APC Media Team - Kubau

APC Media Team - Kubau Official media platform of APC Kubau LGA – Kaduna State. One voice, one family, one future.

30/08/2025
04/07/2025

SAKON BARKA DA SHIGOWAR SABUWAR SHEKARAR MUSULUNCI TA 1447 AH.Daga Akawun Jihar Kaduna, Hon. Bashir Suleiman-Zuntu, FCNA...
26/06/2025

SAKON BARKA DA SHIGOWAR SABUWAR SHEKARAR MUSULUNCI TA 1447 AH.
Daga Akawun Jihar Kaduna, Hon. Bashir Suleiman-Zuntu, FCNA.

Yayin da muke tarbar wannan sabuwar shekarar Musulunci ta 1447 Hijiriyya, ina mika sakon fatan alheri da barka ga daukacin al’ummar Musulmi na Jihar Kaduna, Najeriya, da duniya baki ɗaya.

Sabuwar shekarar Hijira lokaci ne na tunani mai zurfi, sabunta imani, da jajircewa wajen tsayawa kan gaskiya, hadin kai, da sadaukar da kai domin ci gaban jama'a. Wannan rana tana tunatar da mu Hijirar Manzon Allah, Annabi Muhammad (SAW), wacce ta kasance alamar sadaukarwa, juriya, da bege a cikin mawuyacin hali.

Ina rokon Allah (SWT) da ya sanya wannan shekara ta kasance mai cike da zaman lafiya, yalwar arziki, da shiriya mai dorewa. Allah ya karɓi addu’o’inmu, ya gafarta mana kura-kuranmu, kuma ya ci gaba da sanya albarka ga iyalanmu, al’ummarmu, da jihar Kaduna, tare da ci gaba da wadata mai dorewa.

Mu yi amfani da wannan lokaci mai alfarma wajen sabunta niyyarmu ta kasancewa masu gaskiya, tausayi, ladabi, rikon amana da mutunta juna, waɗanda su ne ginshikan addini da ci gaban al’umma.

Barka da sabuwar shekarar Hijira ta 1447.
Allah (SWT) ya sa ta zamo shekara mai albarka da rahama a garemu baki ɗaya. Amin, Ya Hayyu Ya Qayyum.

Daga:
Hon. Bashir Suleiman-Zuntu, FCNA
Akawun Jihar Kaduna.

17/06/2025

Senator Uba Sani ✌️✌️✌️

Happy Democracy Day 2025Allah yacigaba da bamu zaman lafiya Akasarmu baki daya ameen.Uba SaniBashir Suleiman-ZuntuMusa S...
12/06/2025

Happy Democracy Day 2025

Allah yacigaba da bamu zaman lafiya
Akasarmu baki daya ameen.

Uba Sani
Bashir Suleiman-Zuntu
Musa Sale Banki
Shehu Yunusa
Hon Hamisu Ibrahim Kubau
Ja'afar Muhammad Kubaù
Jamilu A Hasheem
Musa Anchau Ibrahim
Haruna Saleh
Hashimu Garba
Shehu Zakari
Umar Sani Kargi
Sabo Aminu
Albashir Umar Anchau
Sumaiyya Bilyaminu

APC Media Team Kubau
Prince Prince

Alhaji
31/05/2025

Alhaji

Thank you KagarkoThank you Kagarko Thank you Kagarko Senator Uba Sani ......X2....✌️
27/05/2025

Thank you Kagarko
Thank you Kagarko
Thank you Kagarko

Senator Uba Sani ......X2....✌️

A yau Litinin, 26 ga Mayu, 2025, Uwar Gidan Mai girma gwamnan jihar Kaduna, Hajiya Hafsat Uba Sani, tare da tawagarta su...
27/05/2025

A yau Litinin, 26 ga Mayu, 2025, Uwar Gidan Mai girma gwamnan jihar Kaduna, Hajiya Hafsat Uba Sani, tare da tawagarta sun kai ziyara karamar hukumar Kubau domin kaddamar da shirin bada tallafi mai taken “A KORI TALAUCI” ga mata a yankin.

