MADUBI News 24/7

MADUBI News 24/7 MADUBI News 24/7

Muna so a cike gibin da aka samu a siyan magungunan cuta mai karya garkuwa jiki'Gamayyar Ƙungiyoyin Masu Cuta mai Karya ...
14/09/2025

Muna so a cike gibin da aka samu a siyan magungunan cuta mai karya garkuwa jiki'

Gamayyar Ƙungiyoyin Masu Cuta mai Karya Garkuwar Jiki a Najeriya (NEPWHAN), ta nanata buƙatar haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen samar da kuɗaɗe a cikin gida don cike giɓin da aka samu bayan Amurka ta dakatar da ba da tallafin magungunan kashe kaifin cutar a ƙasashe k**ar Nijeriya.

NEPWHAN ta ce janye tallafin, wanda yanzu Amurka ta dawo da wani ɓangarensa, manuniya ce cewa ƙasashe k**ar Najeriya su ɗaura ɗamarar nemar wa kansu mafita, da nufin kuɓutarwa da tsare lafiyar al'ummarsu.

Abdulƙadir Ibrahim, shi ne babban jami'i na ƙasa a gamayyar ya shaida cewa, duk sun san gwamnati na iya bakin kokarinta, amma ita kadai ba zata iya ba.

Ya ce,"Dole ne a janyo kowa da kowa domin ayi wannan tafiyar baki Daya."

"Duk da an yi alkawarin za a bayar da wani bangare na kasafin kudi domin a cike gibin da aka samu, kuma ba wai abin cuta mai karya garkuwa jiki kadai ya hsafa ba, har da tarin tibi da ma maleriya."In ji shi.

matsayin Sarkinsu sannan s**a rinƙa aikawa da wasiƙu zuwa garuruwan da ke gefen Takai har zuwa Kano suna neman a yi musu...
14/09/2025

matsayin Sarkinsu sannan s**a rinƙa aikawa da wasiƙu zuwa garuruwan da ke gefen Takai har zuwa Kano suna neman a yi musu mubaya'a wanda ƙin yin hakan na nufin za a yaƙe su." In ji Dakta Raliya.

Da s**a tabbatar sun yi ƙarfin da za su iya yaƙi sai s**a tunkaro Kano domin yaƙa da ƙwace sarautar Kano daga Sarki Tukur.

"A watan Agusta na 1894 s**a taho Kano, sai Allah ya jarrabi Yusuf da ciwon da ya janyo ajalinsa a garin Garko. Wasu ma na cewa Yusuf kashe shi wasu ƴan uwansa s**a yi saboda suna son ɗora wani daban. To sai dai an ce kafin rasuwar Yusuf ɗin an ji ya ambaci sunan ɗanuwansa Alu ko kuma Aliyu Babba k**ar yadda wasu ke kiran sa.

Shi Alu ya kasance ɗa ne ga ɗiyar Sultan Abdurrahman wani abu da ke ganin idan aka naɗa shi to ba za a sami turjiya daga masarautar Sokoto ba. Ke nan za su haƙura idan aka saka ɗansu maimakon a saka wanda ba su sani ba. Sai dai kuma wasu sun ce an kashe Yusuf ne domin a saka Alu ɗin," k**ar yadda Dakta Raliya ta yi ƙarin haske.

'Sayyadina Umar ya taba aika sako Daular Borno'
Yadda aka naɗa Sarki Alu
Lord Lugard a ofishinsa da ke fadar Sarkin Kano a 1903.

Bayan rasuwar Yusuf, sai aka naɗa Alu a matsayin Sarki inda kuma a ranar 18 ga watan Satumba 1894 Sarki Alu ko kuma Alu babba ya jagorancin ayarin Yusufawa s**a shiga Kano, inda s**a nemi ƙwace mulki daga hannun Sarki Tukur.

To sai dai kuma bayan jin labarin shigar Alu da jama'arsa ne ya sa shi kuma Sarki Tukur da magoya bayansa da iyalansa s**a fice daga Kano a watan Maris, inda s**a nufi Katsina.

