Borno news 24

Borno news 24 Domin kawo muku ingantuttun labaran gida Najeriya harma da kasashen ketare à harshen Hausa

07/02/2023

Allahouma sali wa salim wa barik ala Nabina Mouhamad

Zaɓen Najeriya na 2023: APC da PDP na amfani da sabon salo na aiwatar da sauye-sauye  Sa'o'i 6 da s**a wuceManyan jam'iy...
06/05/2022

Zaɓen Najeriya na 2023: APC da PDP na amfani da sabon salo na aiwatar da sauye-sauye

Sa'o'i 6 da s**a wuce
Manyan jam'iyyun siyasar Najeriya
Manyan jam`iyyun siyasar Najeriya biyu, wato APC da PDP sun fitar da wani sabon salo na aiwatar da sauye-sauye a cikin jadawalinsu na babban zaben da ke tafe.

Irin wannan sauyin kan shafi lokutan gudanar da zaben fid da gwani ko sayar da fom ga masu neman tsayawa takara, wanda wasu `yan kasar ke cewa yana daure musu kai.

APC da PDP, duka sun buge da wata dabi`a ta sassauya ranakun da suke tsayarwa don aiwatar da wadansu muhimman hidimomin da s**a shafi shirin tunkarar babban zaben 2023.

Jam'iyyun dai sun fara wani abu mai k**a da wasan `yar gala-gala ne tun lokacin da suke shirin gudanar da manyan tarukansu, na zabar shugabanninsu inda jam`iyya mai mulki ta yi ta sanya rana tana fasawa.

TALLA

A halin da ake ciki ma jam`iyyun biyu sai da s**a sassauya ranaku ko na wa`adin sayar da fom ga masu neman takara ko kuma uwa-uba, wato ranakun da za su gudanar da zabukan fid da gwani a wadansu matakai.

Zaɓen 2023: Jam'iyyun siyasar Najeriya sun ce sun kammala shiri
Dokar zaɓen Najeriya: Mece ce makomar ministocin Buhari da ke son tsayawa takara?
Zaɓen 2023: Ra'ayin 'yan APC ya bambanta kan ɓangaren da zai karɓi mulkin Najeriya
A kan maganar karba-karba ko shiyyar da za su kebe wa takarar shugaban kasa ma jam`iyyun sun yi ta yunkurawa kai ka ce gobe-gobe za su fadi matsayinsu amma shiru kake ji.

Irin wannan tafiyar kuran sai an yi gaba a koma baya, ko motsi da labewar da manyan jam`iyyun ke yi sun fara daure kan wasu `yan Najeriya.

To sai dai kuma masana siyasa, a nasu bangaren sun ce da sani jam`iyyun suke haka hasali ma dabarar yaki ce.

Dr Abubakar Kari, malami ne a jami`ar Abuja, ya shaida cewa, wadannan jam'iyyu k**ar suna fagen fama ne, kuma shi yaki yana bukatar shiri a don haka su wadannan jam'iyyu suna wadannan 'yan canje-canje ne domin su yi dai-dai da abubuwan da ke faruwa a cikin fagen siyasa.

Ya ce "abu na biyu kuma kowacce jam'iyya a cikin manyan guda biyu na la'akari da abubuwan da daya jam'iyyar ke yi domin ganin kodai ba a bar ta a baya ba, ko kuma ta samu galaba tun ma tafiya ba ta yi nisa ba."

Dr Abubakar Kari ya ce a yanzu duk wani taku da daya jam'iyya ta yi to zai iya yin tasirin a kan dayar.

Tuni dai jam`iyyar APC ta ce ba ta kwanto ko likimo da nufin kwashe wa wata kafa.

Ita ma jam`iyyar PDP ta ce ba ta shakkar kowa don haka a je a kara kawai.

Duk noke-noken da ake ganin k**ar manyan jam`iyyun na yi ta hanyar jinkirta daukar mataki ko sassauya ranakun gudanar da zabukan fid da gwanin dai, za a iya cewa yana da iyaka.

Tun da hukumar zabe ta gicciya sharadi da kuma wa`adin 3 ga watan Yuni, da kowacce jam`iyya za ta mika wa hukumar sunayen masu yi mata takara.

An yi jana'izar mutum 15 da kwalekwalensu ya nutse a Katsina. Hadarin ya faru ne a garin Tsabu cikin karamar hukumar Mai...
06/05/2022

An yi jana'izar mutum 15 da kwalekwalensu ya nutse a Katsina.

