Halarci Online Media

Halarci Online Media Wanna Shafi, Zai Ringa Kawo Muku Ingatatun Labarai Wadanda S**a Shafi Abubuwa Daban Daban Na Rayuwarmu Kamar; limi, Nishadi, Wasanni, Ban Al'ajabi Da Sauransu.

Barista Ali Sa'adu Birnin KuduLauya kuma ɗan siyasa, wanda aka fi sani da Barista Ali Sa’adu Birnin Kudu. Shi ne gwamnan...
17/07/2025

Barista Ali Sa'adu Birnin Kudu

Lauya kuma ɗan siyasa, wanda aka fi sani da Barista Ali Sa’adu Birnin Kudu. Shi ne gwamnan farko na farar hula a jahar Jigawa.

Haihuwa

An haife shi a garin Birnin Kudu wanda shi ne helikwatar mulkin ƙaramar hukumar Birnin Kudu a ranar 13 ga watan Fabarairu na shekarar 1959.

Karatu

Barista Ali Sa’adu Birinin Kudu, ya yi karatunsa na firamare a garin Birnin Kudu, daga nan kuma ya samu nasarar shiga makarantar sakandare ta Birnin Kudu (Birnin Kudu Secondary School) wacce ta koma Kwalejin Gwamnati ta Birnin Kudu (Government College Birnin Kudu). Daga nan kuma ya ɗora zuwa Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya inda ya yi karatun digiri a fannin doka (Bachelor Degree in Law), sannan bayan gamawarsa da shekara guda kuma ya samu tafiya makarantar aikin doka (Law School).

Fara shiga siyasa

Ya fara shiga harkar siyasa a shekarar 1983 a jamhuriya ta biyu. Ya samu tikitin tsayawa takarar majalisar wakilai a kan rusasshiyar jam'iyyar NPP a tsohuwar jihar Kano, amma bai ci zabe ba.

Ya yi takarar ne tare da marigayi tsohon gwamnan jihar Kano, Muhammadu Abubakar Rimi, wanda ke neman sake tsayawa takarar gwamna, bayan ya yi watsi da tsohuwar jam’iyyarsa ta asali ta Peoples Redemption Party (PRP), wadda marigayi Mallam Aminu Kano ya kafa da kuma tsohon gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, wanda shi ma ya tsaya takarar kujerar majalisar wakilai ta kasa.

Aikin Banki

Ali Sa'adu yayi aiki a First Bank daga 1984 zuwa 1991.

Zamowarsa Gwamna

Kafin zamowarsa gwamna ya yi aiki da ma’aikatar Shari’a ta tsohuwar jahar Kano a tarayyar Najeriya na tsawon shekaru uku inda ya daga baya ya shiga siyasa a shekarar 1991. Ya kafa tarihin zamowarsa gwamnan farar hula na farko a Jahar Jigawa. An zaɓe shi ya zama gwamnan Jahar Jigawa a watan Disamba na shekarar 1991 a ƙarƙashin tutar jama’iyyar SDP (Social Democratic Party). A lokacin yana da shekaru 33 da haihuwa, ya k**a aiki a watan Janairu na shekarar 1992. Ya bada gudunmawa sosai wajen gina wannan jaha ta Jigawa. Mulkinsa ya ƙare a watan Disamba na shekarar 1993.

An ce yana cikin gwamnonin kalilan da ke da kusanci da kujerar mulki a matakin kasa. Sak**akon haka an ce ya samu gata mai yawa daga A*o Rock idan aka kwatanta da yawancin abokan aikinsa na wasu jihohi.

Siyasar Ali Sa’adu Birni Kudu ta samu cikas bayan juyin mulkin da sojoji s**a yi ba tare da zubar da jini ba wanda marigayi Janar Sani Abacha ya jagoranta. Bayan juyin mulkin, an haramta ayyukan siyasa a kasar.

Bayan ya bar mulki a matsayin gwamnan farar hula na farko a jihar Jigawa, Kudu ya fice daga harkokin siyasa a jihar har zuwa wani lokaci a shekarar 2003 inda ya sake gudanar da yakin neman zaben kujerar gwamna a karkashin inuwar jam’iyyar NDP. Ya fafata da gwamnan jihar mai ci a lokacin, Saminu Turaki; amma ya fadi.

Bayan ya sha kaye a zaben 2003, tsohon gwamnan ya sake ficewa daga fagen siyasar jihar har zuwa shekarar 2007 inda ya ya koma jam'iyyar PDP.