"Sun tsaya a wani gari da ake kira Kamri domin samun mafaka. To shi kuma Sultan Abdurrahman na Sokoto da labari ya je masa cewa an kori Sarki Tukur, sai ya nemi taimakon sarakunan Zazzau da Katsina da Kazaure da su zo su taimaka wa Tukur su mayar da shi kan kujerarsa ta hanyar yaƙar Alu. To amma ba su amince sun kawo ɗauki ba.

A watan Maris 1895 tawagogin Tukur da na Alu s**a haɗu a wani gari da ake kira Tafashiya da ke kan hanyar Katsina, inda aka gwabza.

Alu ya samu nasara a kan Tukur bayan illata shi sak**akon faɗuwar da dokinsa ya yi inda kuma ya yi jinya ta wasu kwanaki kafin ya rasu a ranar 16 ga watan Maris ɗin 1895 wanda kuma hakan ne ya kawo ƙarshen yaƙin.

Abin da ganawar Peter Obi da Goodluck ke nufi a siyasar NajeriyaBabu shakka ganawar da tsohon Shugaban Najeriya Goodluck...
13/09/2025

Abin da ganawar Peter Obi da Goodluck ke nufi a siyasar Najeriya

Babu shakka ganawar da tsohon Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya yi da Peter Obi ta ƙara jawo muhawara da kuma matso da babban zaɓen ƙasar da za a yi a 2027 kusa a zukatan mabiya harkokin siyasar ƙasar.

Jiga-jigan adawar biyu daga kudancin Najeriya sun gana ne a ranar Alhamis a Abuja, yayin da haɗakar 'yan hamayya ke ci gaba da ɗaukar salo iri-iri domin tunkarar jam'iyar APC mai mulki.

Duk da cewa Obi na iƙirarin har yanzu shi ɗan jam'iyyar Labour (LP) ne, yana kuma cikin ƴan hamayyar da s**a dunƙule a jam'iyyar haɗaka ta ADC.

Kazalika, duk da shi ma Jonathan bai taɓa bayyana ficewarsa daga babbar jam'iyyar adawa ta PDP ba, bai cika shiga ayyukan jam'iyyar ba tun daga lokacin da ya faɗi zaɓe a 2015, abin da ya sa ake yi masa kallon ya dawo daga rakiyarta musamman a yanzu da take cikin rikici tsamo-tsamo.

Ana iya cewa babban abin da haɗuwar 'yansiyasar biyu ke nufi shi ne yunƙurin yi wa APC taron dangi bayan ta shafe shekara 10 tana mulkin Najeriya.

Bayani kan jagororin ƙungiyar Ansaru da ake yankewa hukunci a Najeriya.A ranar Alhamis ɗin nan wata babbar kotun tarayya...
11/09/2025

Bayani kan jagororin ƙungiyar Ansaru da ake yankewa hukunci a Najeriya.

A ranar Alhamis ɗin nan wata babbar kotun tarayya a Abuja ta yanke wa Mahmud Usman, ɗaya daga cikin kwamandojin ƙungiyar Ansaru guda biyu da aka gurfanar a gaban kuliya, hukuncin zaman gidan yari na shekaru 15.

Alƙalin kotun mai shari'a Emeka Nwite ta nemi jami'an DSS su tsare Mahmud Usman a wurinsu kafin a kammala yanke masa hukunci kan ragowar tuhume-tuhume 31 da ake yi masa shi da Abubakar Abba wanda shugaban ma'aikatansa ne.

Ana dai tuhumar kwamandojin biyu ne da laifuka 32 masu alaƙa da ayyukan ta'addanci a 2022, bayan kai hari a barikin soji na Wawa Cantonement a Kainji da ke jihar Neja.

Munanan hare-hare shida da aka kai Nijar bayan juyin mulkin soji
Tuhume-tuhume
Ansaru.

