Nasarawa HAUSA TV

Nasarawa HAUSA TV Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Nasarawa HAUSA TV, TV Channel, Lafia.

Shugaban hukumar, Farfesa Ibrahim Wushishi ya shaida wa BBC cewa jihar Kano ce kan gaba a yawan ɗaliban da s**a samu nas...
17/09/2025

Shugaban hukumar, Farfesa Ibrahim Wushishi ya shaida wa BBC cewa jihar Kano ce kan gaba a yawan ɗaliban da s**a samu nasara a jarrabawar a faɗin wuraren da hukumar ke shirya jarrabawar da s**a haɗa da wasu ƙasashen Afirka.

Karin bayani - https://bbc.in/46qRlxE

Likitocin sun kafa hujja da yawan sunadarai masu amfani da ke jikin fara saboda itatuwan da take ci.Shin da fara da nama...
17/09/2025

Likitocin sun kafa hujja da yawan sunadarai masu amfani da ke jikin fara saboda itatuwan da take ci.

Shin da fara da naman kaji ko na dabbobi, wanne kuka fi so?

With effect from midnight today, the State of Emergency in Rivers State is hereby lifted. Governor Siminalayi Fubara, De...
17/09/2025

With effect from midnight today, the State of Emergency in Rivers State is hereby lifted. Governor Siminalayi Fubara, Deputy Governor Ngozi Nma Odu, and the State House of Assembly will resume their constitutional duties from September 18, 2025.

My statement on the cessation of the State of Emergency in Rivers State.

Hukumar yaƙi da miyagun ƙwayoyi ta Najeriya NDLEA ta ce wasu gungun mutane ake zargi da manna sunayen ƴan Najeriyar uku ...
17/09/2025

Hukumar yaƙi da miyagun ƙwayoyi ta Najeriya NDLEA ta ce wasu gungun mutane ake zargi da manna sunayen ƴan Najeriyar uku a wasu akwatuna da ke ƙunshe da miyagun ƙwayoyin.

Ƙarin bayani - https://bbc.in/4n7xkn3

Ƙungiyar tuntuɓa ta arewacin Najeriya, ACF ta ce ƴan arewacin ƙasar na da damar fitowa takara duk da cewa wasu shugabann...
17/09/2025

Ƙungiyar tuntuɓa ta arewacin Najeriya, ACF ta ce ƴan arewacin ƙasar na da damar fitowa takara duk da cewa wasu shugabannin APC a yankin sun goyi bayan Shugaba Bola Tinubu ya zarce.

ACF ta ce hana wasu yin takara ya saɓa wa kundin tsarin mulki, kuma ya kamata jam'iyyar APC ta sake yin nazari kan batun.

Masha Allah
17/09/2025

Masha Allah

YABA KYAUTA: Ga Waƙar Ga Rangadawa Ɗan Bello Daga Abubakar Shehu Dokoki•Jama'a mu gaida Dan Bello cikakken Jarumi.•Ga 'y...
16/08/2024

YABA KYAUTA: Ga Waƙar Ga Rangadawa Ɗan Bello

Daga Abubakar Shehu Dokoki

•Jama'a mu gaida Dan Bello cikakken Jarumi.

•Ga 'yan Arewa yanzu ya zama tamkar malami.

•Wanda yake musu yaƙi babu wuƙa ko makami.

•Ya bankaɗo sirrin masu źàlunci wasu har ya sa su tagumi.

•Wayyoni Allah Duniya hàŕàm- a harami.

•Allah suna cutar mu kasa musu dogon źulumi.

•Shi kuma Dan Bello Allah Ka ba shi kariya Ka kare shi daga kowanne irin takunkumi.

•Ɗan Bello, Sadauki na gaske gwanin juriya!

•Masoyin Arewa da duk faɗin Nijeriya!

•Rashin irin.ku shi ya wargaza mana Nijeriya!

•Mun yi kuka mun zubar da hawaye da idaniya!

•Abin baƙin ciki kasarmu tana Hannun ƴan Sharholiya!

•Ba kowa gabansu sai son tarin dukiya!

•Sun barmu ba wuta, ba ilmi bare kiwon lafiya!

•Sun bautar da mu da yunwa mutane suna ta hajijiya!

•Mun yi da na sanin zaɓen su cikin su duk ba mai gaskiya!

•Kowa nace ciki har ehen...ɗik baki ɗaya!

•Allah Ka jiƙan su Tafawa da sauran Mazajen jiya!

•Mun yi kuka, rashin su har yau ba mu tsira ba.

Yaa Allah Ka ba shi kariya ba dan Halinmu ba.

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC na binciken Jalal Arabi kan zargin yin sama da faɗi da wani ɓangare na nair...
16/08/2024

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC na binciken Jalal Arabi kan zargin yin sama da faɗi da wani ɓangare na naira biliyan 90 da gwamnatin Najeriya ta bai wa Nahcon a matsayin tallafi ga aikin hajjin 2024 da ya gabata.

