Qugiya Hausa

Qugiya Hausa Qugiya Hausa Jarida ce ta Online dake Kawo Maku Ingatattun Labaran Cikin Gida Najeriya da Kasashen Ketare.

Idan Kuna Buƙatar Tallace-tallace Ku Tuntuɓi Wannan Number 👉09044351991

Fitaccen Dan Social Media G-Fresh Alameen Ya ce  Bayan Aurensa Samun sa Ya Karo sosai, Inda Yanzu Duk Wata Yana Samun Mi...
09/08/2025

Fitaccen Dan Social Media G-Fresh Alameen Ya ce Bayan Aurensa Samun sa Ya Karo sosai, Inda Yanzu Duk Wata Yana Samun Miliyan 4 a Manhajar Tiktok

Me Za ku ce?

Dan uwa ga Jaruma Rahama Sadau, Abba Sadau Ya ce Saboda Maganganun Mutane Na Baƙin Ciki da Hassada Ya sa Muka Rufe Magan...
09/08/2025

Dan uwa ga Jaruma Rahama Sadau, Abba Sadau Ya ce Saboda Maganganun Mutane Na Baƙin Ciki da Hassada Ya sa Muka Rufe Maganar Auren Rahama Sadau Har Sai Bayan Da Aka Ɗaura Auren

Da dumi'dumi: Gwamnatin jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sa an k**a wanda ya ya tattaki daga j...
09/08/2025

Da dumi'dumi: Gwamnatin jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sa an k**a wanda ya ya tattaki daga jihar Jigawa zuwa kano domin jinjina masa bisa ga soyayyarsa ga talakawan jihar Kano, a wani sako daya aikewa Jaridar Mikiya Kwamarad Lawan Habibu dutse yana cewa Jami'an gidan gwamnati sun dauke ni sunkaini Police division na Phone center sun Ajiye ban san dalilin yin hakan ba.

Mai Girma Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyayen Marigayi Sadik Gentle Wanda Wasu...
09/08/2025

Mai Girma Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyayen Marigayi Sadik Gentle Wanda Wasu Bata Gari S**a Shiga Har Gida S**a Sassara Sadik Gentle Dai Hadimi Ne Ga Gwamnan Kanon Inda Yake a Matsayin Babban Mai Dakko Masa Rahoto a Ma’aikatar Tarihi Da Al’Adu (SSR History and Culture)

Allah Ya Jikan Gentle Ya Tona Asirin Wayanda S**ayi Masa Wannan Zaluncin.

Hotuna Daga 📸 Muhammad Kibadash

YANZU-YANZU: An ɗaura auren jaruma Rahama Sadau yau Asabar a Kaduna Rahotanni sun bayyana cewa an ɗaura auren shahararri...
09/08/2025

YANZU-YANZU: An ɗaura auren jaruma Rahama Sadau yau Asabar a Kaduna

Rahotanni sun bayyana cewa an ɗaura auren shahararriyar jarumar Kannywood Rahama Sadau tare da angonta Ibrahim Garba.

An ɗaura auren yau Asabar a masallacin Masallacin Atiku Auwal Unguwan Rimi k**ar yadda wasu makusantan ta s**a tabbatar.

— Jaridar Arewa

Zan mutu ranar Lahadi bayan na gama wa'azi a coci, in ji Fasto Adeboye Babban Faston Cocin Redeemed Christian Church of ...
09/08/2025

Zan mutu ranar Lahadi bayan na gama wa'azi a coci, in ji Fasto Adeboye

Babban Faston Cocin Redeemed Christian Church of God (RCCG), Fasto Enoch Adejare Adeboye, ya sake bayyana hasashe kan yadda zai rabu da duniya.

Ya ce zai mutu cikin lumana, a ranar Lahadi, bayan ya halarci cocin kuma ya ci sakwara, abincin da yafi so.

Da ya ke jawabi a rana ta huɗu na babban taron cocin na kasa da kasa mai taken “The Overcomers”, Fasto Adeboye ya jaddada cewa mutuwa ba sai da ciwo ba.

Jaridar PUNCH ta rawaito cewa Faston ya taba bayyana wannan hasashen shekaru biyu da s**a gabata, inda ya ce: “Zan mutu ne a ranar Lahadi, bayan na halarci coci, na ci sakwara da nake so, sannan in rabu da duniya ba tare da wani ciwo ba.”

Faston ya ce mutuwarsa za ta kasance ta gaggawa kuma salin-alin zai mutu.

Alarammomi da malamai masu kula da tsangayun Alkur’ani a Jihar Kano sun nemi Gwamnatin Kano ta tabbatar da kulawa ta mus...
09/08/2025

Alarammomi da malamai masu kula da tsangayun Alkur’ani a Jihar Kano sun nemi Gwamnatin Kano ta tabbatar da kulawa ta musamman ga tsangayun karatun Alkur’ani a fadin jihar.

Wannan na cikin sanarwar da Kungiyar Tsangaya Abar Alfaharinmu ta fitar mai dauke da sa hannu Shuagbanta Alaramma Muhammad Sani Musa Nuhu (Sanin Malam).

