VON Hausa

VON Hausa Manufa Da Tsari Tsage Gaskiya Komai Ɗa Cinta Shine Taken Mu VON Hausa Muryar Najeriya.

Shugaban jam'iyyar APC na jahar Kano Abdullahi Abbas ya fara aiki a hukumar kula da kayan Noma ta ƘasaBabban Kwamandan H...
23/07/2025

Shugaban jam'iyyar APC na jahar Kano Abdullahi Abbas ya fara aiki a hukumar kula da kayan Noma ta Ƙasa

Babban Kwamandan Hukumar kula da Tsaftar Kayayyakin Noma ta Ƙasa (NAQS), Dr. Vincent Isegbe, a yau ya karɓi shugaban kwamitin gudanarwa na NAQS, Alhaji Abdullahi Abbas, a ziyararsa ta farko a hukumance zuwa Hedkwatar hukumar da ke Abuja.

Shugaban kwamitin ya samu tarba mai kyau daga Babban Kwamanda tare da sauran membobin hukumar gudanarwa da jami’an da ke hedkwatar. A yayin zaman tattaunawa, Babban Kwamanda ya gabatar da cikakken bayani kan tsarin hukumar, ayyukanta, manufofin dabarunta, tare da irin rawar da take takawa wajen kare tattalin arzikin noma na Najeriya.

Da Dumi Dumi: Godswill Akpabio ya yi kuskure a wajen jawabi a majalisa, ya ce “jana’izar Tinubu” a maimakon Buhari.
23/07/2025

Da Dumi Dumi: Godswill Akpabio ya yi kuskure a wajen jawabi a majalisa, ya ce “jana’izar Tinubu” a maimakon Buhari.

Mataimakin Shugaban Najeriya, Alhaji Kashim Shettima, ya ziyarci Gwamna jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda a gidan gw...
23/07/2025

Mataimakin Shugaban Najeriya, Alhaji Kashim Shettima, ya ziyarci Gwamna jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda a gidan gwamnati dake birnin tarayya Abuja domin jajanta masa bisa ibtila'in Haɗarin motar da ya rutsa da shi a karshen makon da ya gabata.

Cikin hotuna: Wannan su ne motocin da Gwamnatin Jihar Kano ta tanada  Dan  Kawo Karshen Fadan Daba da Rashin Tsaro a jah...
23/07/2025

Cikin hotuna: Wannan su ne motocin da Gwamnatin Jihar Kano ta tanada Dan Kawo Karshen Fadan Daba da Rashin Tsaro a jahar a karkashin sabuwar hukumar tsaro mallakin Gwamnatin jahar Kano da ta samar.

Hotunan Gwamnan jihar Katsina bayan an sallamo shi daga Asibiti, inda yake cigaba da jinyar hannun shi.
23/07/2025

Hotunan Gwamnan jihar Katsina bayan an sallamo shi daga Asibiti, inda yake cigaba da jinyar hannun shi.

Jam’iyyar APC Ta Mayar da Taron NEC Zuwa Fadar Shugaban ƘasaJam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta sanar da sauya ...
23/07/2025

Jam’iyyar APC Ta Mayar da Taron NEC Zuwa Fadar Shugaban Ƙasa

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta sanar da sauya wurin da lokacin gudanar da taron Kwamitin Zartaswa na Ƙasa (NEC) da aka tsara gudanarwa a ranar Alhamis, 24 ga Yuli, 2025.

Taron, wanda da farko aka shirya gudanar da shi a hedikwatar jam’iyyar, yanzu za a yi shi a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.

Kasada da Rai: Yadda wani matashi a Jahun unguwar Liman a Bauchi yahau saman karfen sabis yace bazai saukaba sai dan gwa...
23/07/2025

Kasada da Rai: Yadda wani matashi a Jahun unguwar Liman a Bauchi yahau saman karfen sabis yace bazai saukaba sai dan gwamnan Jihar Bauchi Shamsudden Bala Abdulkadir Muhammad ya amince zaiyi takarar sanata a shekara ta 2027

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, ta sha alwashin sake maka Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, a gaban kotun da...
23/07/2025

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, ta sha alwashin sake maka Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, a gaban kotun daukaka kara, bayan wani abin kunya da ya faru da ita a ranar Talata, inda aka hana ta shiga harabar majalisar dokoki ta tarayya.

A cewar Natasha, ta bayyana cewa an hana ta damar shiga zauren majalisa duk da cewa tana da cikakken ikon wakiltar mazabarta har sai wata kotu ta ce akasin hakan.

Ta ce wannan mataki na nuna bambanci da tauye hakkin ta, kuma wani yunƙuri ne na hana ta gudanar da aikinta a dimokuradiyyannce.

Da Dumi Dumi: Labarin da muke samu cewa Daga wannan lokaci zuwa watan Disambar Bana za'a iya ruguje Shugabancin jam'iyya...
23/07/2025

Da Dumi Dumi: Labarin da muke samu cewa Daga wannan lokaci zuwa watan Disambar Bana za'a iya ruguje Shugabancin jam'iyyar APC daga matakin jaha har Mazabu a jahar Kano.

Da Dumi Dumi: Gwamnatin Jigawa za ta gina shaguna guda 1,000 a kasuwar Farm Center dake Kano a kan kudi Naira biliyan 3....
23/07/2025

Da Dumi Dumi: Gwamnatin Jigawa za ta gina shaguna guda 1,000 a kasuwar Farm Center dake Kano a kan kudi Naira biliyan 3.542.

Gwamnatin ta bayyana wannan ƙuduri a zaman majalissar zartarwa da aka gudanar na wannan sati, a wani shiri na gwamnatin domin zuba hannun jari da samun kuɗaɗen shiga.

An Cimma Matsaya Kan Biyan Haƙƙoƙin Masu Cin Gajiyar Shirin N-Power da Gwamnatin tarayya.A wani muhimmin mataki na warwa...
23/07/2025

An Cimma Matsaya Kan Biyan Haƙƙoƙin Masu Cin Gajiyar Shirin N-Power da Gwamnatin tarayya.

A wani muhimmin mataki na warware takaddamar dake tsakanin Gwamnatin Tarayya da masu cin gajiyar shirin N-Power, an cimma matsaya kan biyan haƙƙoƙin da ake binta. Wannan na zuwa ne bayan wani taron da ya gudana a tsakanin Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, da wakilan wadanda lamarin ya shafa, tare da lauyansu Abba Hikima.

Taron, wanda Ministan Harkokin Jin-ƙai, Nentawe Yilwatda, ya halarta, ya haifar da fahimtar juna inda dukkan bangarorin s**a amince da cewa za a biya bashin da ake binsu da zarar an fara aiwatar da kasafin kudin shekarar 2025.

Sanata Barau ya tabbatar wa manema labarai bayan kammala taron cewa wannan mataki zai kawo ƙarshen dogon zaman jiran da masu cin gajiyar shirin ke yi, tare da dawo da kwanciyar hankali tsakanin su da gwamnati.

Bashin Kasashen Waje: Majalisar Dattawan Najeriya ta sahale wa shugaban kasar Bola Ahmed Tinubu ya karbi bashi daga kasa...
23/07/2025

Bashin Kasashen Waje: Majalisar Dattawan Najeriya ta sahale wa shugaban kasar Bola Ahmed Tinubu ya karbi bashi daga kasashen ketare da ya kai sama da dala biliyan 21 domin kashewa Najeriya tsakanin shekarar 2025 zuwa 2026.

Address

Maiduguri

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when VON Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share