Hadarin ya faru ne a garin Tsabu cikin karamar hukumar Mai’adua inda jirgin ruwan ya kife da mutum ashirin akasari kananan yara mata a kan hanyarsu ta komawa gida daga yawon sallah ranar Laraba da daddare.

📷 Saddam Umar

Shugaba Buhari ya yi buda baki da shugabannin APC a fadarsa da ke Abuja yau Talata. Fadar Shugaban Najeriya
27/04/2022

Shugaba Buhari ya yi buda baki da shugabannin APC a fadarsa da ke Abuja yau Talata.

Fadar Shugaban Najeriya

Gwamnatin Najeriya ta ce ƴan bindiga masu satar mutane na ƙawance da Boko HaramYan bindigaGwamnatin Najeriya ta ce akwai...
14/04/2022

Gwamnatin Najeriya ta ce ƴan bindiga masu satar mutane na ƙawance da Boko Haram
Yan bindiga

Gwamnatin Najeriya ta ce akwai ƙawance tsakanin ƴan bindiga masu satar mutane a yankin arewa maso yammaci da kuma mayaƙan Boko Haram.

Ministan watsa labarai Lai Mohammed ne ya bayyana haka bayan taron majalisar zartarwa da shugaba Buhari ya jagoranta a fadarsa a Abuja.

Ya ce abin da ke faruwa a yanzu akwai ƙawance tsakanin ƴan bindiga da Boko Haram, bayan an tambaye shi ya faɗi waɗanda s**a kai hari a jihar Filato.

Ya ƙara da cewa binciken farko kan harin jirgin ƙasa da aka kai a Kaduna yna nuna “akwai alaƙa tsakanin ƴan bindiga da mayaƙan Boko Haram da ke yankin arewa maso gabashi.

14/04/2022

Fiye da mutum 50 da aka kashe a harin Filato na kusa da ni ne - Dan Majalisa
Yusuf Babayo Gagdi
dan Majalisar Tarayya mai wakiltar mazabar Pankshin/Kanam/KankeImage caption:

Yusuf Adamu Gagdi, dan Majalisar Tarayya mai wakiltar mazabar Pankshin/Kanam/Kanke
Dan Majalisar Tarayya da ke wakiltar mazabar Pankshin-Kanke-Kanam, Yusuf Adamu Gagdi, wanda al’umarsa ne wannan lamari ya shafa, ya ce kawo yanzu an tantance mutane fiye da dubu hudu da s**a tsere wa tashin hankalin.

Ya kuma ce kawo yanzu ya tabbatar da mutuwar mutane fiye da cas’in:

"Mutum fiye da 50 cikin wadanda aka kashe a hare-haren ‘yan-bindiga a Kanam ta jihar Filato, na sansu kuma sun san ni."

Dan Majalisar Tarayyar ya kuma ce wasu fiye da mutum 4,000 sun tsere daga gidajensu sak**akon hare-haren na ranar Lahadi.

Ana taron Majalisar Magabata a Fadar Shugaban Najeriya ta A*o RockMajalisar magabata ta kasa na gudanar da taronta a Fad...
14/04/2022

Ana taron Majalisar Magabata a Fadar Shugaban Najeriya ta A*o Rock
Majalisar magabata ta kasa na gudanar da taronta a Fadar A*o Rock ta shugaban Najeriya da ke Abuja babban birnin Najeriya.

Shugaba Muhammadu Buhari ne ke jagorantar taron majalisar wato (Council of State) a ranar Alhamis.

Yan bindiga sun sace ɗalibai mata a kwalejin Jihar Zamfara'Yan bindigaAFPCopyright: AFP'Yan bindiga sun sace ɗalibai mat...
13/04/2022

Yan bindiga sun sace ɗalibai mata a kwalejin Jihar Zamfara
'Yan bindiga
AFPCopyright: AFP
'Yan bindiga sun sace ɗalibai mata huɗu a Kwalejin Kimiyyar Kiwon Lafiya ranar Talata da dare a Jihar Zamfara da ke arewacin Najeriya.

Wani mazaunin yankin ya faɗa wa BBC cewa maharan sun afka wa gidan da ɗaliban ke zaune wanda ke wajen makarantar a garin Tsafe bayan sun tarar da jami'an tsaro na gadin kwalejin.

Rundunar ‘yan sanda a jihar ta ce jami’an tsaro sun duƙufa domin ganin an ceto ɗaliban da aka sace a gidan da s**a k**a haya suna kwana a cikin garin na Tsafe.

