BID HAUSA

BID HAUSA Welcome to *BID HAUSA*, the premier digital gateway for authentic Hausa‑language audio.

We bridge Northern Nigeria’s cultural heartbeat with global reach, delivering meticulously crafted programmes, crisp news, insightful interviews, and vibrant media eng

Kungiyar KCF ta Karrama Minista Engr. Muttaqa Rabe Darma a KatsinaKungiyar Katsina Consultative Forum (KCF) ta karrama M...
31/05/2026

Kungiyar KCF ta Karrama Minista Engr. Muttaqa Rabe Darma a Katsina

Kungiyar Katsina Consultative Forum (KCF) ta karrama Ministan Gidaje da Raya Birane na Najeriya, Injiniya Dakta Muttaqa Rabe Darma, bisa gudummawarsa wajen ci gaban jihar Katsina da kuma rawar da yake takawa a cikin ayyukan kungiyar.

An gudanar da bikin karramawar ne a ranar Asabar a dakin taro na Hillside da ke birnin Katsina, a wata liyafar cin abincin dare da kungiyar abokai ta shirya wa sabbin jakadun Nijeriya 'yan asalin jihar Katsina a Ghana da Adis'ababa karkashin jagorancin shugaban, kwamitin abokan Alhaji Yakubu Sani Store.

Da yake karɓar lambar yabon, Injiniya Darma ya bayyana cewa karramawar ta zo masa ne ba zato ba tsammani, yana mai cewa ya halarci taron ne domin taya abokansa murnar samun muk**an jakadanci, na kasashen ketare da gwamnatin tarayya ta basu.

“Ban san za a karrama ni ba a wannan taro. Na zo ne domin taya ’yan uwanmu murna da aka ba su damar wakiltar Najeriya a ƙasashen waje. Ina matuƙar godiya da wannan karramawa,” in ji shi.

Ya bayyana karramawar a matsayin abin ƙarfafawa gare shi wajen ci gaba da yin aiki tukuru domin cigaban jihar Katsina da al’ummarta.

Darma ya yi kira ga ’yan asalin jihar da su shiga cikin KCF domin bayar da gudummawa wajen kawo ci gaba a jihar.

Ya kuma bayyana wasu daga cikin ayyukan da kungiyar ta gudanar cikin shekaru biyu da s**a gabata, inda ya ce ta riƙa shirya tarurruka domin wayar da kan jama’a kan muhimman batutuwan zamantakewa da tattalin arziki.

A cewarsa, taron farko ya mayar da hankali ne kan illolin miyagun ƙwayoyi, har ma aka fitar da littafi a kai, yayin da taro na biyu kuma ya tattauna hanyoyin rage talauci a jihar Katsina.

Ya kara da cewa ba a samu gudanar da taron shekara-shekara a bana ba, amma suna fatan za a gudanar da shi kafin tsakiyar shekara.

’Yan uwa, abokan arziki da masoya sun taya Minista Muttaqa Rabe Darma murnar wannan karramawa tare da yi masa fatan alheri.

TAMBAYA

Shin wannan karramawa da Kungiyar KCF ta bai wa Minista Injiniya Dakta Muttaqa Rabe Darma ta dace da irin gudummawar da yake bayarwa wajen ci gaban Jihar Katsina, ko kuwa akwai wasu da ya k**ata su ma su samu irin wannan yabo?

Ku bayyana ra'ayoyinku a sashen sharhi.

MINISTAN GIDAJE YA NUNA RASHIN GAMSUWA DA JINKIRIN KAMMALA GIDAJEN RENEWED HOPE A KATSINABID HAUSAMinistan Gidaje da Ray...
31/05/2026

MINISTAN GIDAJE YA NUNA RASHIN GAMSUWA DA JINKIRIN KAMMALA GIDAJEN RENEWED HOPE A KATSINA

BID HAUSA

Ministan Gidaje da Raya Birane na Tarayyar Najeriya, Injiniya Dakta Muttaqa Rabe Darma, ya bayyana rashin gamsuwarsa kan jinkirin kammala aikin gina gidajen shirin Renewed Hope Housing Estate da ke kusa da Jami’ar Umaru Musa Yar’adua (UMYUK) a Jihar Katsina.

Ministan ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar duba aikin da ya kai wurin a ranar Lahadi, inda ya nuna damuwa kan yadda wasu daga cikin kwangilolin da aka bayar tun watan Disambar 2024 domin a kammala su cikin watanni shida har yanzu ba a kammala su ba.

