Qugiya Hausa

Qugiya Hausa Qugiya Hausa Jarida ce ta Online dake Kawo Maku Ingatattun Labaran Cikin Gida Najeriya da Kasashen Ketare.

Idan Kuna Buƙatar Tallace-tallace Ku Tuntuɓi Wannan Number 👉09044351991

Tinubu ya umarci sabbin hafsoshin tsaro su zama masu hazaƙa wajen yakar ta’addanci da barazanar tsaroShugaban Najeriya B...
30/10/2025

Tinubu ya umarci sabbin hafsoshin tsaro su zama masu hazaƙa wajen yakar ta’addanci da barazanar tsaro

Shugaban Najeriya Bola Ahmad Tinubu ya bukaci sabbin hafsoshin tsaro da ya nada su kasance masu samar da sabbin dabaru da jajircewa wajen tinkarar ta’addanci da barazanar tsaro da ke addabar kasar.

Shugaban ya bayyana hakan ne a lokacin da yake karrama sabbin hafsoshin tsaro da mukamansu a fadarsa da ke Abuja ranar Alhamis.

Tinubu ya bayyana wannan yunƙurin a matsayin wata sabuwar aniya da jajircewar gwamnati wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro ga ‘yan Najeriya baki ɗaya.

“Yau ba wai bikin ba da mukamai kawai muke yi ba, muna sabunta kudirinmu na tabbatar da zaman lafiya da tsaro a ƙasa. Sojojinmu sun bayar da gudunmawa mai girma wajen kare ƙasar nan, wasu ma sun sadaukar da rayukansu don zaman lafiyar Najeriya,” in ji shi.

Shugaban ya yaba da kokarin dakarun soji wajen dawo da zaman lafiya a yankunan da aka taba samun rikice-rikice da kuma ceto mutanen da aka yi garkuwa da su, yana mai cewa hakan ya raunana ƙungiyoyin ta’addanci da ke ƙasar.

Sai dai ya gargadi sabbin hafsoshin cewa barazanar tsaro tana ta sauyawa, inda sabbin ƙungiyoyin ‘yan bindiga da masu tayar da hankali ke fitowa musamman a Arewa ta Tsakiya, Arewa maso Yamma da wasu sassan Kudu.

“Ba za mu bari wannan barazanar ta ci gaba yaduwa ba. Dole mu yi gaggawa mu murƙushe su tun kafin su yi ƙarfi. Mu sare kan macijin tun wuri,” in ji Tinubu.

Ya kuma shawarce su da su yi amfani da fasahar zamani da sabbin dabaru domin su kasance gaba da waɗanda ke barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali na ƙasa.

“Ina so ku zama masu samar da sabbin dabaru, masu hangen nesa da jarumtaka. ‘Yan Najeriya suna jiran sakamako, ba ƙorafi ba,” in ji shugaban.

Shugaban ƙasar ya kuma sake tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da tallafa wa rundunonin soji da kayan aiki da duk wata bukata don cimma nasarar aiki.

A jawabinsa bayan karramawar, Babban Hafsan Tsaron ƙasa, Janar Olufemi Oluyede, wanda ya yi magana a madadin sauran hafsoshin, ya tabbatar da cewa za su yi aiki tare don magance matsalolin tsaro da ke addabar ƙasar.

“Ina tabbatar wa Shugaban ƙasa da ‘yan Najeriya cewa za mu yi iyakar kokarinmu wajen kawar da duk wani nau’in laifi da ta’addanci a Najeriya, domin a samu damar bunƙasar harkokin tattalin arziki da zaman lafiya,” in ji shi.

A cikin waɗanda aka karrama akwai Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, Laftanar-Janar Waidi Shaibu; Babban Hafsan Rundunar Ruwa, Vice Admiral Idi Abbas; Babban Hafsan Rundunar Sama, Air Marshal Sunday Aneke; da kuma Babban Daraktan Leken Asiri na hukumar Tsaro, Laftanar-Janar Emmanuel Undiandeye.