Ya ce, suna neman a saka wakilin tsangayu a cikin Majalisar Koli ta Malamai da aka kafa, a samar da fitulun sola a dukkan tsangayu, a dinga ware musu kaso a kasafin kudin kowace shekara, da kuma gina rumfunan karatu, bandakuna da dakunan kwana ga almajirai.

Sauran bukatun sun hada da samar da ruwan sha, muhalli na dindindin, karrama fitattun alarammomi, sanya almajirai cikin shirye-shiryen koyon sana’a da raba jari da kuma samun kaso a tallafin takin zamani.

Sanarwar ta kuma yi godiya ga Gwamnan kan nadin Gwani Musa Falaki a matsayin mai taimakawa gwamna kan harkar tsangayu, tare da jinjina wa tsohon Gwamna Kwankwaso bisa ɗaukar nauyin koyar da almajirai kyauta.

09/08/2025

Ƙungiyar Tsangaya Abar Alfaharimmu Ta Aika Wa Gwamnan Kano Wasiƙar Buƙatar Tallafi

Ƙungiyar Tsangaya Abar Alfaharimmu ta rubuta wasiƙa ga Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, tana bayyana godiya kan irin gudunmawar da yake bayarwa tare da roƙon ƙarin kulawa da tallafi ga almajirai da malamansu.

A wasiƙar, ƙungiyar ta yaba da jajircewar gwamnan wajen yakar zalunci da tabbatar da adalci, tare da kiran gwamnati ta ci gaba da ɗaukar nauyin lafiya da walwalar almajirai a fadin jihar.

ALLAHU AKBAR: Irfan Khan kenan jarumin da ya musuluntar da mutane 1200 daga addinin Hindu zuwa Musulunci.Sanadiyyar haka...
09/08/2025

ALLAHU AKBAR: Irfan Khan kenan jarumin da ya musuluntar da mutane 1200 daga addinin Hindu zuwa Musulunci.

Sanadiyyar hakan aka ɗaure shi har na tsawon shekaru huɗu a gidan yari kuma daga ƙarshe Allah yayi masa rasuwa a shekarar 2020.

Allah yajikansa da sauran Musulmi baki daya.
______ Sashin Tallace -Tallace ______

Kamfanin Dillacin Labarai Na Jaridar QUGIYA HAUSA Ya Shirya Tsaf Domin Tallata Maku 👇

1) Kasuwancin Ku
2) Ra'ayoyinku
2) Siyasa
4) Bukatunku, Korafe-korafe
5) Tallata Dan Siyasar Ku, Ko Ayyukansa
6) Gayyata Ko Tarukan Ku
7) Tunawa Da Zagayowar Haihuwa
8) Kokenku Ga Ɗan Siyasa

Da Sauransu Cikin Farashi Mai Sauki Ko Hulda Da Mu, Ku Aiko Mana Da Sakonnin A WhatsApp 09044351991.

Sai Kun Zo....

Za A Fara Wayar Da Kan 'Yan Najeriya Kan Sabbin Ka'idojin Neman Bizar Amurka Gwamnatin Tarayya ta haɗa gwiwa da Ofishin ...
08/08/2025

Za A Fara Wayar Da Kan 'Yan Najeriya Kan Sabbin Ka'idojin Neman Bizar Amurka

Gwamnatin Tarayya ta haɗa gwiwa da Ofishin Jakadancin Amurka a Nijeriya domin wayar da kan ‘yan Nijeriya kan sababbin ƙa’idojin neman bizar Amurka tare da tabbatar da bin ƙa’ida yayin neman.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana haka a taron manema labarai da ya gudana tare da Jakaden Amurka a Nijeriya, Richard M. Mills Jr., a Abuja ranar Juma’a.

Ya ce wannan yekuwar wayar da kan ta zama dole saboda Amurka tana ci gaba da zama ɗaya daga cikin wuraren da ‘yan Nijeriya suke yawan ziyarta.

Idris ya ce a tsawon shekaru ‘yan Nijeriya suna tafiya Amurka saboda dalilai daban-daban, ciki har da yawon buɗe ido, kasuwanci, karatu, da kuma neman magani.

Ya ce: “An san Nijeriya a duniya a matsayin ƙasar da ‘yan ƙasar ta suke yawan yin tafiya zuwa ƙasashe daban-daban, suna hulɗa da ƙasashen duniya ta fuskar harkar kasuwanci, ilimi, yawon buɗe ido, da sauran muhimman fannoni. Amurka na ci gaba da kasancewa ɗaya daga cikin wuraren da ‘yan Nijeriya s**a fi ziyarta, abin da ke nuna zurfin dangantaka mai tsawo tsakanin ƙasashen biyu.

“Yawancin ‘yan Nijeriya suna zuwa Amurka ne domin karatu, aiki, neman magani, ziyartar ‘yan'uwa, yawon buɗe ido, da damar zuba jari.

"Wannan mu’amala mai ƙarfi tana ci gaba da bunƙasa al’ummomin biyu.