Daga cikin tuhume-tuhumen 32 da ake yi wa kwamandojin ƙungiyar, akwai zargin samun horon sanin dabarun ƙirƙira da amfani da abubuwan fashewa daga ƙungiyoyin ta'adda.
Ana kuma tuhumar su da samun horo kan dabarun yaƙi daga wata ƙungiyar ƴan ta'adda a ƙasar Mali.
Hukumar DSS ta zargi kwamandojin biyu da kitsa harin da aka kai gidan yarin Kuje a 2022 wanda ya yi sanadiyyar tserewar fursunoni fiye da 600.

Har wayau, ana tuhumar mutanen biyu da aikata wasu laifuka da s**a haɗa da yin garkuwa da Alhaji Musa Umar Uba da Magajin Garin Daura a 2019 da sauran ayyukan fashi da makami.
Ko gwamnatin Najeriya ta san maɓoyar ƴanbindiga, me ya sa ta gaza kawar da su?

Yadda aka k**a su
AnsaruAsalin hoton,ONSA
A ranar 16 ga watan Agustan da ya gabata ne gwamnatin Najeriya ta ce jami'an tsaronta sun samu nasarar k**a wasu gawurtattun ƴanta'adda, ƴan tsagin ƙungiyar Ansaru da take zargi da kitsa fasa gidan yarin kuje a shekarar 2022, har wasu fursunoni s**a tsare.

Mai ba shugaban Najeriya shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu ne ya bayyana haka ne a taron manema labarai da ya gudana a ofishinsa da ke Abuja inda ya ce ƴanta'addan biyu na cikin waɗanda suke nema ruwa a jallo.

Mece ce Ingausa kuma wane tasiri za ta yi ga harshen Hausa?Farfesa Abdalla Uba Adamu2 Satumba 2025A duniyar zamani da ci...
03/09/2025

Mece ce Ingausa kuma wane tasiri za ta yi ga harshen Hausa?

Farfesa Abdalla Uba Adamu

2 Satumba 2025
A duniyar zamani da cigaba musamman a ɓangaren fasaha, harshen Hausa ma yana samun sabbin fuskoki da salo daban-daban.

Ɗaya daga cikin waɗannan sabbin abubuwa da s**a bijiro wa harshen Hausa shi ne Ingausa (EngHausa) – wato hanyar haɗa Turancin Ingilishi da Hausa a cakuɗa su wajen magana da rubutu a mu'amalar yau da kullum.

Yanzu haka, matasa da dama, musamman a kafafen sada zumunta, suna amfani da Ingausa wajen bayyana kansu cikin salo mai jan hankali.

Amma mece ce Ingausa? kuma mene ne tasirinta ga harshen Hausa?

Game da dalilin da ya sa aka fara amfani da Ingausa (EngHausa), Farfesa Abdalla Uba Adamu ya ce harshe tamkar abu ne mai rai da ke buƙatar aro sabbin abubuwa, inda ya ce ''Harshe abu ne da ke mirginawa, yake arowa ya kuma bayar da aro ga wasu harsunan," in ji shi.

nazarce-nazarce.

Ya yi misali da karin Ingilishi na Pidgin, inda ya ce da farko bai samu karɓuwa ba, "amma yanzu gidajen jarida na duniya suna watsa labarai da shi kuma ya karɓu."

Sai farfesan ya ce ba yana nufin asalin harshen ya mutu ba ne, "amma aro ya zama dole."

Shi ma Injiniya Rimgim ya ce burinsa cibiyar ta wuce koyar da sana'a, "ina so mu samu damar buɗe jami'a ko kwalejin ilimi da za a riƙa koyar da ilimin fasahar zamani da ƙere-ƙere kuma matasanmu su samu satifiket da zai yi daidai da na ko wace makaranta."

Ya ce yana fata ya ga EngHausa ya samu karɓuwa a tsarin ilimin Najeriya, inda zai zama ana iya amfani da shi a hukumance.

Ya ce a ilimin ƙirƙirarriyar basira, "idan ba mu yi amfani da harshen uwa wajen gina shi ba, to lallai za a tafi a bar mu a baya saboda za ta amfani da abin da take da shi ne."