Bikin ya samu halartar iyalan hafsoshin da matayensu, inda s**a rantse da alkawarin bin doka da tsayawa kan rantsuwar ofis a gaban Shugaban ƙasa.

Ina Bama masoya hakuri bisa shawara da suketa bamu akan tsayawa takaran kujerar shugaban matasan Jam'iyyar APC ta Jahar ...
29/10/2025

Ina Bama masoya hakuri bisa shawara da suketa bamu akan tsayawa takaran kujerar shugaban matasan Jam'iyyar APC ta Jahar Kaduna.

Bisa hakan yasa nake karaba ba masoya Na birni da karkara hakuri cewa muna kan cigaba da tuntubar magabatan mu masu Ruwa Da tsarki akan lamarin, Wanda Nan gaba kadan zamu sanarda matsayar mu officially, Mungode bisa kyautata mana zato.

Hon. Saifullahi chiroma kauranwali

📰 SANARWAR MANEMA LABARAI (PRESS RELEASE) DAGA SANIN MALAM SMNMu Ahalin Tsangayun Al-Kur’ani Mun Yi Tir Da Allah Wadai N...
29/10/2025

📰 SANARWAR MANEMA LABARAI (PRESS RELEASE) DAGA SANIN MALAM SMN

Mu Ahalin Tsangayun Al-Kur’ani Mun Yi Tir Da Allah Wadai Na Ƙaryar da Gidan Jaridar Rariya Ya Yaɗa

Mu Ahalin Tsangayun Al-Kur’ani muna bayyana cikakken takaicimmu na ƙaryar da gidan jaridar Rariya ya yaɗa, inda s**a ƙirƙiro labari marar tushe da hujja na Kanzan Kurege s**a jingina wa almajirai.

Wannan batu ƙarya ne tsagwaronta, kuma ya saba da gaskiya da ɗabi’ar aikin jarida.
Muna kira ga dukkan masu yada jita-jita da labaran ƙarya da su guji jingina mana abubuwan da bamu da wata alaƙa mu da su.

Tsangayun Al-Kur’ani ba za mu lamunta a ci gaba da wasa da mutuncinmu, da mutuncin malamanmu da almajiranmu ba.
Muna kira ga hukumomin da abin ya shafa su ɗauki matakin gyara da neman afuwa ga al’umma.

> “Idan kunne ya ji — to....!!!!!
idan kuma an ƙi ji, tabbas ba a gani ba.”

Tsangaya Abar Alfaharim Mu
✍️ Sanin Malam SMN
📅 29/10/2025

Ba a tauye ’yancin addini a Nijeriya, inji  Ministan Yaɗa Labarai a hirar CNNMinistan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alha...
29/10/2025

Ba a tauye ’yancin addini a Nijeriya, inji Ministan Yaɗa Labarai a hirar CNN
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu tana ƙara maida hankali wajen magance matsalolin tsaro a ƙasar nan domin tabbatar da tsaro da walwalar ’yan ƙasa.

Da yake magana a cikin wata hira da gidan talbijin na CNN ya yi da shi a London a daren Talata, Idris ya ƙaryata iƙirarin da wasu jami’an ƙasashen waje suke yi cewa wai ’yan ta’adda a Nijeriya suna kai hare-hare ne kan Kiristoci kawai.

Ya bayyana cewa irin waɗannan iƙirari ba su da tushe kuma ba su bayyana haƙiƙanin yanayin tsaron ƙasar nan, inda ya jaddada cewa ’yancin yin addini yana cikin kundin tsarin mulkin Nijeriya.

Ya ce: “Wasu daga cikin iƙirarin da wasu jami’an Amurka s**a yi sun ta’allaƙa ne kan bayanai marasa inganci da kuma zato cewa yawancin waɗanda ake kai wa hare-hare Kiristoci ne. E, ana kai wa Kiristoci hari, amma waɗannan miyagun ba mabiya addini ɗaya kawai suke kai wa farmaki ba. Suna kai wa Kiristoci hari, suna kuma kai wa Musulmi hari, musamman a arewacin ƙasar.”

