MADUBI News 24/7

  • Home
  • MADUBI News 24/7

MADUBI News 24/7 MADUBI News 24/7

24/07/2025

APC ta nada Nentawe Yilwatda a matsayin sabon shugabanta

'Jam'iyyarmu ta APC na fuskantar barazanar faɗuwa a 2027'Wani jigo a jam'iyyar APC mai muki a Najeriya wanda kuma ya nem...
24/07/2025

'Jam'iyyarmu ta APC na fuskantar barazanar faɗuwa a 2027'

Wani jigo a jam'iyyar APC mai muki a Najeriya wanda kuma ya nemi takarar shugaban kasa a jam'iyyar a baya, ya bayyana wa cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da jam'iyyarsu ta APC na fuskantar babbar barazana a zaɓe mai zuwa.

Alhaji Adamu Garba, ya ce makusantan shugaban ƙasar ba sa fada masa gaskiya kan ainihin abin da ke faruwa musamman a arewacin ƙasar, yana gargaɗin cewa hakan zai iya jefa gwamnatin cikin haɗari.

Ya kara da cewa hadakar 'yan hamayya ta ADC na iya zamar wa APC kadangaren bakin tulu a zaɓe mai zuwa, musamman bayan rasuwar tsohon shugaban ƙasar Muhammadu Buhari.

Ya ce idan aka lura tsarin da aka bi wajen kirkiro APC tun ainahi, jam'iyyar ta samu mafi rinjayen kuri'unta daga arewa ne har ta kafa gwamnati a 2015.

''Saboda mu arewaci a wannan lokacin mun samar da kuri'u miliyan 12 da 'yan kai, yayin da kudu ta bayar da kuri'un da ba su fi miliyan uku da wani abu ba,'' in ji shi.

Wannan mutumin mai shekaru 27 da aka yanke wa shekaru 21 a gidan  kurkuku a yayin da ya kwanta da  jaririya mai wata 3 d...
22/07/2025

Wannan mutumin mai shekaru 27 da aka yanke wa shekaru 21 a gidan kurkuku a yayin da ya kwanta da jaririya mai wata 3 da aihuwa a ADOO.

Wani Fim Na Falasdinawa Ya Lashe Kyautar Fitaccen Shiri A Bukin Oscar Na Hollywood
20/07/2025

Wani Fim Na Falasdinawa Ya Lashe Kyautar Fitaccen Shiri A Bukin Oscar Na Hollywood

Harrison ya ba da gudunmowar jini sau 1, 173, a cikin fiye da shekaru 60 bai taba saba alkawarin daukar jinin da aka yi ...
20/07/2025

Harrison ya ba da gudunmowar jini sau 1, 173, a cikin fiye da shekaru 60 bai taba saba alkawarin daukar jinin da aka yi dashi ba har sa'ar da ya yi ritaya a shekarar 2018 yana da shekaru 81.

Wani mutumin kasar Austireliya da ake yabawa saboda ceton rayuwar jarirai fiye da milyan 2 ta hanyar shafe shekaru yana bada gudunmowar jini ya mutu yana da shekaru 88.

James Harrison wanda jininsa ke dauke da wani nau'in sinadarin protein da ba kasafai ake samunsa ba dake baiwa jiki kariya, ya mutu ne a cikin baccinsa a ranar 17 ga Febrairun daya gabata a wani asibitin Austireliya da ke jihar New South Wales, a cewar kungiyar bada agaji ta Red Cross da ake kira da lifeblood.

Harrison ya ba da gudunmowar jini sau 1, 173, a cikin fiye da shekaru 60 bai taba saba alkawarin daukar jinin da aka yi dashi ba har sa'ar da ya yi ritaya a shekarar 2018 yana da shekaru 81.

A jumlance, an karawa iyaye mata miliyan 2 jinin da ke dauke da kwalaben sinadarin anti-d daga jinin harrison fiye da miliyan 3 a Austireliya tun daga 1967.

A 1999, an bashi babbar lambar girmamawa ta kasar Austireliya da nufin yabawa irin talafawar da yake baiwa lifeblood da kuma shirin hada alluran anti-d.

Gwamnonin Najeriya biyar da kotu ta wanke bayan zargin rashawa.Babbar Kotu a Legas ta wanke tsohon gwamnan jihar Ekiti, ...
20/07/2025

Gwamnonin Najeriya biyar da kotu ta wanke bayan zargin rashawa.

Babbar Kotu a Legas ta wanke tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayodele Fayose, a shari'ar halasta kuɗaɗen haram da hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC ta shigar da shi a gaban kotu.