Ana ci gaba da kai hari wasu yankunan Zamfara duk da sulhu da 'yanbindigaRahotanni na nuna cewa 'yan bindiga na ci gaba ...
03/09/2025

Ana ci gaba da kai hari wasu yankunan Zamfara duk da sulhu da 'yanbindiga

Rahotanni na nuna cewa 'yan bindiga na ci gaba da kai hare-hare suna kashe mutane da kuma sace dabbobi da sauran dukiya a wasu sassa na yankin karamar hukumar Shinkafi ta jihar Zamfara, a Najeriya.

A lamari na bayan-bayan nan sai da 'yan bindigan s**a kashe mutum biyar, s**a raunata wasu hudu a garin Galadi.

Hare-haren dai na aukuwa ne duk da yunkurin yin sulhu da al'ummomin wasu garuruwa na Shinkafin ke yi da 'yan bindigan, da kuma matakan tsaro da ake dauka.

Matsalar hare-haren 'yan bindiga, wadda ta zame wa yankin arewa maso yammacin Najeriya wani karfen-kafa, na ci gaba da addabar garin Galadi da sauran kauyuka da dama da ke makwabtaka da shi a yankin karamar hukumar Shinkafi ta jihar Zamfara. Kamar dai yadda wani mutumin yankin ya

Hanyoyin gane masu damfara a intanetA zamaninmu na yau, intanet ta zama hanya mafi sauƙi da mutane ke amfani da ita waje...
03/09/2025

Hanyoyin gane masu damfara a intanet

A zamaninmu na yau, intanet ta zama hanya mafi sauƙi da mutane ke amfani da ita wajen sadarwa da kasuwanci da samun bayanai.

Amma k**ar yadda take da amfani, haka kuma ta zama cibiyar aikata laifuka ga mazambata.

Masu damfara ta intanet suna amfani da dabaru iri-iri wajen yaudarar mutane domin sace musu kuɗi ko bayanai masu muhimmanci.

Wannan matsala ta shafi kowa, daga matasa zuwa manya, musamman a ƙasashe masu tasowa k**ar Najeriya da sauran ƙasashen Afirka, inda rahotanni s**a nuna yadda dubban mutane ke rasa miliyoyin kuɗaɗe saboda damfara ta intanet.

Gano hanyoyin da ƴan damfara ke amfani da su na da wahala saboda tsananin dabararsu da hikima, k**ar yadda Abdullahi Salihu Abubakar, mai bincike kan kafofi da hanyoyin sadarwa na zamani ya shaida.

Yadda ƴan damfara ke aiki
DamfaraAsalin hoton,Getty Images
Abubakar ya ce ƴan damfara na amfani da hanyoyi da dama wajen jefa mutane cikin tarkonsu, ba ta intanet kaɗai ba.

Wasu daga cikin dabarunsu sun haɗa da:

Nazarin yanayin mutane: Kafin su tura saƙo ko su tunkari mutum, s**an yi nazari kan halayensa da abin da ya fi jan hankalinsa. Wannan yana taimaka musu wajen tsara dabaru masu tasiri.
La'akari da ɗabi'un mutane: Suna lura da ɗabi'un mutum domin su fahimci yadda za su ja hankalinsa cikin sauri da sauƙi.

Lura da abin da ya fi ɗaukar hankali: Suna bincika abubuwan da mutane suke yi a wani lokaci domin su tsara saƙo ko aiki da zai fi jan hankali.
Tsara dabaru domin jan hankalin mutane: Suna ƙirƙirar dabaru daban-daban domin mutane su saurare su, su bi sawu, ko su bayar da bayanai na sirri.

Aika saƙonni ta wayar salula: Ƴan damfara kan tura saƙonni tas kai-tsaye, ko su kira mutum da wasu lambobi da ba a saba gani ba kuma su yi iƙirarin cewa akwai matsala a bankinsa wadda ake buƙatar ya gaggauta bayar da bayanai domin gyarawa.