Rubutawa Muhammad Cisse

Tarihin Sahabbai Al-Habab Bn Al-Mundhir (RA)Al-Habab b. al-Mundhir (Da Larabci: الحباب بن المنذر ) ya na daga cikin saha...
15/07/2025

Tarihin Sahabbai

Al-Habab Bn Al-Mundhir (RA)

Al-Habab b. al-Mundhir (Da Larabci: الحباب بن المنذر ) ya na daga cikin sahabban manzon Allah (SAWW), kuma daya daga cikin Ansar. Ya kasance tare da Manzon Allah (SAWW) a mafi yawan yakokinsa. An san shi da suna "Dhul-Ra'y" (Mai ra'ayi), saboda shawarwari da nasihohi masu kyau da yake bai wa mutane.

An ce ya kasance jajirtacce kuma masanin balaga. Al-Habab ibn Al-Mundhir ya rasu a zamanin khalifancin Sayyidina Umar (RA), ya na da shekaru sama da hamsin.

Al-Habab ibn Al-Mundhir bn al-Jumuh al-Ansari, mahaifiyarsa ita ce "Shumus bt. Haqq b. Ummih b. Haram. Lafazin nasa shi ne "Abu Umar" ko "Abu Amr". Ya haifi 'ya'ya maza biyu, "Khashram" da "al-Mundhir", da 'ya mace mai suna "Umm Jamil".

Al-Habab ya halarci mafi yawan yakokin Manzon Allah (SAWW).

Yakin Badar: Ya halarci yakin Badar, kuma a lokacin da musulmi su ka yanke shawarar kafa sansaninsu, sai ya ba da shawarar a yi zango a kusa da rijiyoyin Badar. A lokacin ya na da shekara talatin da uku, amma shawararsa ta samu karbuwa har ma Allah ya tabbatar da hakan. A wannan yakin Al-Habab shi ne mai rike da tutar Khazraj .

Yakin Uhud: A yakin Uhud Manzon Allah (SAWW) ya umurci Al-Habab da su tattara bayanai daga sansanin makiya. Lokacin da ya cika aikinsa, Manzon Allah (SAWW) ya ba shi tutar Khazraj. A wannan yakin, ya na daya daga cikin mutane goma sha biyar da s**a rage tare da Manzon Allah (SAWW) da ba su gudu ba.

Ya kuma kasance daya daga cikin mutane takwas da s**a sha alwashin kare Manzon Allah (SAWW) har sai sun mutu.

Yakin Hamra'ul-Asad: Lokacin da Annabi (SAWW) ya umurci mutane da su tafi wani yaki bayan yakin Uhudu, Al-Habab ya yi biyayya ga Manzon Allah (SAWW).

Yakin Banu Nadir da Banu Qurayza: Lokacin da Manzon Allah (SAWW) ya yanke shawarar tafiya yaki da Banu Al-Nadir, Al-Habab ya ba da shawarar cewa sojojin su zauna a tsakanin kagaran Banu al-Nadir don yanke hanyoyin sadarwa a tsakaninsu, kuma Annabi (SAWW) ya karbi shawararsa.

Har ila yau Al-Habab ya halarci yakin Banu Qurayza, kuma a wannan yakin ma ya ba wa Manzon Allah (SAWW) Shawarar soji.

Yakin Khaibar: A yakin Khaibar, Manzon Allah (SAWW) ya ba Ali bn Abi Talib (AS) tutarsa, Al-Habab bn Al-Mundhir a wannan yakin ma ya ba da wata shawara ga me da tura sojoji kuma Manzon Allah (SAWW) ya karbi shawararsa. Shi ne kuma mai rike da tutar Khazraj.

Yakin Ta'if: A wannan yakin Al-Habab ya je wurin Manzon Allah (SAWW) ya ba da wasu shawarwari game da kai farmaki kuma Manzon Allah (SAWW) ya karbi shawararsa.

Sauran Yakukuwa: Al-Habab ya halarci yakin Khandaq, Banu l-Mustalaq, Hudaibiyya, Hunain, da Tabuka, kuma ya kasance mai rike da tutar Khazraj a wasunsu.

Lokacin Annabi (SAWW) ya tura Ali ibn Abi Talib (AS) da ruguza wani gunki na kabilar Tayy, Al-Habab ibn Al-Mundhir yana cikin wadanda su ka taya shi.