Idris ya ce masu yaɗa irin waɗannan labaran ƙaryar suna taimaka wa ’yan ta’addar ne, saboda manufar ’yan ta’adda ita ce su haddasa rikici tsakanin Musulmi da Kiristoci a ƙasar.

Ya ƙara da cewa Nijeriya ƙasa ce da ta yi yarda da bambancin addinai, don haka yaɗa labaran ƙarya na nuna rashin jituwa zai iya haifar da rarrabuwar kai.

Ya ce: “Kiran lamarin da cewa hare-haren kan Kiristoci ne kawai zai iya haifar da rarrabuwar kai a Nijeriya. Miyagun suna son a ɗauka kamar ana faɗa ne tsakanin Musulmi da Kiristoci. Mun shaida akwai hare-hare kan Kiristoci, kuma mun shaida akwai hare-hare kan Musulmi. Amma ba daidai ba ne a ce Nijeriya ƙasa ce da ba ta mutunta ’yancin addini, ko a ce ko'ina babu tsaro a Nijeriya. Nijeriya ƙasa ce mai aminci.”

Ministan ya amince cewa akwai matsalolin tsaro, amma kuma gwamnati tana ɗaukar matakai masu ƙarfi da tsari don magance su.

Ya bayyana cewa gwamnati ta ƙarfafa rundunonin tsaro tare da zuba jari a fannoni kamar noma da ayyukan jinƙai domin ƙarfafa zaman lafiya.

Ya ce: “Ko canje-canjen da aka yi na shugabannin hafsoshin tsaro kwanan nan duk don a ƙarfafa tsarin tsaron ƙasar ne, domin gwamnati ta iya magance kowace irin matsala a kan lokaci.”

29/10/2025

YANZU YANZU
Munyi raga raga da farashin Mtn Data Ku duba a comment section 👇👇

Ina rokon matasan malamnu na sunnah masu amfani da social Media da su shaltu wurin yada abunda zai amfanar da al'umma ka...
29/10/2025

Ina rokon matasan malamnu na sunnah masu amfani da social Media da su shaltu wurin yada abunda zai amfanar da al'umma kamar gyaran akida ibada da kyawawan dibiun manzon Allah (S.A.W) kuma shuguji bacin juna akan mas'aloli na kashin kai.

Fitaccen Malamin Addinin Musulunci Farfesa Isa Ali Pantami ya buɓaci a samar da hukumar tantance masu wa'azi a Nijeriya,...
29/10/2025

Fitaccen Malamin Addinin Musulunci Farfesa Isa Ali Pantami ya buɓaci a samar da hukumar tantance masu wa'azi a Nijeriya, A ƙarƙashin Sarkin Musulmi Sa'ad Abubakar III.

Farfesa Pantami ya bayyana haka ne a cikin wata hira da ya yi da DW Hausa.

“Ni bana goyon bayan Gwamnati kai tsaye ta ɗauki mataki kan bada damar yin wa'azi ko hanawa, tsarin da nike tunani shi ne ƙarƙashin Sultan ya zama akwai tsari na samar da a kowace jiha za a haɗa kungiyoyi na Addini a samu wakilci JNI, wakilci na Izalah, wakilci na Tijaniyya na Ƙadiriyya, wakilci na musulmai lauyoyi, wakilci na duk wadanda s**a dace.

“Ya zama kowace jiha akwai wakilai da za a haɗa, a bada ƙa'idoji, ayi Legislative da Musulmai ya zama su za su yi dokar, ya zama wannan suna da ikon su daga jiha ƙarƙashin shugabancin Sultan su riƙa bibiyar masu wa'azin, wani ana masa kashedi, wani idan ta gagara a dakatar da shi, idan yaƙi dakatuwa sai hukuma ta shigo ciki”. Inji shi.