Amfani da manhajojin sadarwa da shafukan boge: Suna amfani da Facebook, WhatsApp, Instagram, TikTok da imel. Ta hanyar jan hankali da ake kira 'social engineering', suna nuna k**ar sun san ka ko sun taɓa haɗuwa da kai domin su samu bayanai k**ar lambobin waya, imel, ko bayanan sirri.

Bijiro da buƙatu na ƙarya: Suna amfani da labaran ƙarya k**ar cewa kuɗin mutum sun maƙale, ko ana ɗaukar ma'aikata domin su ja hankalinsa ya bayar da bayanai ko kuɗi.

02/09/2025
Jirgin ƙasan Abuja-Kaduna zai koma aiki nan da kwana 10Ministan sufurin Najeriya, Sa'idu Ahmed Alkali ya ce nan da kwana...
02/09/2025

Jirgin ƙasan Abuja-Kaduna zai koma aiki nan da kwana 10

Ministan sufurin Najeriya, Sa'idu Ahmed Alkali ya ce nan da kwana goma jirgin ƙasan Abuja-Kaduna da ya lalace zai koma aiki.

A makon jiya ne dai jirgin ƙasan ya kauce hanya, inda ya tunsture a kusa da tashar Asham bayan ya taso daga Abuja zai tafi Kaduna ɗauke da mutum 618, ciki har da har da fasinja 583 da ma'aikatan jirgin ƙasan guda 15 da ma'aikacin jinya 1 da masu goge-goge 11, sannan aƙalla fasinja bakwai ne s**a ji rauni.

A wata ziyara da ministan sufurin ya kai wajen da jirgin ya kauce hanya a jiyar Litinin, ya yaba da ƙoƙarin jami'an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki bisa ƙoƙarin da s**a yi wajen tabbatar da tsaron fasinjojin da sauran ma'aikatan jirgin har aka kwashe su.

"A lokacin da jirgin ya tuntsure, jirgin yana tafiya ne da tarago guda bakwai. Tuni mun kwashe guda huɗu, sannan muna ƙoƙarin kwashe sauran. Muna sa ran nan da kwana biyu za mu kwashe sauran taragon, sannan in sha Allah nan da kwana goma jirgin ƙasa zai koma aiki k**ar yadda ya saba," in ji ministan.

An bayyana jihohin arewacin Najeriya da za su iya fuskantar ambaliya a watan SatumbaHukumar kula da madatsun ruwa ta Naj...
02/09/2025

An bayyana jihohin arewacin Najeriya da za su iya fuskantar ambaliya a watan Satumba

Hukumar kula da madatsun ruwa ta Najeriya wato Nigeria Hydrological Services Agency (NiHSA) ta yi gargaɗin cewa aƙalla jihohin arewacin Najeriya guda 18 ne ke fuskantar barazanar ambaliya a mako biyu na farkon watan Satumban nan da aka shiga.

A wata sanarwa da hukumar ta fitar a shafinta na X, ta ce jihohin Najeriya 29 ne tare da Babban Birnin Tarayya Abuja suke fuskantar barazanar ta ambaliya a tsakanin 1 zuwa 15 ga watan Satumba.

Hukumar ta ce ambaliyar za ta iya shafar ƙananan hukumomi 107, da garuruwa 631, sannan aƙalla manyan titunan ƙasar 50 za su fuskanci tsaiko.

Daga cikin jihohin da s**a fi shiga barazanar, akwai Borno da Zamfara da Jigawa da Kebbi da Yobe da Filato da Gombe da Taraba da Sokoto, sannan akwai jihar Kaduna barazanar ba ta ƙarfi sosai.

Mene ne ke haddasa yawaitar ambaliyar ruwa a Najeriya?

Kauce wa X
Ya k**ata a bar bayanan X?
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X s**a bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Address

Lafia Beriberi
5050

Telephone

+2348037773271

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when MADUBI News 24/7 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to MADUBI News 24/7:

Share