Shugagan Kwalejin Yusuf Idris Maradun ya ce ɗalibai biyar 'yan bindigar s**a k**a amma daga baya s**a saki ɗaya daga cikinsu saboda ta kasa tafiya sak**akon lalurar ƙafa.

Latsa hoton ƙasa ku saurari hira da shugaban kwalejin:

Buhari ya amince da kafa sabuwar kwalejin fasaha a KanoA Najeriya, Shugaba Muhammadu Buhari ya sanya hannu kan dokar kaf...
13/04/2022

Buhari ya amince da kafa sabuwar kwalejin fasaha a Kano
A Najeriya, Shugaba Muhammadu Buhari ya sanya hannu kan dokar kafa sabuwar kwalejin fasaha ta Tarayya a garin Kabo da ke Jihar Kano.

Cikin wata sanarwa da Ma'aikatar Ilimi ta Najeriya ta fitar ranar Talata, za a kafa wasu kwalejojin a JIhar Delta da Abiya da ke kudancin ƙasar.

Kano na da jami'o'i da manyan makarantu na gwamnatin Tarayya da gwamnatin jiha, abin da ya sa wasu ke cewa ba a bukatar karin wasu.

Yanzu haka malaman jami'a a ƙasar na yajin aiki sak**akon rashin mutunta yarjejeniyar da gwamnatin Najeriya ta ƙulla da malaman gamed da kuɗaɗen tafiyar da jami'o'in da kuma albashinsu.

Sai dai Sanata Barau Jibrin, wanda ya gabatar da ƙudirin kafa kwalejin fasahar ya shaida wa BBC cewa akwai bukatar kwalejin.

Ya ƙara da cewa nan da watan Oktoba mai zuwa za a fara karatu a cikinta.

Latsa hoton ƙasa ku saurari hira da Sanata Barau Jibrin:

Sojojin Najeriya sun ce sun kashe wani babban kwamandan IswapSojojin Najeriya sun ce sun kashe ɗaya cikin manyan kwamand...
09/04/2022

Sojojin Najeriya sun ce sun kashe wani babban kwamandan Iswap

Sojojin Najeriya sun ce sun kashe ɗaya cikin manyan kwamandojin Iswap da wasu mayaƙa a wani farmaki a arewa maso gabashi.

Sojojin sun ce sun kashe kwamandan mai suna Abubakar Danbuduma da mayaƙa 19.

Rundunar sojin ta ce dakarunta sun kai harin ne a yankin Tafkin Chadi ta hanyar amfani da jiragen yaƙi.

Abu ne mai wahala a iya tantance gaskiyar labarin. Amma wannan na zuwa a yayin da mayaƙan Iswap ke karɓe ikon wasu ƙauyuka tana tilasta wa mutane biyan haraji

Gwamnatin Najeriya ta fadi dalilin da ya sa aka shiga matsalar lantarki a ƙasaGwamnatin Najeriya ta ce an samu matsala n...
09/04/2022

Gwamnatin Najeriya ta fadi dalilin da ya sa aka shiga matsalar lantarki a ƙasa
Gwamnatin Najeriya ta ce an samu matsala ne a babban layin samar da lantarki na ƙasa.

Wata sanarwar daga ofishin ministan lantarki na Najeriya Injiniya Abubakar Aliyu ta ce ana gudanar da bincike domin gaggauta magance matslar.

An fuskanci katsewar lantarki a sassan Najeriya a ranar Juma'a.

Sanarwar ta ce: "muna sanar da al'umma cewa matsalar ta faru ne karfe 18:30 a ranar 8 ga Afrilu, wanda ya haifar da matsalar lantarki a sassa da dama na ƙasa.

Jami’ar kimiyya da fasaha  ta kano dake garin Wudil ta tabbatar da bada goyan bayanta  wajen samun nasarar harkokin kara...
09/04/2022

Jami’ar kimiyya da fasaha ta kano dake garin Wudil ta tabbatar da bada goyan bayanta wajen samun nasarar harkokin karatu a jami’ar Al-Istiqama dake Karamar Hukumar Sumaila a Jihar Kano.

Shugaban Jam’iyyar Farfesa Shehu Alhaji Musa, ya bada tabbacin a yayin da tawagar shugabannin gudanarwar jami’ar ta Al-Istiqama , s**a kai ziyarar kulla alakar aiki zuwa jami’ar ta Wudil, karkashin jagorancin shugaban ta Farfesa Salisu Shehu.

Shehu Alhaji yace Jami’ar ta Wudil zata taimaka wajen horar da malamai, da musayarsu tsakanin Jami’ar tare da yin bincike a fannoni daban -daban.