Rubutawa Muhammad Cisse

Tarihin Kabilar Da Ta Fi Ban-Tsoro A Duniya Kabilar North Sentinel Dake Rayuwa A Kan Tsibiri.mutanen kabilar North senti...
15/07/2025

Tarihin Kabilar Da Ta Fi Ban-Tsoro A Duniya Kabilar North Sentinel Dake Rayuwa A Kan Tsibiri.

mutanen kabilar North sentinel Island. Kabilar da tafi kowacce ban tsoro da kuma kebewa daga cikin al’umma.

A zanen taswira, North sentinel Island yana yanayi ne da sauran gurare na indian Ocean wanda yake kewaye da kwawar teku masu daukar hankali. North Sentinel Island yana nan ne a bakin tekun Bengal dake Andaman archipelago.

Shi dai North Sentinel Island ba k**ar sauran gurare na bakin ruwa bane da aka sani domin kuwa a kan kwatanta ko misalta shi da waje mafi wahala mafi muni sannan kuma wajen da ya fi ko wane waje tsoro yayin ziyara, sannan kuma guda ne ga mutanen da s**a fi kowannen mutane kadaita ko kuma ware kansu daga sauran mutanen duniya.

Wannan abu na abin mamaki da ake dangata wadannan mutane da shi ba zai iya misaltuwa ko aunawa a ma’auni ba kai tsaye, amma mafi yawan gaskiyar ita ce, a kiyasi na k**ar shekara 60,000 North Sentinel Island ya kasance gida ne ga kabila masu cin gashin kansu kuma suke ki' suna hana sauran mutanen duniya kusantar su karfi da yaji.

Idan aka hango North Sentinel Island daga sama k**ar yadda tauraron dan’Adam na European Space Agency ta labarta.

Kabilar “Sentineli” sun kai hari ga kusan duk wani mahaluki da ya shiga yankinsu. a shekarar 1896 sun soki wani dan Indiya wanda ya gudo daga birninsu har ya kasance cewa ruwa ya kawo shi zuwa bakin gabar ruwan da suke har lahira, a shekara ta 1974, sun yi wa wadansu ‘yan daukar fim ruwan masu, (kwari da baka) shekara ta 2004 kuwa daya daga cikin mutanen kabilar ne ya saita sannan ya harbo wani jirgin sama mai saukar ungulu wanda yake shawagi a sararin Subhaana sak**akon tura shi da aka yi ya duba ko akwai wadanda suke a raye har zuwa lokacin' bayan an sami yanayi na girgizar kasa, a baya bayannan ma a shekarar 2006 mutanen sun kashe wasu masu ‘su’( masu kamun kifi) wadanda s**a fada kogin yankinsu bisa kuskure

Tsuguno dai bata kare ba, domin kuwa bayan an tura jirgin sama mai saukar ungulu akan ya je ya taho da gawarwakin wadanda s**a kashe din kuwa, mutanen sun sake kai hari ne wa shi kansa jirgin.

Wannan muguwar dabi’a ta mutanen North Sentinel Island ne ya sanya aka kasa sanin wani abu mai yawa game da wannan kabila, abin da aka sani kawai shi ne suna da mak**ai musamman irin danginsu kwari da baka, sannan kuma suna amfani da raga irin ta kamun kifi, suna amfani da kwale-kwale, su kan yi kamun kifi, su shiga daji domin samun ganyayyaki na daji, amma babu wani labari na noma ko kiwo ko kuma wani abu da ya danganta su da kunna wuta ko da kuwa irin ta ita ce ce, mutane su kan yada jita- jitar cewa mutanen Sentinel su kan jira ne har sai an yi tsawa sannan kafin ta hura musu wuta a jikin gunguma-gunguman itatuwan da s**a hada wanda za su yi ta amfani da shi har na tsawon wani lokaci.

Sanannen abu ne cewar kabilar sentinel su ne mutane na karshe dake rayuwa a duniyar nan wanda ya kasance cewar ba wanda yake taba su ko kuma zuwa kusa da su da abin da ya danganci zamani.

mutane sun yi kokarin bincike akan kabilar sentinel inda wasu s**a yi nasarar samun wadansu bayanai kalilan.