An shirya bayar da tallafin ne a matakin farko ga mata 200, inda kowacce mace za ta amfana da naira dubu 100. Sai dai, ganin yawan matan da s**a halarta da kuma jajircewarta na tallafa wa mata domin su dogaro da kansu, Hajiya Hafsat Uba Sani ta kara yawan wadanda za su amfana zuwa 300.

A yanzu haka, adadin matan da s**a amfana da wannan tallafi a karamar hukumar Kubau ya kai 300, kuma kowacce daga cikinsu ta karɓi naira dubu 100, wanda jimillar kudin ya kai naira miliyan talatin (₦30,000,000).

Uwar gidan gwamna ta tabbatar wa matan cewa, gwamnatin Malam Uba Sani za ta ci gaba da tallafa musu domin karfafa gwiwar su wajen dogaro da kai, lamarin da ya kasance daya daga cikin manyan manufofin gwamnatinsa.

A cikin jawabansu daban-daban, Akawun jihar Kaduna, Hon. Bashir Suleiman Zuntu, da Shugaban Karamar Hukumar Kubau, Hon. Musa Sale Banki, sun bayyana farin cikinsu da godiya ga Uwar Gidan gwamna bisa wannan gagarumin tallafi da ta bai wa matan Kubau. Sun kuma tabbatar mata da cewa, matan za su yi amfani da tallafin yadda ya kamata. Haka kuma, sun tabbatar da ci gaba da samun goyon bayan al’ummar karamar hukumar Kubau ga jam’iyyar APC daga sama har kasa a karkashin jagorancin Gwamna Malam Uba Sani (Damo Sarkin Hakuri).

A nasu bangaren, matan da s**a amfana da tallafin sun bayyana matukar godiyarsu ga Hajiya Hafsat Uba Sani, tare da alkawarin amfani da tallafin yadda ya dace. Haka kuma sun sake jaddada cewa karamar hukumar Kubau ta jam’iyyar APC ce a jiya, yau, da gobe In Sha Allah.

Taron ya samu halartar manyan baki daga sassa daban-daban na jihar Kaduna da karamar hukumar Kubau, wanda s**a hada da: Mataimakin Shugaban karamar hukumar, Sakataren mulki na karamar hukumar, kansiloli da Sarakuna iyayen Kasa.

A ƙarshe, matan karamar hukumar Kubau sun tabbatar wa Uwar Gidan Mai girma gwamna da cewa:

Uba Sani Sau Biyu Ne ✌️

Jam’iyyar APC Daga Sama Har Kasa✌️

APC Uwa Daya, Uba Daya✍️

Daga kubau
Prince Prince 👑

25/05/2025

Uba sani
✌️✌️✌️✌️
In sha Allah

BREAKING : governor Uba Sani paid KASU lecturers their money that was withheld by former governor Elrufai and other his ...
10/05/2025

BREAKING : governor Uba Sani paid KASU lecturers their money that was withheld by former governor Elrufai and other his predecessors which caused the recent strike as gathered by the veteran Facebook Mustapha Yamusa Rigasa.

With this current big alerts that is hitting the bank account of KASU lecturers, this gesture will Mark the end of the two weeks strike.

MUHIMMIN SAKO ZUWA GA ’YAN BANI NA IYA MASU SON GANIN GAZAWAR JAGORAN JAM’IYYAR APC A KARAMAR HUKUMAR KUBAU, HON. BASHIR...
10/05/2025

MUHIMMIN SAKO ZUWA GA ’YAN BANI NA IYA MASU SON GANIN GAZAWAR JAGORAN JAM’IYYAR APC A KARAMAR HUKUMAR KUBAU, HON. BASHIR SULEIMAN-ZUNTU, FCNA.