"Sababbin abubuwan da Ofishin Jakadancin Amurka ya bayyana game da sauye-sauye a ayyukan ofishin jakadancin da hanyoyin neman bizar sun jima suna cikin labarai kwanan nan.

“Waɗannan sauye-sauyen, k**ar yadda Ofishin Jakadancin Amurka ya bayyana, wani ɓangare ne na ƙoƙarin inganta bayar da sabis, ƙara saurin aiki, da mayar da martani ga sauye-sauyen buƙatun ayyukan jakadanci.”

Ministan ya yaba wa gwamnatin Amurka bisa ƙoƙarin yin bayani kai-tsaye ga ‘yan Nijeriya a wannan taro tare da tabbatar da samun sahihan bayanai na zamani ga kowa.

Haka kuma ya jaddada girmamawa da haɗin gwiwa tsakanin Nijeriya da Amurka da kuma jajircewar Ofishin Jakadancin wajen sanar da matafiya ‘yan Nijeriya.

A nasa jawabin, Jakaden Amurka, Ambasada Mills, ya ce bin ƙa’idojin neman biza da dokokin Amurka na ‘yan Nijeriya abu ne mai muhimmanci wajen ƙarfafa dangantaka tsakanin ƙasashen biyu.

“Bin dokokin neman biza na Amurka ba kawai wani nauyi ba ne, amma ginshiƙi ne na amincewa da girmama juna tsakanin ƙasashen biyu,” inji Ambasada Millis.

Ya ƙara da cewa: “Kamar yadda Minista ya bayyana, ni da shi mun yi tattaunawa mai amfani game da dokokin biza na Amurka da kuma yadda za mu isar wa ‘yan Nijeriya muhimmancin bin waɗannan dokokin.

“Bari in fayyace cewa Amurka tana daraja ƙarfaffar dangantakar ta da Nijeriya da kuma nau’o’in hulɗa da yawa da ke tsakanin ƙasashen biyu.

"Bizar Amurka na taka muhimmiyar rawa wajen ci gaba da riƙe waɗannan lamurran dangantaka da ƙarfafa su, ko ta hanyar bai wa mutane damar tafiya domin ilimi, kasuwanci, yawon buɗe ido, ko musayar al’adu.”

Jakaden ya jaddada cewa ya zama dole a yi amfani da biza bisa ga dokoki da ƙa’idojin Amurka.

Ya ce: “Tabbas, muna maraba da baƙi ‘yan Nijeriya a Amurka k**ar yadda Nijeriya take maraba da ‘yan Amurka masu zuwa wannan ƙasa. Dukkan gwamnatoci suna son baƙi su girmama dokokin ƙasashen mu da ƙa’idojin mu.”

Ya gargaɗi masu neman biza cewa yin amfani da ita ba bisa ƙa’ida ba ko bayar da bayanan ƙarya yayin neman ta yana iya rage amincewar juna a tsakanin ƙasashen biyu.

Ya ce: “Muna kira ga dukkan masu neman biza da su bayar da sahihan bayanai kuma su bi sharuɗɗan biza ɗin su, domin na sani, mafi yawan ‘yan Nijeriya suna yin hakan. Ta yin haka, za mu ƙarfafa ɗorewar zumunci tsakanin ƙasashen mu.”

Ambasada Mills ya kuma yaba wa Idris bisa jajircewar sa wajen kare ‘yancin faɗar albarkacin baki a Nijeriya, yana mai jaddada cewa wannan ɗabi'a ce da ta yi daidai da manufofin Amurka.

Ya kuma yaba wa haɗin kai da ake samu daga hukumomin Nijeriya, ciki har da Hukumar Wayar da Kan Jama’a ta Ƙasa, Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya, Hukumar Kwastan ta Nijeriya, da Fadar Shugaban Ƙasa, wajen wayar da kan jama’a kan ƙa’idojin biza.

Haka kuma ya shawarci ‘yan Nijeriya da su nemi sahihan bayanai daga shafin soshiyal midiya na Ofishin Jakadancin Amurka kuma su tabbatar da cewa duk wata tambaya da suke da ita za su samu amsa cikin lokaci.

Tsohon gwamnan jihar Kano Malam Ibrahim Shekarau ya kai wa ɗan gwagwarmaya Bello Galadanci (Ɗan Bello) ziyarar ta'aziyya...
08/08/2025

Tsohon gwamnan jihar Kano Malam Ibrahim Shekarau ya kai wa ɗan gwagwarmaya Bello Galadanci (Ɗan Bello) ziyarar ta'aziyya bisa rasuwar mahaifinsa Malam Habib.

YANZU-YANZU Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023 Peter Obi ya sauka birnin Bauchi domin ziyarar duba wasu Makar...
08/08/2025

YANZU-YANZU

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023 Peter Obi ya sauka birnin Bauchi domin ziyarar duba wasu Makarantu.

📷- Albarka Radio

Address

Kano

Telephone

+2349033391934

Website

http://Qugiyahausa.com.ng/

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Qugiya Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Qugiya Hausa:

Share