A shekarar 1771 wani mai binciken yanayi na kasar Birtaniya mai suna John Ritchie ya wuce ta wannan waje, ya ce daga bangaren Kudu maso Yammacin Andaman akwai gabar wani kogi mai kyau wanda yake rufe da bishiyoyi yana da girma da tsawo sannan kuma idan za mu yanke hukunci daga yawan hàske da ake iya hanga daga wajen za mu iya cewa wuri ne da ya dace da rayuwa, 'jirgin na ruwa ya yi ta shawagi har tsawon wasu shekaru yana kewayawa yana komawa har na tsawon shekara 100, amma ba’a sami wani abu na dorar wa game da mutanen ba.

A shekarar 1869 jeremiah Homfray, mutumin da ke da alhakin kula da Andamanese ya yi tafiya zuwa Sentinel Island domin binciko wadansu masu laifi wadanda s**a kubuta daga penal Colony a Port Blair.

Da fara isarsu, Homray wanda yake tafe da rakiyar ‘yan sanda da da kuma wadansu daga cikin Andamanese s**a hango wadansu mutane su goma zaune a bakin tekun ‘tsirara ’suna da dogon gashi rike da ‘kwari da baka’ suna harbin kifi.

Daga nan dai mutanen na Sentinel s**a nemi waje s**a boye bayan sun hango wannan jirgi na su Homray. Mutanen na Andamanese da s**a kasance cikin firgici tsoro da kuma faduwar gaba yayin da s**a hango abin da ke faruwa, sun gargadi Homfray da kakkausar muraya a kan hatsarin da ke tattare da wadannan mutane, amma sai ya yi bitis da gargadin na su ya kuma sanya wa ransa cewar ya isa wannan waje inda kuma hari ne ya biyo baya daga wadannan mutane.

A wannan shekarar kuma wata tawaga ta ‘yan kasuwa daga indiya sun fado wannan waje sak**akon jirginsu na kasuwanci da ya farfashe a cikin kogi har ya wanko su zuwa North Sentinel bayani ya nuna cewa mutane 86 daga cikin wadanda s**a rayu cikin fasinjan jirgin da kuma mutum 20 daga cikin masu kula da jirgin sun sauka lafiya a bakin tekun.

A kwana na uku da saukarsu ne kuwa ‘yan kabilar Sentinel s**a kawo masu hari. Kyaftin din jirgin ya ce: mutanen suna zamane a tube ma’ana tsirara, suna da guntun gashi da kuma hanci ja, sannan suna bude bakunansu domin fitar da wata irin kara k**ar na namun daji, suna amfani da baka wanda s**an yi tsinin bakinsa da karfe, kyaftin din ya ce ya kubuta ne daga hari wadan nan mutane ta kan burbushi jirgin yayin da kuma aka kawo masa agaji kwanaki da dama bayan ya kubuta ta hanyar wasu matafiya da hanya ta wuto da su ta wajejen inda daga baya kuma aka tura jirgin ruwa irin na yaki domin ceton sauran wadanda s**a rayu wanda s**a samu s**a gudu daga tekun Sentinel da taimakon duwatsu da itatuwa.

Bayan wannan ruguntsimi kuwa, an share sama da shekaru goma 13 ba tare da wani ya sake waiwayar wadannan mutanen ba.

A Janairu na shekarar 1880 ne kuma wasu mayakan Britaniya s**a sami nasarar sauka a tsibirin na North Sentinel, mayakan, karkashin jagorancin Maurice Bidal Portman dan shekaru 20 sun shiga tsibitin neman wadan nan kabila inda s**a s**a ci karo da hanyoyi ma banbanta da kuma sababbin kauyuka wadanda aka yi watsi da su.

Portman ya ce yanayin girki da sarrafa abinci na mutanen Sentinel ya yi k**a da na mutanen Onges, ba irin na aborigin da mutanen Andaman ba. A lokacin wannan zagaye Portman ya ce bai gamu da ko mutum kwaya daya ba na daga wannan kabila duk sun watse cikin daji.

Cikin sa’a ne bayan wasu kwanaki masu dama ana bincike sai kuwa s**a ci karo da mutum shida daga cikin Kabilar Sentinel wadanda s**a kunshi mata da miji dattijai da s**a manyanta sai kuma ‘ya’yansu guda hudu inda s**a k**a su, s**a tattarasu s**a mai da su Port Blair.