Alhaji Musa, ya ce za kuma su taimaka wajen samarda sashin nazarin kimiyya da fasaha musamman a fannin noma.

Inda ya kara da cewa, samun karin jami’oi masu zaman kansu a Jihar Kano, zai taimaka wajen samar da cigaban ilimi a Jihar dama kasa baki daya.

Da yake jawabi shugaban Jami’ar ta Al-Istiqama Farfesa Salisu Shehu, ya bayyana cewa sun ziyarci jami’ar ne domin duba yadda zasu yi aiki tare, da hakan zai taimaka wajen kafuwar jami’ar.

Akarshe ya bayyana farincikinsa bisa tarbar da hukumar jami’ar ta Wudil ta yi musu da ya kwatanta a matsayin nasara.

Borno: Mahaifin Matar Gwamna Umaru Zulum ya riga mu gida gaskiya Asabar, Afirilu 09, 2022 at 5:08 Safiya by  Ahmad Yusuf...
09/04/2022

Borno: Mahaifin Matar Gwamna Umaru Zulum ya riga mu gida gaskiya Asabar,

Afirilu 09, 2022 at 5:08 Safiya by Ahmad Yusuf Borno - Matar gwamna Babagana Umaru Zulum na jihar Borno,

Dakta Falmata Umara Zulum, ta yi rashin mahaifinta, Alhaji Kauna Bulama Kyari.

ta fara wata gwagwarmayan taimakawa yara marasa galihu a Calabar - Kayi musharaka a wannan shirin na Patreon, mu hada kai wajen canza rayukan mutane! Ya rasu ne ya na da shekara 70 a duniya bayan ya sha fama da jinya, k**ar yadda jaridar Daily Trust ta rahoto. Borno: Mahaifin Matar Gwamna Umaru Zulum ya riga mu gida gaskiya Hoto: dailytrust.com Source: UGC Sakatariyar watsa labarai ta matar gwamnan, Hajiya Aisha Ngubdo, ita ce ta bayyana haka a wata sanarwa da ta fiyar jiya Jumu'a a Maiduguri, babban birnin jihar Borno. Misis Ngubdo ta bayyana mamacin da mutumin kirki, da kulawa wanda mutane za su yi rashinsa ba wai iyalansa kaɗai ba. A cewar Sakatariyar watsa labarai ta mace lamba ɗaya a Borno, Al'ummar jihar Borno sun yi babban rashi da zasu jima ba su mance da shi ba.

Buhari ya nemi majalisa ta amince da naira tiriliyan huɗu a matsayin kuɗin tallafin maiBuhariState HouseCopyright: State...
08/04/2022

Buhari ya nemi majalisa ta amince da naira tiriliyan huɗu a matsayin kuɗin tallafin mai
Buhari

State HouseCopyright: State House
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya nemi majalisar tarayyar ƙasar ta ƙara yawan kuɗin tallafin man fetur na kasafin kuɗin 2022 daga biliyan 442 zuwa tiriliyan huɗu.

Buhari ya buƙaci hakan ne cikin wata wasiƙa da ya rubuta wa 'yan majalisar, inda yake neman su yi wa dokar kasafin kuɗin gyara.

Cikin wasiƙar wadda Kakakin Majalisar Wakilai Femi Gbajamila ya karanta a zaman majalisa na ranar Alhamis, Buhari ya ambaci hauhawar farashin ɗanyen man fetur sak**akon yaƙi tsakanin Rasha da Ukraine.

"Kamar yadda kuka sani, an samu sauyi a tattalin arziƙin duniya da kuma na cikin gida wanda ya tilasta neman gyara kan Tafarkin Harkokin Kuɗi na 2022 wanda aka gina kasafin kuɗi na 2022 a kansa," a cewar Buhari.

A cewarsa, sauyin da za a samu a tafarkin ya haɗa da ƙari a kan hasashen farashin ɗanyen mai daga dala 62 zuwa 73 a kan kowace ganga da aka saka a kasafin kuɗin na 2022.

07/04/2022

Buhari ya gana da sabon shugaban jam'iyyar APC a Fadar A*o Rock

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya gana da shugaban jam'iyyar APC ta kasa, Sanata Abdullahi Adamu a Fadar A*o Rock da ke Abuja.

Tsohon shugaban riko na APC kuma gwamnan jihar Yobe Mai Mala Buni ya raka sabon shugaban.

Wannan ne karo na farko da Sanata Abdullahi Adamu ke kai ma Shugaba Buhari ziyara tun bayan da aka kammala babban taron jam'iyyar a Abuja.

