11/08/2026
Hukumar Kare Hakkin Dan Adam ta Kasa (NHRC) ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta sanya DSS ko ta umarci Sufetor-Janar na Yan Sanda wajen gaggauta kamawa tare da gurfanar da fitaccen malamin addinin Musulunci Sheikh Sani Yahaya Jingir a gaban kuliya bisa zargin kalaman kiyayya da tayar da hankali kafin babban zaben 2027.
A cikin wata sanarwa da Sakataren Zartarwa, Chief Tony Ojukwu, SAN, ya sanyawa hannu, hukumar ta ce ta damu matuka da kalaman da aka danganta ga Sheikh Jingir a wani bidiyo da ke yawo a yanar gizo, wanda ta bayyana a matsayin abin kyama, abin tayar da hankali kuma mai iya haifar da rarrabuwar kawuna a addini.
A cewar hukumar, irin wadannan kalamai suna lalata ka'idojin daidaito, rashin nuna wariya da kuma zaman lafiya da aka tabbatar a karkashin Kundin Tsarin Mulkin Najeriya da kuma hakkokin dan adam na kasa da kasa.
NHRC ta bukaci Sufeto Janar na 'Yan Sanda, Darakta Janar na DSS da sauran hukumomin da abin ya shafa da su gaggauta daukar matakin yiwa Shehin Malamin Tabarma nan take,tare da gurfanar dashi a gaban kuliya idan bincike.
Me za ku ce?
Daga Saifullahi Lawal Imam.