Daga Muhammad Cisse

Mihailo Tolotos Mutumin Da Ya Rayu Shekaru 82 Bai Taba Ganin Mace BaMihailo Tolotos, an haife shi a shekara ta 1856, ya ...
15/07/2025

Mihailo Tolotos Mutumin Da Ya Rayu Shekaru 82 Bai Taba Ganin Mace Ba

Mihailo Tolotos, an haife shi a shekara ta 1856, ya yi rayuwa mai ban mamaki ta keɓabban Dutsen Athos, gidan waliyai na Girka da aka haramta zuwan mata. Waliyai sun rene bayan ya zama maraya, abin mamaki bai taba ganin mace ba a cikin shekaru 82 da ya yi ya na raye.

Labarin Mihailo Tolotos, wani ɗan ƙasar Girka wanda rayuwarsa ta kasance ɗaya daga cikin mutanen da ke a keɓe da duniya ta taɓa sani.

An haife shi a shekara ta 1856 a Halkidiki cikin kasar Girka (Greece), Tolotos ya rasa mahaifiyarsa 'yan sa'o'i kadan bayan ta haife shi. Waliyai yan darikar Orthodox (Ta Kiristanci) sun ɗauke shi, s**a kai shi gidan waliyai na Dutsen Athos, ɗaya daga cikin wuraren da aka keɓe, kuma daya daga cikin tsarkakakkun wuraren addini a duniya. Amma akwai wata doka da ba za a iya karya ta ba: babu macen da aka yarda ta shiga wajen, an kafa dokar hana mata shiga wurin tun karni na 10 kuma dokar tana nan har zuwa yau.

Dutsen Athos: Wurin da ko dabbobi mata ba a yarda su shiga ba

Dutsen Athos ba wurin bauta ba ne kawai. Gida ga kusan waliyai 2,000. Gidan yanzu yana karkashin hukumar kula da kayan tarihi da al'adu ta Majalisar Dinkin Duniya (UNESCO), kuma har yau yana aiki a ƙarƙashin tsoffin al'adunsa. Ba wai kawai an hana mata shiga ba, hatta dabbobi mata k**ar shanu da tumaki an hana su shiga. Manufar ita ce a taimaki waliyai wajen kulawa da zaman gwauranci (rashin yin aure) da mai da hankali wajen ibada. Kuma Mihailo Tolotos ya ɗauki wannan matsananciyar rayuwar mara misaltuwa.

Bai taɓa barin Dutsen Athos ba, bai taɓa shiga garuruwan da ke kusa ba, kuma bai taɓa sa idonsa a kan mace ba. Ilimin da ya sani kawai game da jinsin mata ya fito ne daga littattafai.

Ba mace kadai ba, bai taba ganin mota, jirgin sama ko kallon fim ba

Rayuwar Tolotos ba kawai rashin ganin mata ba ce. A cewar wani labarin da mujallar Edinburgh Daily Courier ta buga a 1938, ta ce bai taba ganin mota, jirgin sama, ko fim ba.

Yadda aka binne shi bayan ya mutu

Lokacin da ya rasu a shekara ta 1938, waliyai na Dutsen Athos sun yi masa jana'iza ta musamman don girmama shi. Sun yi imani cewa watakila shi kaɗai ne namiji a tarihi da ya rayu kuma ya mutu ba tare da ya ga mace ba, furucin da har yanzu yana ɗaukar tunanin mutane da yawa.

Zuwa Yau

Har zuwa yau, mata basa shiga Dutsen Athos, duk da karuwar muhawara tsakanin kasa da kasa na nuna wariya. Duk da haka dutsen ya kasance wuri mai tsarki ga waɗanda s**a zaɓi rayuwar zuhudu (gudun duniya), k**ar yadda Tolotos ya yi sama da shekaru ɗari da s**a wuce.

Source: Time Entertainment
Fassarar Muhammad Cisse

Buhari da matarsa ​​ta farko Safinatu da 'ya'yansaHoton a lokacin ya na tare da marigayiyar matarsa ​​Safinatu da Yayans...
15/07/2025

Buhari da matarsa ​​ta farko Safinatu da 'ya'yansa

Hoton a lokacin ya na tare da marigayiyar matarsa ​​Safinatu da Yayansu; Fatima, Hadiza da Zulaihat a gidan gwamnati, a Dodan Barrack legas.

Tsohon shugaban kasa marigayi Muhammadu Buhari yayi Aure kafin matarsa ​​ta yanzu Aisha Buhari. Buhari tun yana matashin soja ya auri Safinatu a watan Disamba 1971, jim kadan bayan kammala karatunta na jami’a, kuma sun haifi ‘ya’ya biyar tare, Fatima, Hadiza, Zulaihat, Safinatu da kuma marigayi Musa.