Ganawar na da nasaba da shirye-shiryen da jam'iyyar ke yi na zabukan fitar da gwani domin tunkarar babban zabe na kasar da za a yi a shekara 2023.

DA ƊUMI-ƊUMI: KOTU TA RUSHE KWAMITIN RIƘON DA PDP TA KAFA A KANOBabbar Kotun Tarayya mai lamba 7 da ke birnin tarayya Ab...
07/04/2022

DA ƊUMI-ƊUMI: KOTU TA RUSHE KWAMITIN RIƘON DA PDP TA KAFA A KANO

Babbar Kotun Tarayya mai lamba 7 da ke birnin tarayya Abuja ta rushe Kwamitin riƙon da uwar jam’iyyar PDP ta kafa a Kano.

Lauyan jam’iyyar PDP ta Kano Barrister Ibrahim Isah Wangida ya yiwa Freedom Radio ƙarin bayani a kai.

Ya ce “Lauyan uwar jam’iyyar PDP ta ƙasa ya shaida wa Kotu cewa, ba su kafa kwamitin riƙon ƙwarya ba, sannan ba su aika wa INEC takarda kan hakan ba”.

“Saboda haka kotu ta ce idan ma sun kafa to ta yi watsi da shi, ta amince Shehu Wada Sagagi ya ci gaba da shugabancin jam’iyya” a cewar Wangida.

Sai dai a nasu martanin Kwamitin riƙon sun bayyana cewar umarnin da Kotu ta bayar ya zo ne bayan da aka riga aka naɗa su, ba kafin ba.

Sakataren Kwamitin Barrister Baba Aliyu ya shaida wa Freedom Radio matsayarsu a kai.

“Suna ta kwana-kwana sun kasa kawo mana odar, saboda kotun ma bata da hurumi, amma mun aika wakilanmu su je kotun domin su karɓo mana kwafin umarnin.

Ya ci gaba da cewa “Tun farko kotun ta bada wannan odar ne bayan an riga an kafa kwamitinmu, ta ce kar a yi, a daidai lokacin da an riga an yi, kuma duk wannan shure-shure da suke ba zai hana mutuwa ba”.

“Basu da buri sai su dagula mana jam’iyya, saboda haka muna sanar da masu kishin PDP cewa ba abin da zai faru, duk mai sha’awar takara ya je ya sayi fom” a cewar Barrister Baba Aliyu.

WAIWAYE:

Idan zaku iya tunawa Shugabancin jam’iyyar PDP ƙarƙashin jagorancin Alhaji Shehu Wada Sagagi su ne s**a shigar da ƙara gaban Kotun, suna neman ta dakatar da uwar jam’iyyar daga rushe su.

Hakan yazo a daidai lokacin da wani tsagin jam’iyyar a Kano s**a nemi uwar jam’iyyar ta ƙasa da ta sauya shugabancin.

Tsagin na zargin su Shehu Wada Sagagi da yiwa jam’iyyar zagon ƙasa, kasancewar su mabiya tsohon Gwamna Kwankwaso wanda ya tsallake ya fice daga PDP zuwa NNPP.

Sai dai Alhaji Shehu Wada Sagagi da tawagarsa sun sha musanta zargin suna masu cewa, basu da buri face ganin ci gaban jam’iyyar.

Da Dumi Dumi: Ministan Sharia a Najeriya Malami Ya Ajiye Mukaminsa Rahotonni sun bayyana cewa! Ministan Shari'a Abubakar...
07/04/2022

Da Dumi Dumi: Ministan Sharia a Najeriya Malami Ya Ajiye Mukaminsa

Rahotonni sun bayyana cewa! Ministan Shari'a Abubakar Malami, Ya Ajiye Mukaminshi Na Minista Domin Yin Takarar Gwamnan Jihar Kebbi A Zaben 2023

Wane Fata Zaku Mishi?

YANZU-YANZU: Osinabajo Ya Dira Garin Maiduguri, Jihar Borno 'Mataimakin shugaban kasar Najeriya, farfesa. Yemi osinbajo,...
07/04/2022

YANZU-YANZU: Osinabajo Ya Dira Garin Maiduguri, Jihar Borno

'Mataimakin shugaban kasar Najeriya, farfesa. Yemi osinbajo, ya dira garin maiduguri a domin bude wani katafaren dakin taro da attajirin Najeriya Alhaji Muhammad Indimi ya Gina a abban jami'ar ta Maiduguri"

Daga Barrista Nuraddeen Isma'eel

Address

Maiduguri
00234

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Borno news 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Borno news 24:

Share