13/10/2025
SANARWA GA MANEMA LABARAI
Radda Visionary Network Ta Ƙarfafa Haɗin Gwiwa da Hukumar Hisbah ta Jihar Katsina; Ta Karrama Kwamanda Janar da Lambar Girmamawa
Katsina, Najeriya — 11 ga Oktoba, 2025
Ƙungiyar Radda Visionary Network ta kai ziyarar ban girma ga Kwamanda Janar na Hukumar Hisbah ta Jihar Katsina, Dr. Aminu Usman (Abu Ammar), domin ƙarfafa haɗin gwiwa da kuma tattauna sabbin hanyoyin yin aiki tare wajen bunƙasa al’umma, ƙarfafa matasa, da inganta ci gaban mata a fadin Jihar Katsina.
A lokacin ziyarar, tawagar da Mohd Sani Lawal, shugaban ƙungiyar, ya jagoranta tare da Umar Jamilu, Sakataren Ƙungiya, Fatima Sabo Nalado, Mataimakiyar Shugaba, Ibrahim Babangida Aliyu Turaji, Ma’ajin Ƙungiya, da Zainab Bello Ali Mashi, Jagorar Mata ta II, tare da sauran mambobin zartarwa, sun mika Lambar Girmamawa ga Dr. Usman domin girmama irin gudunmawarsa, jagorancinsa mai hangen nesa, da jajircewarsa wajen bunƙasa al’umma da ɗaukaka tarbiyya.
A cikin jawabin sa, Dr. Usman ya bayyana godiya mai zurfi bisa wannan karramawa, inda ya yaba da ƙoƙarin ƙungiyar wajen ƙarfafa matasa da mata. Haka kuma ya amince da farin ciki ya zama Mai tallafawa (Patron) ga Radda Visionary Network, inda ya sha alwashin ci gaba da bayar da goyon baya da hadin kai ga manufofin ƙungiyar.
A nasa jawabin, shugaban ƙungiyar, Mohd Sani Lawal, ya bayyana cewa manufar ziyarar ita ce ƙarfafa alaƙa da Hukumar Hisbah wajen inganta zaman lafiya, ladabi da tarbiyya, da kuma haɗin kai a cikin al’umma. Ya tabbatar da cewa ƙungiyar tana da cikakken shiri na yin aiki tare da hukumomi da cibiyoyi domin inganta shirin ƙarfafa matasa, ci gaban mata, da dorewar shirye-shiryen al’umma.
Ƙungiyar Radda Visionary Network ta jaddada cewa wannan karramawa da ta bai wa Dr. Usman alama ce ta ci gaba da manufar ƙungiyar na girmama shugabanni masu gaskiya, sadaukarwa, da jajircewa wajen haɓaka ci gaban al’umma.