15/08/2024
DA DUMI-DUMINSA: Ka Zaɓi Kowace Ƙasa Daga Cikin Kasashen Afirka Domin Zama Jakada, Shugaba Tinubu Ga Ganduje
Saga Muhammad Kwairi Waziri
Shugaba Ƙasa Bola Tinubu ya baiwa shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje damar Zaɓar kowace kasa daga Afirka domin zama jakada.
Idan mai karatu bai mance ba an nada Ganduje a matsayin shugaban jam’iyya mai mulki na kasa ne a ranar 3 ga watan Agusta, 2023, biyo bayan murabus din da Abdullahi Adamu ya yi.
Majiya mai tushe ta tabbatar mana da cewa, yanzu haka tinubu ya fara wakilta Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio ya yi da ya gaya wa Ganduje.
A cewar majiyoyin, Mista Akpabio ya shaida wa shugaban jam’iyyar APC na kasa cewa tayin jakadan shugaban kasar na da nufin ceto shi daga shari’ar cin hanci da rashawa da yake fuskanta a Kano a halin yanzu.
Ganduje, wanda faifan bidiyon sa na cin hanci da rashawa a shekarar 2018 ya janyo masa baƙin jini da kuma ba'a, yana kuma fuskantar tuhumar cin hanci da rashawa tare da matarsa, dansa da sauran masu hannu da shuni na sama da Naira biliyan 50.
Sai dai majiyoyi na cikin gida sun ce Ganduje ya yi gunaguni lokacin da aka labarin ya iso shi, kuma ya ki amincewa da tayin shugaban kasar cikin dabara, yana mai bayanin cewa tuhume-tuhumen "nau'i ne kuma yawan cin su karya ne" kuma zai ci nasara a shari'arsa a kotu.
Ya ƙara da cewa “Shin haka ne shugaban kasa zai saka min? dan haka, na tsufa da yawa da zan iya rike jakadanci ba.
Kuma Duk tuhume-tuhumen da ake yi na karya ne, kuma zan ci nasara a shari’a ta a kotu,” a cewar Ganduje yayin da yake mayar da martani ga Akpabio.
Daga aga baya shugaban kasar ya sanar nawa Ganduje cewa ya bashi dama ya zaɓi duk ƙasar da yake a Afirka.
Sai dai wasu majiyoyi sun ce shugaban ya yi masa zabi uku a Afirka, Asiya da Turai.
Wata majiya da ke kusa da shugaban jam’iyyar APC ta ce abin da shugaban ya fi so shi ne ya nada shi jakadan Najeriya a kasar Chadi, bayan ya yi aiki a Ndjamena a matsayin babban sakataren hukumar kula da