MADUBI News 24/7

MADUBI News 24/7 MADUBI News 24/7

Su wane ne ke fafatawa a zaɓen gwamnan jihar Anambra?Hotunan ƴan takarar gwamnan AnambraAsalin hoton,SOLUDOBayanan hoto,...
08/11/2025

Su wane ne ke fafatawa a zaɓen gwamnan jihar Anambra?

Hotunan ƴan takarar gwamnan AnambraAsalin hoton,SOLUDO
Bayanan hoto,Hotunan ƴan takarar gwamnan Anambra
Sa'o'i 5 da s**a wuce
Ana gudanar da zaɓen gwamnan jihar Anambra Anambra da ke kudu maso gabashin Najeriya.

A wannan zaɓen, mutum 16 ne gaba ɗaya ke neman kujerar gwamnan Anambra ciki har da gwamna mai ci, Chukwuma Soludo, wanda ke neman tazarce.

Dubban jami'an tsaro ne aka jibge a jihar domin zaɓen, yayin da manyan 'yan takara s**a rattaɓa hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya, domin tabbatar da zaɓen cikin lumana da mutunta juna.

Ga wasu muhimman abubuwa da s**a kamata a sani game da 'yan takarar da ke fafatawa a zaɓen na gwamnan Anambra na 2025.

Charles Soludo ( Jam'iyya APGA)
Chukwuma SoludoAsalin hoton,CHUKWUMA SOLUDO

Chukwuma Charles Soludo shi ne gwamna na biyar da aka zaɓa ta tsarin dimokuraadiyya a jihar Anambra.

Yanzu haka yana neman wa'adi na biyu a karo na biyu kenan.

A lokacin zaɓen fitar da gwani na jam'iyyar APGA, Gwamna Soludo ne ya lashe zaɓen a lokacin domin babu wanda ya ƙalubalance shi.

Wane tasiri korar jami'an tsaro daga aiki ke yi a Najeriya?Ƙwararru a harkar tsaro na jan hankalin Najeriya dangane da y...
07/11/2025

Wane tasiri korar jami'an tsaro daga aiki ke yi a Najeriya?

Ƙwararru a harkar tsaro na jan hankalin Najeriya dangane da yawaitar korar jami'an tsaro daga aiki, bayan kwashe shekaru suna samun horo da tattara bayanan sirri.

A ranar Talata ne hukumar tsaro ta DSS ta ƙasar ta sanar da korar ma'aikatanta guda 115 daga aiki duk da dai hukumar ba ta fito fili ta faɗi dalilan korar ba, amma ta ce ta yi hakan ne sakamakon wasu sauye-sauye da take yi.

A makon da ya gabata ne rahotanni s**a karaɗe Najeriya kan raɗe-raɗin sallamar wasu manyan sojoji fiye da 100 sakamakon sauyin manyan hafsoshin tsaro a ƙasar da ya biyo bayan zargin kitsa juyin mulki.

Ana dai ganin cewa korar ma'aikatan tsaron daga aiki na da tasiri sosai ga tsarin tsaron ƙasar.

'Ba laifi ba ne korar mai laifi daga aiki'
Dakta Kabiru Adamu, shugaban kamfanin Beacon Security and Intelligence Limited, da ke nazari kan harkokin tsaro a yankin Sahel ya ce kamar kowane ma'aikaci a Najeriya, shi ma jami'in tsaro idan ya yi laifi za a iya korar sa.

"Babu shakka idan jami'in tsaro ya yi laifin da ya saɓa yarjejeniyar aiki da s**a saka hannu tsakaninsa da wanda yake yi wa aiki, doka ta bayar da damar a kore shi kamar kowane ma'aikaci. To amma idan ka dubi irin ƙwarewarsu da ilimin da suke da shi to irin wannan ne muke jan hankalin gwamnati a kai."

Dakta Kabiru Adamu ya ce korar ma'aikatan da hukumar DSS ta yi shi ne abin da ya fi tayar musu da hankali.

"Akwai yiwuwar sun aikata laifin da za a kore su. Wannan ba laifi ba ne. Amma yadda hukumar ta wallafa hotunansu. Wannan gaba ɗaya an ɓata musu rayuwarsu domin hakan zai iya shafar tunaninsu."

"Sannan akwai abin da a sashen bincike da ake kira "counter espionage" da ƙasashe ke ɗauka na hana bazuwar bayananta na sirri. To bayyana hotunansu zai bai wa ƙasashen da ke hamayya da Najeriya damar iya amfani da su waɗannan jami'an wajen tatsar bayanan da za a iya yi wa ƙasa zagon ƙasa," in ji Dakta Kabiru.

Hanyoyi uku na amfana daga waɗanda aka kora
Dakta Kabiru Adamu ya lissafa wasu hanyoyi guda uku da ya ce ya kamata hukumomin tsaro su bi domin hana tsoffin jami'an tsaron su shiga hannun masu yi wa tsarin tsaron ƙasar zagon ƙasa.