A yayin rangadin, an bayyana masa cewa wasu kamfanonin da aka ba kwangilar sun samu ci gaba sosai, inda kamfanin K4 Engineering Services ya kusa kammala dukkan gidajen da aka ba shi alhakin ginawa. Sai dai ayyukan da s**a shafi hanyoyi, samar da ruwa da sauran kayayyakin more rayuwa har yanzu ba su kai matakin kammalawa ba.

Da yake jawabi ga 'yan kwangilar da jami’an da ke kula da aikin, ministan ya ce ba daidai ba ne a amince da wani wa’adin kammala aiki sannan a kasa cikawa ba tare da neman karin lokaci ko bayyana dalilan jinkiri ba.

Ya umarci dukkan masu ruwa da tsaki a aikin su gabatar masa da cikakken rahoto kan matsayin kowace kwangila, ciki har da sunan ɗan kwangila, ranar bayar da kwangila, wa’adin kammalawa da kuma adadin aikin da aka kammala.

Da aka tambaye shi ko ya gamsu da yadda aikin ke tafiya, ministan ya amsa da cewa:

> "A’a, ban gamsu ba. Duk wanda ya rattaba hannu kan kwangila yana da alhakin bin sharuɗɗan da ya amince da su."

Sai dai ya yabawa ingancin wasu daga cikin gidajen da aka kammala, yana mai cewa bai lura da wasu manyan matsalolin gine-gine ba a gidajen da ya duba. Haka kuma ya ce za a tura ƙwararrun masu tantance gine-gine domin tabbatar da ingancinsu kafin gwamnati ta karɓe su.

Ministan ya ƙara da cewa gwamnatin tarayya na aiwatar da irin wannan shirin na gidaje a jihohi da dama na ƙasar nan, tare da tabbatar da cewa ba za a karɓi gidajen da ba a kammala yadda ya k**ata ba ko kuma waɗanda ke da matsalolin inganci.

A cewarsa, an sanar da shi cewa ana gina gidaje 250 a Katsina ƙarƙashin shirin, amma bayan duba aikin ya gano cewa kusan gidaje 130 ne kawai aka kammala gaba ɗaya, yayin da sauran ke ci gaba da aiki.

TAMBAYA

Shin ya k**ata gwamnatin tarayya ta ɗauki mataki mai tsauri kan ‘yan kwangilar da s**a gaza kammala ayyukansu a kan lokaci, ko kuma a ba su ƙarin wa’adi domin kammala aikin?

BID HAUSA
Haɗa Kan Al'umma,

Rundunar VCRU ta ’Yan Sandan Katsina Ta Dakile Yunkurin Tayar da Zaune Tsaye, Ta K**a Mutane 6 Tare da Kwato Kayan AikiR...
29/05/2026

Rundunar VCRU ta ’Yan Sandan Katsina Ta Dakile Yunkurin Tayar da Zaune Tsaye, Ta K**a Mutane 6 Tare da Kwato Kayan Aiki

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Katsina ta samu nasarar k**a wasu mutane shida da ake zargi da hannu a wani hari da aka kai wa mazauna ƙauyen Keku da ke ƙaramar hukumar Musawa.

A ranar Laraba, 27 ga Mayu, 2026, da misalin ƙarfe 2:00 na rana, wasu mutane shida sun kai hari kan mazauna ƙauyen Keku da sanduna da adduna. Harin ya jikkata mutane da dama da raunuka mabambanta.

Bayan samun rahoton lamarin, jami’an rundunar VCRU sun gaggauta isa wurin tare da cafke waɗannan mutane da ake zargi:

1. Dayyabu Salisu, mai shekara 25

2. Usama Mansur, mai shekara 23

3. Yunusa Nura, mai shekara 27

4. Abdulmumini Alka, mai shekara 23

5. Buhari Suleiman, mai shekara 27

6. Abubakar Safiyanu, mai shekara 27

A yayin binciken farko, jami’an tsaro sun kwato adduna, sanduna da babura waɗanda ake zargin an yi amfani da su wajen aikata laifin.

Binciken farko ya nuna cewa waɗanda ake zargin sun haɗa baki ne domin tayar da tarzoma da kawo cikas ga gudanar da bukukuwan Babbar Sallah cikin lumana tare da kawo barazana ga zaman lafiyar da ake morewa a yankin. Gaggawar da jami’an VCRU s**a yi wajen kai ɗauki ta taimaka matuƙa wajen hana lamarin rikidewa zuwa babbar fitina.