Karin bayani - https://bbc.in/3SPGk3a

Hukumar Zabe Ta Jihar Kano (KANSIEC) Ta De Duk Mai Son Tsayawa Takarar Ciyaman Sai Ya Sayi Fom Akan Naira Milyan Goma, K...
15/08/2024

Hukumar Zabe Ta Jihar Kano (KANSIEC) Ta De Duk Mai Son Tsayawa Takarar Ciyaman Sai Ya Sayi Fom Akan Naira Milyan Goma, Kansila Kuma Milyan Biyar

Me za ku ce?

DA DUMI-DUMINSA: Ka Zaɓi Kowace Ƙasa Daga Cikin Kasashen Afirka Domin Zama Jakada, Shugaba Tinubu Ga Ganduje Saga Muhamm...
15/08/2024

DA DUMI-DUMINSA: Ka Zaɓi Kowace Ƙasa Daga Cikin Kasashen Afirka Domin Zama Jakada, Shugaba Tinubu Ga Ganduje

Saga Muhammad Kwairi Waziri

Shugaba Ƙasa Bola Tinubu ya baiwa shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje damar Zaɓar kowace kasa daga Afirka domin zama jakada.

Idan mai karatu bai mance ba an nada Ganduje a matsayin shugaban jam’iyya mai mulki na kasa ne a ranar 3 ga watan Agusta, 2023, biyo bayan murabus din da Abdullahi Adamu ya yi.

Majiya mai tushe ta tabbatar mana da cewa, yanzu haka tinubu ya fara wakilta Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio ya yi da ya gaya wa Ganduje.

A cewar majiyoyin, Mista Akpabio ya shaida wa shugaban jam’iyyar APC na kasa cewa tayin jakadan shugaban kasar na da nufin ceto shi daga shari’ar cin hanci da rashawa da yake fuskanta a Kano a halin yanzu.

Ganduje, wanda faifan bidiyon sa na cin hanci da rashawa a shekarar 2018 ya janyo masa baƙin jini da kuma ba'a, yana kuma fuskantar tuhumar cin hanci da rashawa tare da matarsa, dansa da sauran masu hannu da shuni na sama da Naira biliyan 50.

Sai dai majiyoyi na cikin gida sun ce Ganduje ya yi gunaguni lokacin da aka labarin ya iso shi, kuma ya ki amincewa da tayin shugaban kasar cikin dabara, yana mai bayanin cewa tuhume-tuhumen "nau'i ne kuma yawan cin su karya ne" kuma zai ci nasara a shari'arsa a kotu.

Ya ƙara da cewa “Shin haka ne shugaban kasa zai saka min? dan haka, na tsufa da yawa da zan iya rike jakadanci ba.

Kuma Duk tuhume-tuhumen da ake yi na karya ne, kuma zan ci nasara a shari’a ta a kotu,” a cewar Ganduje yayin da yake mayar da martani ga Akpabio.

Daga aga baya shugaban kasar ya sanar nawa Ganduje cewa ya bashi dama ya zaɓi duk ƙasar da yake a Afirka.

Sai dai wasu majiyoyi sun ce shugaban ya yi masa zabi uku a Afirka, Asiya da Turai.

Wata majiya da ke kusa da shugaban jam’iyyar APC ta ce abin da shugaban ya fi so shi ne ya nada shi jakadan Najeriya a kasar Chadi, bayan ya yi aiki a Ndjamena a matsayin babban sakataren hukumar kula da

Masu zanga-zanga sun kwashe takardun shari'ar Ganduje a kotu - Gwamnatin KanoƘarin bayani: https://bbc.in/3X4DsCa
14/08/2024

Masu zanga-zanga sun kwashe takardun shari'ar Ganduje a kotu - Gwamnatin Kano

Ƙarin bayani: https://bbc.in/3X4DsCa

Dan Bello Ya Tafi Next Level, Inda A Wannan Karo Ya Bankaɗo Laifukan Matar Ganduje, Inda Aka Gano Ta Wawure Kuɗi Sama Da...
14/08/2024

Dan Bello Ya Tafi Next Level, Inda A Wannan Karo Ya Bankaɗo Laifukan Matar Ganduje, Inda Aka Gano Ta Wawure Kuɗi Sama Da Bilyan 20 A Asusun Gwamnatin Kano

Idan baku manta ba Dan Bello ya nemi APC a Kano da ta ba shi haƙuri ko ya cigaba da fallasa irin satar da s**a aikata, inda kuma s**a gagara yin haka.

A cewar sa matar Ganduje Hajiya Hafsat Ganduje lokacin da suke kan mulki kai tsaye ake tura kudi a asusun bankunan ta da ta buɗe har guda 44, adadin ƙananan hukumnin Kano.

Ta rinka sanya ana tura miliyoyin kuɗi ba tare da ɓoye-ɓoye ba, a ƙarshe an gano kamfanin tsohon Kwamishinan Kananan Hukumomin Kano Murtala Sule Garo ne ke fitar dasu.

Yanzu haka ana zargin ta da sace kuɗi sama da biliyan 20, daga asusun Gwamnatin jihar Kano.

Daga Salisu Editor

Address

Lafia

Telephone

+2349065643433

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Nasarawa HAUSA TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Nasarawa HAUSA TV:

Share

Category