An ce Buhari ya san Safinatu tun ta na da shekara 14 kafin aurensu. Matar Buhari ta farko Safinatu ta kasance uwargidan shugaban kasar Najeriya a lokacin da yake shugaban kasa.

An haifi Safinatu Buhari a garin Jos na Jihar Filato a ranar 11 ga Disamba, 1952, ya'ce ga Alhaji Yusufu Mani da Hajiya Hadizatu Mani wacce ta fito daga karamar hukumar Mani a jihar Katsina kuma ‘yar kabilar Fulani ce ta Arewacin Najeriya.

Lokacin da Musa 'Yar'Adua, kwamishinan al'amuran Legas a lokacin, ya nada mahaifinta a matsayin sakatare na musamman iyayenta sun koma jihar Legas.

Safinatu Buhari ta yi makarantar firamare da ke Tudun Wada, Jos. A shekarar 1971 ta yi karatu a Kwalejin horas da malamai ta mata ta Katsina inda ta samu shaidar kammala karatun digiri na biyu.

Ta yi karatun Islamiyya kuma tana iya rubutu da Ingilishi da Larabci. Lokacin da Safinatu Buhari ta na raye, ta kasance malamar makaranta.

Safinatu Buhari ta hadu da Muhammadu Buhari tana da shekaru 14, kuma sun yi aure tana da shekaru 18 a duniya a shekarar 1971.

Ya'yansu biyar ne Tare da Muhammad Buhari

Zulaihat Buhari, Fatima Buhari, Hadiza Buhari, Safinatu Lami Buhari, da marigayi Musa Buhari.

Safinatu Buhari ta koma Kaduna da ‘ya’yanta bayan da Ibrahim Babangida ya hambarar da gwamnatin Muhammadu Buhari.

A shekarar 1988, sun rabu da mijinta Nata

Mutuwa

Safinatu Buhari ta rasu ne a ranar 14 ga watan Junairu, 2006, tana da shekaru 53 a duniya, sak**akon kamuwa da ciwon suga. Ya Allah Ya Jikanta Tare Da Muhammadu Buhari AMEN 🙏.

Daga Muhammad Cisse

Alhaji Adamu Chanchangi (mai Cancangi Airlines)An san Alhaji Amadu chanchangi a matsayin babban mai taimakon jama'a wand...
14/07/2025

Alhaji Adamu Chanchangi (mai Cancangi Airlines)

An san Alhaji Amadu chanchangi a matsayin babban mai taimakon jama'a wanda ke sanya murmushi a fuskokin wadanda s**a ci karo da shi. Chanchangi wanda ya shahara wajen kafa kamfanin jirgin sama mai zaman kansa na biyu a Najeriya, wanda ya fito daga karamar hukumar Takum ta jihar Taraba.

Kafa Kamfanin Chanchangi Airlines

A ranar 5 ga Janairu, 1994, ɗan kasuwan ya kafa kamfanin jirgin sama na Chanchangi. Kamfanin yana da hedikwatarsa a Kaduna. Ya zuwa Maris 2007, kamfanin jirgin yana da ma'aikata 780. A 2009, yana da jiragen sama shida.

Haka kuma ya samu lambar yabo ta hukumar kula da filayen jiragen sama ta tarayyar Najeriya (FAAN) da kuma lambar yabo ta ‘Corporate Merit Award’ na ‘Best Domestic Airline of the Year’ na shekarar 1998, 1999 da 2000.

Duk da cewa, ya samu nasara sosai, kamfanin jirgin ya fuskanci matsaloli shekaru biyu a wa’adi na biyu na mulkin tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo.

A ranar 10 ga watan Disamba, 2005, gwamnatin Obasanjo ta dakatar da kamfanin saboda rashin tsaro da ayyukansa, amma a ranar 22 ga watan Disamba na wannan shekarar ne kamfanin ya koma aiki. Tsakanin 2005 zuwa 2010, kamfanin jirgin ya rubuta wasu abubuwan da s**a faru da s**a kasance masa kalubale.

A shekarar 2012, kamfanin jiragen saman Ethiopian Airlines ya shigar da karar Chanchangi, inda ya ce yana bin kamfanin bashin biliyoyin nairori domin kula da lafiyar jiragensa. Kamfanin jirgin na Chanchangi ya kasa fitowa ya kare kansa daga tuhumar da ake masa.

