce,tallafin na daga cikin cikon alkawarin yakin neman zaben Sanatan na inganta rayuwar masu bukata ta musamman.

Major Yahaya Rimi mai ritaya ya ce tunda farko sai da aka horas da wadanda s**a amfana akan sana'ar dinki da sabulun ruwa da sarka da kiwon kaji da sauran sana'oi.

Daga nan sai ya nanata kudirin Sanatan na cigaba da bullo da shirye-shirye da zasu inganta rayuwar al-ummar Mazabar tashi.

Sauran wadanda s**a maganta a lokacin taron sun hada da wakilin Ma'aikatar Jin Kan Al'umma da mataimaki na Musamman ga Sanatan.

Wasu daga cikin wadanda s**a amfana sun yabawa Sanatan akan kula da rayuwar su,sai s**a yi mashi addu'ar fatan nasara.

Ko A Saudiyya Ba'a Rufe Makarantu A Watan Azumi-Cewar SoworeTsohon Dan Takarar Shugaban Kasa a Najeriya Omoyele Sowore,y...
04/03/2025

Ko A Saudiyya Ba'a Rufe Makarantu A Watan Azumi-Cewar Sowore

Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa a Najeriya Omoyele Sowore,ya caccaki wasu Gwamnoni na kasar akan rufe makarantu a wannan lokaci na watan Ramadan.

A cewar Sowore, ko a Saudiyya ba a rufe makarantu a azumin Ramadan,kuma hakan ba dai-dai bane.

Omoyele Sowore, ya kira Gwamnonin Arewa da 'wawaye' kuma 'jahilai' kan rufe makarantun.

Tsohon dan takarar shugaban kasar ya ce 'jahilci ne rufe makarantu saboda wai ana azumin watan Ramadan.

Me Zaku Ce Akan Wannan?.

Yan Mazabar Tarauni Ta Jihar Kano Sun Ragargaji Dan Majalissar Su Akan Tallafin AzumiAl'ummar Mazabar Tarauni Ta Jihar K...
03/03/2025

Yan Mazabar Tarauni Ta Jihar Kano Sun Ragargaji Dan Majalissar Su Akan Tallafin Azumi

Al'ummar Mazabar Tarauni Ta Jihar Kano sun ragargaji Man Majalisar su saboda ya raba masu gero da dawa a matsayin tallafin azumi.

Me Zaku Ce Akan Wannan?.

Hoto: Hamza Imam Kano (Facebook)

Ku Sanya Ido Ga Ya'yan Ku Mata Da Ke Fita Sallar Tarawihi- Hisbah Ga IyayeHukumar Hisbah reshen Karamar Hukumar Katsina ...
03/03/2025

Ku Sanya Ido Ga Ya'yan Ku Mata Da Ke Fita Sallar Tarawihi- Hisbah Ga Iyaye

Hukumar Hisbah reshen Karamar Hukumar Katsina ta bukaci iyaye akan su sanya ido sosai ga ya'yan su mata da ke fita sallar Tarawihi a wannan lokaci na watan Ramadan.

Kwamandan Hisbah na Karamar Hukumar Katsina Malam Shamsu Kabir ya yi wannan kira,inda ya bukaci iyaye da su rika lura da lokacin fitar ya'yan su da lokacin dawowar su gida.

Malam Shamsu Kabir ya hori iyaye akan su tsananta bincike don gano masallacin da ya'yan nasu ke zuwa Sallar Asham da Tahajjud,domin hana su hulda da samari bata gari.

Daga nan sai ya yi gargadi da jan kunne ga matasa da yan mata gami da nasiha akan su ji tsoron Allah su tsaya su yi ibada cikin wannan wata mai albarka.

Ya ce Hukumar Hisbah zata zagaya lungu da sako na Karamar Hukumar Katsina domin gano masu aikata laifukan da s**a sabawa Addini, musamman a wannan lokaci na Ramadan.

