24/05/2026
A wata huɗubar juma'a da Shahidin Jagora Syed Ali Khamnei (R) ya taba yi a shekarun baya.
Wannan magana na yanko tane a cikin wata huɗubar Juma'a da Jagora Shahid Syed Ali Khamnei (R) ya yi a shekaru baya, a cikin huɗuɓar ya bayyana hakikanin manufar jamhuriyar Musulunci akan sauran kasashen musulmi na duniya, huɗabar na da tsawo amma dai na yanko iya nan saboda a fahimcta me nake nason cewa. Ga ta kamar haka.
A cikin huɗuba Jagora na cewa: “Iran ta bayyana manufofinta na haɗin kan Musulunci da kuma goyon bayan gwagwarmaya yaji da rashin adalci ba tare da nuna bambanci ba.
Iran ba ta neman yaɗa akidar lɍañ ko akidar Shi’annci a tsakanin Musulmi. Iran tana bin tafarkin ɗaukaka Alƙur’ani ne da Sunnah, da kuma farfaɗo da al’ummar Musulmi baki daya daga barci mai nauyi da gafala.
Juyin juya halin Musulunci na ganin cewa taimaka wa mayaƙan Ahlus-Sunnah a ƙungiyoyi kamar H@mas da Palestinian Islamic Jihad, da kuma mayaƙan Shi’a a Hezbollah da Amal, wajibi ne na addini da umarnin Ubangiji, ba tare da nuna bambanci tsakanin wannan ko wancan ba.
Gwamnatin Iran tana bayyanawa da babbar murya cewa ta yi imani da farkawar al’umma Muslmi, ba ta hanyar ta’addanci ba; da haɗin kan Musulmi, ba rinjaye da rikicin mazhabobi ba; da ’yan’uwantakar Musulunci, ba girman kai na ƙabila ko wariyar launin fata ba; da jihadin Musulunci, ba tashin hankali a kan wasu ba.
Kuma tana mai tsayawa a kan wannan alkawari, in sha Allah.
Almujitabah Abubakar