Ya kamata wadanda muke magana a kansu su fahimci cewa duk wani gini da Ubangiji ya assasa, babu wani mahaluki da zai iya rushe shi, komai ƙarfin sa.

A ’yan kwanakin nan, wasu ’yan bani na iya da ke neman shahara a kafafen sada zumunta na zamani sun fito suna ƙoƙarin bata suna da ƙimar Jagoran Jam’iyyar APC na Karamar Hukumar Kubau, kuma Akawun Jihar Kaduna, Hon. Bashir Suleiman-Zuntu. Sun rika yada bayanai da bidiyon wani mutum fusatacce, wanda ya tara wasu matasa domin cimma wata manufa ta kashin kansa duk da nufin gurgunta darajar wannan babban jigo kuma jagora na jam’iyyar APC a Karamar Hukumar Kubau, da kuma ɓata sunan gwamnatin mai girma Gwamna Malam Uba Sani.

A jiya, bayan yada faifan bidiyon da aka ɗauka ba tare da izinin matasan da ke cikinsa ba, hankalin wadannan matasa ya tashi. Sun fito fili s**a yi Allah-wadai da wannan fusataccen mutum, tare da nisanta kansu daga zancensa mai cike da ƙaryar banza da ci da zuci. Daga nan s**a garzaya gidan Jagora Hon. Bashir Suleiman-Zuntu, bisa rakiyar Shugaban Matasan Jam’iyyar APC na Karamar Hukumar Kubau, domin sake bayyana mubaya’arsu gare shi, da kuma tabbatar da cikakken goyon bayansu ga jam’iyyar APC daga sama har ƙasa.

Hotunan da ke ƙasa suna nuna wannan ziyarar da matasan da aka yaudara s**a kai, don sake jaddada biyayyarsu da goyon bayansu ga Akawun Jihar Kaduna da jam’iyyar APC a dukkan matakai.

Yanzu dai, a Karamar Hukumar Kubau, lamarin ya fita daga cikin shakku. ’Yan bani na iya da kuma fusatattu sun shiga ruɗani. Hausawa sun ce: "Shure-shure ba ta hana mutuwa, sai dai idan lokaci ne bai yi ba."

APC Daya Ce a Kubau LG.👂

APC Uwa Daya, Uba Daya.✍️

Uba Sani Sau Biyu Ne✌️

APC Daga Sama Har Kasa✌️

AKAWUN JIHAR KADUNA HON. BASHIR SULEIMAN-ZUNTU, FCNA: LIMAMIN KAWO SAUÝI KUMA JAGORAN APC A KARAMAR HUKUMAR KUBAUKaramar...
08/05/2025

AKAWUN JIHAR KADUNA HON. BASHIR SULEIMAN-ZUNTU, FCNA: LIMAMIN KAWO SAUÝI KUMA JAGORAN APC A KARAMAR HUKUMAR KUBAU

Karamar hukumar Kubau na daga cikin kananan hukumomin da ke jihar Kaduna da s**a yi sa’ar samun nagartaccen jagora, wanda ya sadaukar da kansa wajen kawo ci gaba da inganta rayuwar al’umma. Wannan jagora ba wani ba ne face Akawun Jihar Kaduna, Hon. Bashir Suleiman-Zuntu, wanda ya zamo abar koyi ga kowa da kowa sakamakon hazaka, hangen nesa da gaskiya da ya ke nunawa.

Nagartarsa da jajircewarsa tare da aiyukan alheri na Mai girma Gwamnan jihar Kaduna, Malam Uba Sani (Damo Sarkin Hakuri), su ne ginshikan gagarumin sauyin da jam’iyyar APC ta ke samu a karamar hukumar Kubau da ma jihar Kaduna baki ɗaya.

