Modern journalists

Modern journalists Modern journalist is a new medium. zaku iya bayar da talla ga wannan shafin
(2)

Domin samun sahihai kuma ingantattun Larabarai, akan al'amurran da ke faruwa a gida Nijeriya, dama sauran Ƙasashen Ketare wasu lokuttan, gami da tallata Hajojin ku, ko kuma ra'ayin ku.

Jirgin farko ɗauke da alhazan Jihar Nasarawa, ya dawo gida Najeriya bayan kammala aikin Hajji a Ƙasa mai Tsarki.
03/06/2026

Jirgin farko ɗauke da alhazan Jihar Nasarawa, ya dawo gida Najeriya bayan kammala aikin Hajji a Ƙasa mai Tsarki.

Magoya bayan Dr. Mustapha Inuwa sun zargi shugabannin Jam'iyar ADC ta Ƙasa, da shirya makarkashiya wajen hana shi takara...
02/06/2026

Magoya bayan Dr. Mustapha Inuwa sun zargi shugabannin Jam'iyar ADC ta Ƙasa, da shirya makarkashiya wajen hana shi takara.

A wani nazari da Jaridar Modern Journalists ta gudanar, ya bayyana tun bayan fitar da sunan Ahmad Babba Kaita daga shiyar Daura a matsayin Ɗan takarar Gwamna, mabiya bayan Inuwa ke bayyana lamarin a matsayin cin amana da kuma makarkashiya.

Haka kuma, a wata sanarwa mai tsawo da wato Kungiya ta masu rajin kishin ADC a Jihar Katsina ta fitar, ta zargi Shugabannin Jam'iyar ADC na Ƙasa Devid Mark, da kuma Ɗan takararta na Shugaban Ƙasa Alh. Atiku Abubakar da yin amfani da tasirin siyasar Mustapha Inuwa wajen kafa Jam'iyar a Jihar Katsina.

Kamar yadda s**a bayyana, bayan samun nasarar shigar magoya baya da dama Jam'iyar haɗakar a Jihar, jagororin na Ƙasa sun yi ƙoƙarin fitar da sunayen wasu mutane biyu, da ake ganin zasu iya yin tasiri a tafiyar, tare da kakaba Ɗan takarar su da suke da ra'ayi wato Sanata Ahmad Babba Kaita.

Kazalika, tun bayan fitar da sunan Ɗan takarar wasu daga cikin magoya bayan Mustapha Inuwa sun fara yunkurin ficewa daga tafiyar, wanda tuni wasu daga cikin su ma s**a fara aikewa da takardar barin Jam'iya a Mazabunsu.

Waɗan nan sune ƴan takarar kujerar Gwamna, da Jam'iyar ADC ta fitar a Jihar Katsina.Hon. Salisu UliAlh. Ahmad Babba Kait...
01/06/2026

Waɗan nan sune ƴan takarar kujerar Gwamna, da Jam'iyar ADC ta fitar a Jihar Katsina.
Hon. Salisu Uli
Alh. Ahmad Babba Kaita

Sai dai abun tambaya, shin waye halastaccen Ɗan takara a cikin su?

Gwamnatin Jihar Kano ta gwangwaje Ma'aikatanta da tallafin naira 20,000, a matsayin goron sallah Babba.Wannan na kunshe ...
26/05/2026

Gwamnatin Jihar Kano ta gwangwaje Ma'aikatanta da tallafin naira 20,000, a matsayin goron sallah Babba.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Babban Sakataren yaɗa labarai na ofishin sakataren gwamnatin Jihar Musa Tanko Muhammad ya rabawa manema labarai, a Jihar.

A wata sanarwa da Ma'aikatar yaɗa labarai ta Jihar Katsina ta fitar, ta bayyana Hon. Nura Aliyu tsohon Babban Maitaimaka...
25/05/2026

A wata sanarwa da Ma'aikatar yaɗa labarai ta Jihar Katsina ta fitar, ta bayyana Hon. Nura Aliyu tsohon Babban Maitaimakawa Gwamna Dikko Radda, akan harkokin inganta rayuwar al'umma, a matsayin wanda gwamnati ta dakatar tun bayan samun shi da hannu wajen karkatar da kayayyakin al'umma.

Kazalika, kafin wannan lokaci Nura Aliyu Garkuwa ya aikewa gwamnati da takardar yin murabus domin shiga sahun masu neman takarar kujerar Majalissar Dokoki mai wakiltar mazabar karamar Hukumar Batsari, a Jihar Katsina.

I dan za'a tuna, a makon da ya gabata ne Rundunar ƴan sandan Jihar Katsina ta fitar da sanarwar k**a Nura Garwa, akan zargin jagorantar tawagar wasu ƴan ta'adda da su s**ai garkuwa da Ɗan Makwabcinsa dake zaune a rukunin gidaje na Sardauna Estate dake cikin garin Katsina.

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Dandalin sada zumunta Yar'adua ya ƙaryata batun fidda Ɗan takarar Gwamna a Jam'i...
24/05/2026

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Dandalin sada zumunta Yar'adua ya ƙaryata batun fidda Ɗan takarar Gwamna a Jam'iyar su ta ADC a Jihar Katsina.

Yana mai cewa, ta hanyar zaɓen fidda gwani, ko kuma tattaunawa ne kaɗai doka ta baiwa ko wace Jam'iya damar fidda Ɗan takara, ba kawai wasu tsirarun Mutane su zauna su yi gaban kansu a madadin Miliyoyin al'umma ba.

"Batun ayyana sunan wani a matsayin Ɗan takarar Gwamna a Jam'iyyar ADC ba gaskiya ba ne"~Alh.Lawal Daura meneman takarar...
23/05/2026

"Batun ayyana sunan wani a matsayin Ɗan takarar Gwamna a Jam'iyyar ADC ba gaskiya ba ne"~Alh.Lawal Daura meneman takarar Gwamnan Jihar Katsina.

A cikin wani saƙo da ya aika ga magoya bayansa Lawal Daura yace, har yanzu kwamitin Sasanci na ADC bai fitar da sunan kowa ba, a matsayin Ɗan takarar Gwamna.

Don haka, ya buƙaci magoya bayan nasa da su kwantar da hankalin su, tare da yin watsi da duk wasu rahotanni marassa tushe da ake yaɗawa a kafofin sadarwa.

23/05/2026

Yadda akayi zaɓen fidda gwani na shugaban kasa a jam'iyyar APC kenan a mazabar Kudu 3 a karamar hukumar Katsina. Part 10

23/05/2026

Yadda akayi zaɓen fidda gwani na shugaban kasa a jam'iyyar APC kenan a mazabar Kudu 3 a karamar hukumar Katsina. Part 9

23/05/2026

Yadda akayi zaɓen fidda gwani na shugaban kasa a jam'iyyar APC kenan a mazabar Kudu 3 a karamar hukumar Katsina. Part 8

Address

Yahaya Madaki Way Katsina
Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Modern journalists posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Modern journalists:

Share