KUN JI KO: “Duk wanda ya isa anan cikin Jihar Kano, amma bai buɗe bakinsa wajen kare Annabi (S.A.W) ba, babu shakka wann...
29/10/2025

KUN JI KO: “Duk wanda ya isa anan cikin Jihar Kano, amma bai buɗe bakinsa wajen kare Annabi (S.A.W) ba, babu shakka wannan mutum yana da rauni wajen ƙauna gareshi (S.A.W) kuma makiyin sane Qada'an.

Wannan magana ta shafi kowa — daga sarakuna, ‘yan siyasa, attajirai, malamai (musamman waɗanda ke intisabi da darika), har zuwa talakawa. Mu sani, kare Annabi (S.A.W) wajibi ne ga kowane musulmi.”

Sanin Malam
28/10/2025

KA JI MAZA: Rashin Adalci Ne Sai Ƴan Afrika Sun Rubuta Jarabawar Turanci Ko Faransanci Kafin Su Samu Izinin Shiga Turai,...
28/10/2025

KA JI MAZA: Rashin Adalci Ne Sai Ƴan Afrika Sun Rubuta Jarabawar Turanci Ko Faransanci Kafin Su Samu Izinin Shiga Turai, Amma Yan Turai Suna Shigowa Afirka Cikin Sauƙi Ba Tare Da Koyon Harshen Yankin Kamar Hausa, Zulu Ko Shona Ba - Kyftin Ibrahim Traoré

Shugaban Burkina Faso, Captain Ibrahim Traoré, ya bayyana rashin adalci a dokokin da ke tsara yadda Yan Afirka ke tafiya zuwa ƙasashen Turai.

A wani taron jama’a da ya halarta, Traoré ya tambayi dalilin da yasa dole ne ‘yan Afirka su rubuta jarabawar Turanci ko Faransanci kafin su samu izinin shiga Turai, amma ‘yan Turai kuma suna shigowa Afirka cikin sauƙi ba tare da koyon harshen yankin kamar Hausa, Zulu ko Shona ba.

Ya ce wannan dabi’ar tana nuna halin mulkin mallaka da har yanzu ake gani a hulɗar Turai da Afirka, yana kuma kira ga ƙasashen Afirka su tsaya kai da fata wajen neman daidaito.

Maganarsa ta jawo muhawara mai zafi a kafafen sada zumunta, inda mutane da dama s**a yaba da tsayuwarsa wajen kare mutuncin Afirka.

Shin kuna ganin ya kamata ƙasashen Afirka su fara tilasta wa ‘yan Turai su koyi harsunanmu kafin su shigo ƙasashenmu?

📷/: Kyaftin Ibrahim Traore/[File Photo]

28/10/2025

YANZU YANZU
Masu amfani da mtn data na cikin alheri dumu-dumu, su duba comment Section domin samun data mai rahusa 👇

TIRƘASHI: Duka guda Balalau yayiwa Masuss**a sai gashi ya koma darika,kunga anyi nasara, a cewar wannan matashin.
27/10/2025

TIRƘASHI: Duka guda Balalau yayiwa Masuss**a sai gashi ya koma darika,kunga anyi nasara, a cewar wannan matashin.

TO FA: Tinda kunbi masuss**a ya kamata kudena maulidi a qurani de baa ambaci ranar haihuwar Annabi ba dole sede a hadith...
27/10/2025

TO FA: Tinda kunbi masuss**a ya kamata kudena maulidi a qurani de baa ambaci ranar haihuwar Annabi ba dole sede a hadith ko sira.

A cewar Matashin Dan Social Media Mubaraky.

Me Za Ku Ce?

Address

Kano

Telephone

+2349033391934

Website

http://Qugiyahausa.com.ng/

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Qugiya Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Qugiya Hausa:

Share