Tun a lokacin da Hon. Bashir Suleiman-Zuntu ke matsayin Shugaban karamar hukumar Kubau, ya bude kofa ga kowa domin bayar da gudunmawa wajen gina karamar hukumar bisa gaskiya da adalci, ba tare da nuna banbanci ko son rai ba. Wannan tsarin shugabanci ya sa jama’a s**a kara yarda da shi tare da amincewa da jagorancinsa, wanda ya taimaka matuka wajen hadin kan dukkan ‘yan jam’iyyar APC a karamar hukumar Kubau.

Haka kuma, jajircewa da nagartaccen shugabanci na Akawun jihar Kaduna, tare da tsare-tsaren ci gaba da ayyuka masu ma’ana na Mai girma gwamna Uba Sani, sun kara wa jam’iyyar APC farin jini da tagomashi a karamar hukumar Kubau. Wannan ne ya sanya masu ruwa da tsaki daga jam’iyyun adawa kamar PDP da SDP ke ta komawa cikin jam’iyyar APC ba kakkautawa.

Daga ƙarshen shekarar 2024 zuwa yanzu, jam’iyyun adawa sun shiga wani hali na rushewa a karamar hukumar Kubau, bayan ficewar manyan jiga-jigansu zuwa APC. Wannan sauyin siyasa ya samo asali ne daga ingantaccen jagoranci da kuma ayyuka na zahiri da jama’a ke amfana da su a gwamnatin Malam Uba Sani tare da tagartaccen jagoranci na Akawun jihar Kaduna.

A makon da ya gabata, Akawun jihar Kaduna ya jagoranci wani babban kamu na ‘yan jam'iyyar adawa ta PDP zuwa APC, wanda hakan ya zama tamkar “jana’izar” jam’iyyar PDP ne a karamar hukumar Kubau. Daga cikin wadanda s**a sauya sheka akwai:

Hon. Hashimu Garba Anchau, tsohon Shugaban karamar hukumar Kubau, tsohon Dan Majalisar Dokokin jihar Kaduna, kuma dan takarar majalisar dokokin jiha a karkashin PDP a 2023.

Hon. Aminu Kargi, tsohon mataimakin Shugaban karamar hukumar Kubau.

Shugabannin matasa na Jam'iyyar PDP a karamar hukumar Kubau, da shugabanni na mazabu daban-daban na PDP.

Da sauran jajirtattun ‘yan siyasa na Jam'iyyar PDP daga sassa daban-daban na karamar hukumar Kubau.

Bayan haka, tun kafin wannan, jam’iyyar APC ta karbi wasu manyan jiga-jigan PDP kamar su Hon. Sabo Aminu Anchau, tsohon Shugaban karamar hukumar Kubau kuma Dan takarar Majalisar Wakilai na PDP a zaben 2023, na cikin gida daya gabata da mabiyansa baki daya.

Wannan juyin siyasa a karamar hukumar Kubau na ci gaba ne da shaidar karbuwa da nagartar jagoranci na Akawun jihar Kaduna, Hon. Bashir Suleiman-Zuntu, da kuma kyawawan manufofi da ingantattun ayyukan alheri na gwamna Malam Uba Sani da ke bayyana a ko’ina cikin jihar Kaduna.

Saboda haka, jam’iyyar APC a karamar hukumar Kubau ta shirya tsaf don karasa murkushe duk wata jam’iyyar adawa tare da tabbatar da cigaba da samun nasarar jam'iyyar APC a karamar hukumar Kubau, daga sama har kasa.

Muna kara jaddada bukatar jama’ar jihar Kaduna da su yi watsi da duk wata jita-jita da masu neman suna da 'yan bani na iya ke yadawa akan jam’iyyar APC da jagoranta a karamar hukumar Kubau, domin irin waɗannan batutuwa ba su da asali b***e madogara.

APC – Uwa Daya Uba Daya.
Uba Sani – Sau Biyu Ne!✌️
APC – Daga Sama Har Kasa baki daya

Address

Kubau LGA
Kubau

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when APC Media Team - Kubau posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share