Ya zuwa shekarar 2012, lokacin da kamfanin jirgin ya dakatar da aiki, jiragensa biyu ne kawai su ka rage.

Kamfanin jiragen na Chanchangi ya gudanar da zirga-zirgar jiragen sama a ciki da wajen Najeriya. Wasu daga cikin abokan huddarsa su ne:

🔹️Majalisar Dinkin Duniya
🔸️Sojojin Najeriya
🔹️Kwamandan Sojoji & Staff College, Jaji
🔸️Makarantar horar da kwallon kafa ta Najeriya

Zargin Boko Haram

A shekarar 2011, wata mujalla ta zargi Chanchangi da daukar nauyin mayakan Boko Haram, amma ya musanta zargin, yana mai bayyana hakan a matsayin hasashe na wani mawallafin mujalla.

Ya ce ya fi shagaltuwa da harkokinsa na zirga-zirgar jiragen sama da ayyukan jin kai da ya ke yi domin bunkasa kasa.

Trevor Worthington, Manajan Darakta na Kamfanin Jirgin Sama na Chanchangi, ya kira taron manema labarai inda ya musanta zargin rahotannin.

Ya ce “A gaskiya, shugabanmu ba ya cikin masu daukar nauyin ayyukan kungiyar kuma ba ruwansa da su, Alhaji Ahmadu ya shagaltu da harkokinsa na sufurin jiragen sama da ayyukan jin kai a kokarinsa na bayar da gudunmawar ci gaban kasa.

“Sabanin akidar kungiyar, shugabanmu mai taimakawa ne wajen karatun boko da na addinin Islama, don haka ya gina makarantar sakandare ta Gummi inda ake baiwa dalibai marasa galihu, musulmi da wadanda ba musulmi ba” ilmi kyauta.

Rasuwa

Attajirin, wanda dan asalin Jihar Taraba ne, ya rasu ne a safiyar ranar Laraba 19 ga watan Afrilu a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja, yayin da ake kokarin kai shi wani asibiti da ke Abuja.

Rahotanni sun ce marigayin ya rasu ya bar mata biyu da 'ya'ya 33 cikinsu har da dan Majalisar Wakilai daga Jihar Kaduna Alhaji Rufa'i Chanchangi.

Ya Allah Ya Jikan Amadu chanchangi Da RahamarSa AMEN 🙏

Rubutawa Muhammad Cisse

Yau Shekaru 95 Da Fara Gasar Wasan Kwallon Kafa Ta Duniya (Fifa World Cup)Gasar cin kofin duniya ta FIFA ta 1930 ita ce ...
13/07/2025

Yau Shekaru 95 Da Fara Gasar Wasan Kwallon Kafa Ta Duniya (Fifa World Cup)

Gasar cin kofin duniya ta FIFA ta 1930 ita ce gasar cin kofin duniya ta FIFA ta farko, gasar cin kofin duniya na kungiyoyin kwallon kafa na maza na kasa. An yi shi a Uruguay daga 13 zuwa 30 ga Yuli 1930. Hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA ce ta zabi Uruguay a matsayin kasar da za ta karbi bakuncin gasar, a lokacin da kasar za ta yi bikin cika shekaru 100 na kundin tsarin mulkinta na farko, kuma kungiyar kwallon kafa ta Uruguay ta ci gaba da rike kambunta na kwallon kafa a gasar Olympics ta bazara ta 192. An buga dukkan wasannin a babban birnin Uruguay, Montevideo, mafi rinjaye a filin wasa na Estadio Centenario. Kuma kasar Uruguay mai karbar bakuncin wasance tayi nasarar daukan kofi.

Asalin Wasan Kwallon Kafa (Football)

An fara yin wasan kwallon kafa ne a nan kasar Sin. Muna iya samun asalin wasan nan a shekaru 2300 da s**a gabata a garin Linzi na lardin Shandong na kasar Sin, kuma tsohon shugaban kungiyar wasan kwallon kafa ta duniya Joseph S Blatter ya riga ya tabbatar da wannan labari.

Wasan kwallon kafa wani muhimmin wasan motsa jiki ne a duniyar yau, to amma yaushe kuma a ina ne aka fara yin wasan?