A ranar 16 ga Yuli, 2025, kotu ta bayyana cewa Fayose bai aikata laifin da ake zargin sa da shi ba, na sama da faɗi da kuɗi haram har naira biliyan biyu.

Fayose ya shafe shekaru yana fuskantar tuhumar cin hanci da rashawa lokacin da yake gwamna, amma kotu ta yanke hukunci cewa babu isassun hujjoji da ke tabbatar da laifinsa.
..Asalin hoton,Ayodele Fayose
Alƙali ya bayyana cewa "binciken da masu gabatar da ƙara s**a yi bai nuna alaƙar da ke tsakanin wanda ake tuhuma da laifukan da ake zarginsa da su ba, ta yadda kotu za ta ga dacewar kiran sa domin ya ba da bahadi."

Tun da farko, kotun ta ba wa Fayose izinin fita ƙasar waje domin jinya bayan ya roƙi hakan.

KAI JAMA'A DUNIYA INA ZA KI KAI MU: An K**a Ta Da Rana Tsaka Ta Zo Binne Wani Kulli A Cikin Makabàrtà wai saboda kar a m...
20/07/2025

KAI JAMA'A DUNIYA INA ZA KI KAI MU:
An K**a Ta Da Rana Tsaka Ta Zo Binne Wani Kulli A Cikin Makabàrtà wai saboda kar a mata kishiya.

20/07/2025

News News: Bala'i ya buge a Kano yayin kisan gilama

Wani lamari mai ban tausayi ya faru a yau a cikin Kano lokacin da aka ba da sanarwar da ba a ba da labari ba a gwargwadon gungun matasa da ke da alaƙa da mutuwar tsohon shugaban kasar Muhammadu Buhari.

Shaidun gani da ido sun rasa iko kuma ya murƙushe daya daga cikin mahalarta, yayin da wata motar da ke dauke da wasu mutane uku da aka bayyana a cikin hadarin. D

WHO ta amince da wani sabon maganin kariyar kamuwa da HIV
15/07/2025

WHO ta amince da wani sabon maganin kariyar kamuwa da HIV

15/07/2025

Za a binne gawar Buhari a cikin gidansa na Daura - Dikko Radda

Tinubu ne zai karɓi gawar Buhari a KatsinaShugaban Nigeria Bola Tinubu ne zai tarbi gawar tsohon shugaba Muhammadu Buhar...
15/07/2025

Tinubu ne zai karɓi gawar Buhari a Katsina

Shugaban Nigeria Bola Tinubu ne zai tarbi gawar tsohon shugaba Muhammadu Buhari a Katsina, domin yi masa jana'iza a Daura.

Ministan yaɗa labarai, Mohammed Idris ne ya tabbatar da hakan da yammacin yau Litinin a Abuja.

A cewar ministan, da misalin karfi 12 ranar gobe Talata ake saran gawar marigayi tsohon shugaban ya isa Katsina.

Sannan za a yiwa shugaban faretin ban girma a filin jirgin saman Katsina, kafin daga bisani a wuce garin Daura da gawarsa.

Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima yanzu haka na Landan, kuma shi ne zai rako gawar har Katsina.

Gwamnatin Najeriya ta kafa kwamiti na musamman da za su tsara jana'izar da kuma duk wani abu da ake bukata wajen binne shugaban.

Yadda za a gudanar da jana'izar Buhari a DauraYayin da ƴan Najeriya ke dakon gawar tsohon shugaban ƙasar, Muhammadu Buha...
15/07/2025

Yadda za a gudanar da jana'izar Buhari a Daura

Yayin da ƴan Najeriya ke dakon gawar tsohon shugaban ƙasar, Muhammadu Buhari wanda ya rasu a ranar Lahadi a birnin London, ta fito da wasu abubuwa da za su zama tamkar matashiya dangane da rasuwar.

Muhammadu Buhari dai ya rasu ne ranar Lahadi a birnin Landan sakamakon ƴar jinya da ya yi. Tsohon shugaban ya rasu yana shekara 82, inda ya bar ƴaƴa 10.

Tsohon Shugaban Najeriya Buhari ya rasu

Lokacin jana'izar Buhari
Muhammadu BuhariAsalin hoton,Getty Images
A yau Talata ne za a yi wa marigayi tsohon shugaban Najeriya, Muhamamdu Buhari jana'iza da misalin ƙarfe 2:00 na rana a mahaifarsa ta Daura da ke jihar Katsina.

Address


Telephone

+2348037773271

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when MADUBI News 24/7 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to MADUBI News 24/7:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share