31/05/2026
Kungiyar KCF ta Karrama Minista Engr. Muttaqa Rabe Darma a Katsina
Kungiyar Katsina Consultative Forum (KCF) ta karrama Ministan Gidaje da Raya Birane na Najeriya, Injiniya Dakta Muttaqa Rabe Darma, bisa gudummawarsa wajen ci gaban jihar Katsina da kuma rawar da yake takawa a cikin ayyukan kungiyar.
An gudanar da bikin karramawar ne a ranar Asabar a dakin taro na Hillside da ke birnin Katsina, a wata liyafar cin abincin dare da kungiyar abokai ta shirya wa sabbin jakadun Nijeriya 'yan asalin jihar Katsina a Ghana da Adis'ababa karkashin jagorancin shugaban, kwamitin abokan Alhaji Yakubu Sani Store.
Da yake karɓar lambar yabon, Injiniya Darma ya bayyana cewa karramawar ta zo masa ne ba zato ba tsammani, yana mai cewa ya halarci taron ne domin taya abokansa murnar samun muk**an jakadanci, na kasashen ketare da gwamnatin tarayya ta basu.
“Ban san za a karrama ni ba a wannan taro. Na zo ne domin taya ’yan uwanmu murna da aka ba su damar wakiltar Najeriya a ƙasashen waje. Ina matuƙar godiya da wannan karramawa,” in ji shi.
Ya bayyana karramawar a matsayin abin ƙarfafawa gare shi wajen ci gaba da yin aiki tukuru domin cigaban jihar Katsina da al’ummarta.
Darma ya yi kira ga ’yan asalin jihar da su shiga cikin KCF domin bayar da gudummawa wajen kawo ci gaba a jihar.
Ya kuma bayyana wasu daga cikin ayyukan da kungiyar ta gudanar cikin shekaru biyu da s**a gabata, inda ya ce ta riƙa shirya tarurruka domin wayar da kan jama’a kan muhimman batutuwan zamantakewa da tattalin arziki.
A cewarsa, taron farko ya mayar da hankali ne kan illolin miyagun ƙwayoyi, har ma aka fitar da littafi a kai, yayin da taro na biyu kuma ya tattauna hanyoyin rage talauci a jihar Katsina.
Ya kara da cewa ba a samu gudanar da taron shekara-shekara a bana ba, amma suna fatan za a gudanar da shi kafin tsakiyar shekara.
’Yan uwa, abokan arziki da masoya sun taya Minista Muttaqa Rabe Darma murnar wannan karramawa tare da yi masa fatan alheri.
TAMBAYA
Shin wannan karramawa da Kungiyar KCF ta bai wa Minista Injiniya Dakta Muttaqa Rabe Darma ta dace da irin gudummawar da yake bayarwa wajen ci gaban Jihar Katsina, ko kuwa akwai wasu da ya k**ata su ma su samu irin wannan yabo?
Ku bayyana ra'ayoyinku a sashen sharhi.