Mai Alfarma Sarkin Musulmi Ya Sanar Da Ganin Jinjirin Watan Ramadan A NajeriyaFadar Mai Alfarma Sarkin Musulmi ta sanar ...
28/02/2025

Mai Alfarma Sarkin Musulmi Ya Sanar Da Ganin Jinjirin Watan Ramadan A Najeriya

Fadar Mai Alfarma Sarkin Musulmi ta sanar da yan Najeriya ganin jinjirin watan Ramadan a Kasar.

Mai Alfarma Sarkin Musulmi Sa'ad Abubakar ne ya sanar da ganin watan a yayin zantawa da Manema Labarai.

Yanzu-Yanzu :Kasar Saudiyya Ta Sanar Da Ganin Jinjirin Watan Ramadan.Yanzu Haka Kuma A Najeriya Ana Cigaba Da Dakon Sana...
28/02/2025

Yanzu-Yanzu :Kasar Saudiyya Ta Sanar Da Ganin Jinjirin Watan Ramadan.

Yanzu Haka Kuma A Najeriya Ana Cigaba Da Dakon Sanar Da Ganin Watan Daga Fadar Mai Martaba Sarkin Musulmi.

Azumin Watan Ramadan.....Gwamnatin Jihar Katsina zata dafa shinkafa buhu 361 a kowace rana har zuwa karshen azumin watan...
28/02/2025

Azumin Watan Ramadan.....

Gwamnatin Jihar Katsina zata dafa shinkafa buhu 361 a kowace rana har zuwa karshen azumin watan Ramadan,domin ciyar da mabukata na musamman a fadin Kananan Hukumomi 34 na Jihar.

Nasarorin Gwamna Radda Sun Nuna Karara Zai Kai Jihar Katsina Ga Tudun Mun Tsira - Cewar Ambasada Kai-KaiMatashin dan siy...
28/02/2025

Nasarorin Gwamna Radda Sun Nuna Karara Zai Kai Jihar Katsina Ga Tudun Mun Tsira - Cewar Ambasada Kai-Kai

Matashin dan siyasa a Jihar Katsina Ambasada Injiniya Abubakar Shehu Kaikai ya bayyana cewa,nasarorin da Gwamna Dikko Umaru Radda ya samu wata yar manuniya ce da ke tabbatar da cewa zai kai al'ummar Jihar Katsina ga tudun mun tsira.

Ambasada Kaikai wanda tsohon Dan Takarar Kukerar Dan Majalissar Tarayya ne na Mazabar Kankia/Ingawa/Kusada ya furta hakan ne a yayin wata zantawa da ya yi da Manema Labarai,ciki har da Accuracy News Hausa.

Kamar yadda ya bayyana,duk wanda ya bar Jihar Katsina kafin hawan mulkin Gwamna Dikko Umaru Radda,idan ya shigo Jihar a yanzu zai tabbatar da an samu gagrumin cigaba ta fuskar shimfida ayyukan raya kasa da cigaban al'umma.

A bangaren inganta rayuwar al'umma kuwa,Ambasada Kaikai ya ce Gwamna Dikko Radda ya bullo da dumbin shirye-shirye wadanda s**a yi matukar tasiri wurin inganta rayuwar al'umma.

Injiniya Kaikai ya yi nuni da cewar,babu wani bangare na cigaban rayuwar al'umma da Gwamnan bai taba ba tun daga lokacinda ya hawo mulki zuwa yau.

"Irin kokarinda Gwamna Radda yake yi ne ya sanya Gwamnoni da dama suke koyi da shi ta fuskar tafiyar da jihohin su".

Ya magantu akan irin yadda kafa Hukumar CWC ta taimaka wurin takaita hare-haren yan bindiga da garkuwa da mutane a Jihar Katsina.

Ambasada Injiniya Kaikai ya ce a matsayin shi na dan siyasa,zai cigaba da yin koyi da salon siyasar Gwamnan domin samun nasara.

Daga nan sai ya roki al'ummar Jihar Katsina akan kada su gajiya wurin yin addu'a ga samun nasarar Gwamnan da sauran Shuwagabanni a dukkan matakai.

To Fa.....Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan Ta Fallasa AkpabioYar Majalisar Dattawan Najeriya Sanata Natasha Akpoti-Uduagha...
28/02/2025

To Fa.....