An garzaya da mutanen da s**a samu raunuka zuwa asibiti mafi kusa domin samun kulawa, kuma ana ci gaba da ba su magani. Za a gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Katsina, Ali Umar Fage, ya yi Allah-wadai da harin tare da tabbatar wa al’umma cewa rundunar za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama'a.

Ya kuma buƙaci mazauna jihar da su kasance cikin natsuwa, su ba jami’an tsaro haɗin kai, tare da sanar da duk wani abu da ke da alamar barazana ga tsaro ta lambobin gaggawa na rundunar:

0815 697 7777

0707 272 2539

0902 220 9690

Rundunar ta sake jaddada cewa ba za ta lamunci duk wani nau’in daba, ɗaukar doka a hannu ko wani aiki da zai iya kawo cikas ga zaman lafiya ba.

Mai magana da yawun Rundunar ’Yan Sandan Jihar Katsina,

DSP Abubakar Sadiq Aliyu, anipr
Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar ’Yan Sanda (PPRO)
Madadin Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Katsina

BID HAUSA HADA KAN AL'UMA

RUNDUNAR ‘YAN SANDAN KATSINA TA TSARA TSARO NA MUSAMMAN DOMIN BABBAR SALLAH TA 2026Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Katsina ta...
26/05/2026

RUNDUNAR ‘YAN SANDAN KATSINA TA TSARA TSARO NA MUSAMMAN DOMIN BABBAR SALLAH TA 2026

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Katsina ta bayyana cewa ta kammala duk wasu shirye-shiryen tsaro domin tabbatar da gudanar da bukukuwan Babbar Sallah ta shekarar 2026 cikin lumana da kwanciyar hankali a faɗin jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, DSP Abubakar Sadiq Aliyu, ya fitar a ranar Talata, inda ya ce an tura isassun jami’an tsaro da kayan aiki zuwa muhimman wurare domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma kafin, yayin da kuma bayan bukukuwan Sallah.

Sanarwar ta bayyana cewa wuraren da aka ƙara tsaurara matakan tsaro sun haɗa da filayen sallar Idi, wuraren shakatawa, tashoshin mota da sauran wuraren taruwar jama’a a sassan jihar.

Rundunar ta ce jami’an da aka tura sun haɗa da jami’an ‘yan sanda na yau da kullum, jami’an rundunoni na musamman, jami’an kula da zirga-zirga da kuma jami’an sirri, waɗanda ke aiki tare da sauran hukumomin tsaro domin tabbatar da zaman lafiya.

A cewar rundunar, matakan tsaron za su fi mayar da hankali ne wajen kula da taron jama’a, daidaita zirga-zirga a manyan hanyoyi, tattara bayanan sirri da kuma hana duk wani abu da zai iya kawo barazana ga tsaro.

Kazalika, rundunar ta yi gargaɗi kan amfani da wasan wuta ba bisa ƙa’ida ba, tukin ganganci da kuma duk wani abu da ka iya haddasa tashin hankali ko karya doka yayin bukukuwan.

‘Yan sandan sun kuma buƙaci al’umma da su bai wa jami’an tsaro haɗin kai, tare da kai rahoton duk wani motsi ko mutum da ake zargi domin ɗaukar matakin gaggawa.

Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Katsina, CP Ali Umar Fage, ya taya al’ummar Musulmi murnar Babbar Sallah tare da tabbatar musu da ƙudirin rundunar wajen tabbatar da tsaro a duk lokacin bukukuwan da ma bayan su.

Rahoton BID HAUSA HADA KAN AL'UMA

26/05/2026

Anyya hon jamilu s kuka

Dan takarar ka ba APC ya keyi aiki ba? Part 21

26/05/2026

Anyya hon jamilu s kuka

Dan takarar ka ba APC ya keyi aiki ba? Part 20

26/05/2026

Anyya hon jamilu s kuka

Dan takarar ka ba APC ya keyi aiki ba? Part 19

26/05/2026

Anyya hon jamilu s kuka

Dan takarar ka ba APC ya keyi aiki ba? Part 18

26/05/2026

Anyya hon jamilu s kuka

Dan takarar ka ba APC ya keyi aiki ba? Part 17

26/05/2026

Anyya hon jamilu s kuka

Dan takarar ka ba APC ya keyi aiki ba? Part 16

Address

Sabon Titi Kwado
Katsina
820001TO820281

Opening Hours

Monday 08:00 - 00:00
Tuesday 08:00 - 00:00
Wednesday 08:00 - 00:00
Thursday 08:00 - 00:00
Friday 08:00 - 00:00
Saturday 08:00 - 00:00
Sunday 08:00 - 00:00

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when BID HAUSA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share