Ɓangaren ƙwararru: Wannan wani ɓangare ne da ake kafawa na ƙwararru da ake kira "thinktank" domin amfana daga basira da ƙwarewar da manyan jami'an tsaro da aka kora ko aka yi wa ritaya daga aiki ta yadda za su taimaka da ƙwarewarsu wajen tsare-tsaren ciyar da ƙasar gaba.
Sake tunaninsu: Wannan kuma wata dabara ce ta sake amfana daga ƙwarewar matsakaita ko ƙananan jami'an tsaro ta hanyar sake ba su horo da yi musu afuwa sannan kuma a saka su a wani tsarin tsaro na daban wanda ba na gwamnati ba wanda ake kira da 'Industrial Security'.
Bibiya: Wannan ma yana da muhimmanci samun alƙaluman jami'an da aka kora ko aka yi wa ritaya domin sanin wurin da suke da haƙiƙanin abin da suke yi ta hanyar bibiyar su. "Wani abu mai tayar da hankali shi ne yanzu babu irin waɗannan alƙaluman waɗanda s**a bar aiki da kuma abin da suke yi," in ji Kabiru Adamu.

Najeriya, ya ce wajibi ne kuma a kauce wa wannan zaluncin, sai fa idan Amurka so take ta yi maye fake da agana a Najeriy...
07/11/2025

Najeriya, ya ce wajibi ne kuma a kauce wa wannan zaluncin, sai fa idan Amurka so take ta yi maye fake da agana a Najeriya.

Birgediya Janar Muhammad Muhammad Yarima mai ritaya, ya ce „ Idan an kula za a ga a kwanannan Amurka ta matsawa Venezuela, ba wani abu bane illa mai, saboda kasar na da man fetir, to a Afirka ai Najeriya na da mai don haka shi y asa Amurka ta ke so ta shigo mata."

Ya ce," A zahiri Trump ba zai shigo Najeriya saboda ana kashe kiristoci ba saboda mai zai shigo, a don haka ya kamata gwamnatin Najeriya ta tashi tsaye don daukar matakin da ya dace."

Masanin tsaron ya ce, "Abin da ya kamata gwamnatin Najeriya ta yi shi ne ta tashi mutane masu mutunci da kima wadanda s**a san abubuwan da ke faruwa kamar jakadun da s**a yi ritaya a sa su su je Amurka su yi magana, sannan gwamnatin Najeriya ta rubuta wasika ta ce ba wai mun bari ana kshe kiristoci bane, a'a ga abin da ke faruwa sannan ga matakan da muke dauka su yi bayani dalla-dalla, amma ba wai a tsaya ana ta ce-ce-kuce a cikin gida ana yadawa a kafafan sada zumunta ba.

Masu iya magana dai kan ce, '' Ba a bori da sanyin jiki, kuma da zafi-zafi kan bugi karfe''.

05/11/2025

130.5K likes, 3828 comments. “China ta gargadi Donald Trump akan maganar kawo hari Nigeria… 🇳🇬 🇺🇸🇨🇳”

Inter Milan na zawarcin Guehi, Everton ta sanya ido kan JacksonInter Milan na sha'awar ɗaukar ɗan wasan bayan Ingila Mar...
01/11/2025

Inter Milan na zawarcin Guehi, Everton ta sanya ido kan Jackson

Inter Milan na sha'awar ɗaukar ɗan wasan bayan Ingila Marc Guehi, mai shekara 25, idan kwantiraginsa da Crystal Palace ya ƙare a bazara mai zuwa, amma ta na fuskantar hamayya daga Barcelona da ​​Bayern Munich da Real Madrid da kuma Liverpool. (Gazzetta dello Sport)

Everton na sa ido kan ɗan wasan gaba na Senegal Nicolas Jackson, mai shekara 24, yayin da Bayern Munich ke jan ƙafa wurin biyan fam miliyan 70 don siyan ɗan wasan gaban na Chelsea. (Football Insider).

Manchester United na zawarcin ɗan wasan tsakiya na Chelsea ɗan ƙasar Brazil Andrey Santos, mai shekara 21, a ƙoƙarinta na ƙarfafa ɓangaren ƴanwasan tsakiyarta a watan Janairu. (Football Insider).

01/11/2025
Me ayyana Najeriya a matsayin ƙasar da ake yi wa Kiristoci kisan gilla ke nufi?Wanda aka sabunta 31 Oktoba 2025Shugaban ...
01/11/2025

Me ayyana Najeriya a matsayin ƙasar da ake yi wa Kiristoci kisan gilla ke nufi?

Wanda aka sabunta 31 Oktoba 2025
Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar cewa zai saka Najeriya cikin jerin ƙasashe "da ake da damuwa a kansu" saboda zargin yi wa mabiya addinin Kirista kisan gilla.

Cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na dandalin Truth Social, Trump ya ce "shi ne mataki mafi ƙanƙanta da ya dauka" zuwa yanzu.

"Kiristanci na fuskantar babbar barazana a Najeriya," in ji shi. "Ana kashe dubban Kiristoci, kuma masu tsaurin kishin Islama ne ke aikata wannan kisan gillar. Saboda haka na ayyana Najeriya ƙasar da ake da damuwa a kanta".

01/11/2025
01/11/2025
01/11/2025

Address

Lafia Beriberi
5050

Telephone

+2348037773271

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when MADUBI News 24/7 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to MADUBI News 24/7:

Share