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan Ta Fallasa Akpabio

Yar Majalisar Dattawan Najeriya Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta ce Shugaban Majalissar Sanata Godswill Akpabio ya neme ta da lalata taki yarda.

Natasha ta ce dalilin kin amincewar ne ya sanya Shugaban Majalisar ke kokarin taÉ—iye mata kafa tun bayan da ya neme ta da wannan manufa ta ki amincewa.

Ba Zamu Iya Cigaba Da Biyan Tallafin Wutar Lantarki Ba - Gwamnatin Tarayya Gwamnatin Tarayyar Najeriya a karkashin jagor...
28/02/2025

Ba Zamu Iya Cigaba Da Biyan Tallafin Wutar Lantarki Ba - Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayyar Najeriya a karkashin jagorancin Bola Ahmed Tinubu ta ce ba za ta iya cigaba da biyan tallafin lantarki ba.

Ministan makamashi na Kasar ya ce yanzu haka ana bin Gwamnatin Tarayyar bashin Naira tiriliyan 4 na tallafin wutar lantarkin.

Sai dai kungiyoyi da 'yan kasuwa sun ce ba za su lamunci karin kudin wuta da gwamnati ke shirin yi ba a fadin Kasar.

Nan Da Mako Biyu Masu Zuwa KTTV Zata Shiga Tauraron Dan Adam - Cewar Janar ManajaShugaban Gidan Talabijin na Jihar Katsi...
27/02/2025

Nan Da Mako Biyu Masu Zuwa KTTV Zata Shiga Tauraron Dan Adam - Cewar Janar Manaja

Shugaban Gidan Talabijin na Jihar Katsina Malam Abba Zayyan ya bayyana cewa,shirye-shirye sun kammala domin shigar da tashar a tsarin tauraron dan adam.

Malam Abba Zayyan ya tabbatar da hakan ne a sa'ilinda ya jagoranci sauran mambobin Hukumar Gudanarwar tashar a wata ziyara da s**a kai a Cibiyar Hanyar da Horon Sana'oi ta Katsina, wato Youth Craft Village.

Accuracy News Hausa ta tsinkayi Malam Abba Zayyan Yana mai cewa, ziyarar na da nufin inganta dankon zumunci da yake tsakanin tashar da cibiyar.

A cewar shi,cibiyar na taka muhimmiyar rawa wurin samun nasarar kudirin Gwamna Dikko Umaru Radda na samar da ababen yi ga matasa,domin su zamo Masu dogaro da kansu.

Ya yi albishir ga cibiyar Cewar tashar ta KTTV ta yi masu shiri na Musamman domin kawo ma al'ummar Jihar Katsina irin kokarin da Gwamna Radda yake yi ta wannan fuska.

Malam Abba Zayyan ya tabbatar da cewa,akwai kokarin da ake yi na ganin an farfado da kananan tashohin Funtua da Daura,domin kara Inganta ayyukan tashar.

A nashi jawabin,Shugaban cibiyar Injiniya Kabir Abdullahi Kofar Soro,ya nuna garin ciki akan wannan ziyara da Hukumar Gudanarwar tashar s**a kawo masu.

Injiniya Kabir Abdullahi Kofar Soro ya sanar da Janar Manaja cewa,Gwamna Dikko Umaru Radda ya ware ma cibiyar kudi sama da naira biliyan 4 a Kasa fin kudin bana.

Wannan kari ne bisa ga kayan aiki da ake daf da kawo ma cibiyar nan ba da jimawa ba.

Shugaban cibiyar ya lashi takobin cigaba da yin bakin kokari wurin rike dankon zumunci da yake tsakanin Hukumomin biyu.

Zamfara.....Rohotanni Da Ke Zo Ma Accuracy News Hausa Na Nuni Da Cewar,Wasu Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Mataimakin Shu...
26/02/2025

Zamfara.....

Rohotanni Da Ke Zo Ma Accuracy News Hausa Na Nuni Da Cewar,Wasu Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Mataimakin Shugaban Karamar Hukuma Da Wasu Mutane A Jihar Zamfara.

Address

Katsina

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when STAR RTV HAUSA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share