Bisa nazarin da masanan ilmin tarihi s**a yi, a ran 4 ga watan Faburairu na shekara ta 2004, kungiyar wasan kwallon kafa ta duniya ta shelanta cewa, 'wasan kwallon kafa ya samo asalinsa ne a kasar Sin (China) wato wasan da ake kira Cuju da aka yi a kasar Sin a da da da can shi ne asalin wasan kwallon kafa.' Bisa nazarin da aka yi, an tarar da cewa, tun bayan da wasan kwallon kafa ya fito a kasar Sin a shekaru 2300 da s**a wuce, sai ya yi ta bunkasa, har ma ya taba samun karbuwa a tsakanin masarauta. A wasu kayayyakin tarihin kasar Sin da aka samu, ana iya gano zane-zanen da aka samu, ana iya gano zane-zanen da aka yi a kansu dangane da wasan Cuju da Sinawa ke yi a da.

Wasan Kwallon Kafa Na Zamani

Amma an soma yin wasan kwallon kafa na zamani ne a jami'ar Cambridge ta kasar Birtaniya, amma ba a samu dokokin wasan ba sai dai har zuwa shekarar 1848. A shekarar 1863, an kafa kungiyar wasan kwallon kafa ta Ingila, kuma an daidaita dokokin wasan da su zama bai daya, daga baya kuma an yi ta bunkasa da kyautata dokokin. A shekarar 1872, an yi gasar wasan kwallon kafa a tsakanin kungiyar Ingila da ta Scotland, wannan ya zama gasa na farko da aka yi a hukunce a tsakanin kungiyoyi a tarihin wasan kwallon kafa. A shekara ta 1904, an kafa kungiyar wasan kwallon kafa ta duniya (FIFA), daga nan, wasan kwallon kafa sai kara bunkasuwa yake ta yi, har ma ya samu karbuwa a duk fadin duniya.

Kungiyar wasan kwallon kafa ta duniya, wato FIFA a takaice, an kafa ta ne a ran 21 ga watan Maris a shekara ta 1904 a birnin Paris na Faransa bisa shawarar da kasashen Belgium da Faransa da Denmark da Spain da Sweden da Holland da Switzerland s**a bayar, a halin yanzu dai, akwai mambobi 204 a cikin kungiyar. A karkashinta kuma, akwai kungiyoyi na shiyya shiyya guda shida, wato na Turai da Asiya da Afirka da Amurka ta arewa da tsakiya da kuma Caribbean da Amurka ta kudu da Oceania. Babban aikin kungiyar FIFA shi ne bunkasa wasan kwallon kafa da kara mu'amalar sada zumunta a tsakanin mambobin kungiyar da jami'anta da kuma 'yan wasa ta hanyar yin gasa iri iri. Bayan haka, ita kuma ta dukufa a kan aiwatar da tsarin dokokin MDD da hana nuna bambancin launin fata da na siyasa da kuma addini.

Gasar Cin Kofin Duniya

Gasar cin kofin duniya shi ne muhimmiyar hanyar da kungiyar FIFA ke bi wajen yin talla, kuma tana da masu kallonta da yawa. Kudin tikitoci da kudin da aka biya don nuna gasar ta telebijin da kudin tallafawa da kuma kudin ciniki sun samar wa FIFA babbar riba.

Muhimman gasa na kungiyar FIFA su ne gasar cin kofin duniya wadda a kan yi shekaru hudu hudu tun daga shekara ta 1930, sa'an nan kuma akwai gasar wasan kwallon kafa ta wasannin Olympic da gasar wasan kwallon kafa ta matasan duniya da gasar wasan kwallon kafa ta matan duniya da dai sauransu.

Babbar mujallar kungiyar FIFA ita ce 'labarun FIFA', wadda a kan buga a watanni daya daya.

Don neman tabbatar da ingancin aikin alkalan wasa a gun gasar duniya da ta shiyya shiyya, kungiyar FIFA ta kan kuma aiwatar da shiye-shiryen horar da alkalan wasan.

Rubutawa Muhammad Cisse

Marigayi Alhaji Adamu Dankabo Alhaji Muhammad Adamu Dankabo, an haife shi a garin Kabo a ranar 4 ga watan Afrilu a sheka...
12/07/2025

Marigayi Alhaji Adamu Dankabo

Alhaji Muhammad Adamu Dankabo, an haife shi a garin Kabo a ranar 4 ga watan Afrilu a shekara ta 1942.

Yayi karatun Alƙur'ani a garin Kabo. Sannan ya fara karatun firamare a cikin garin gwarzo, daga nan ya samu gurbin karatu a makarantar lardi dake garin Kano. Marigayi ya halarci makarantar horar da aiki jirgin sama ta FTC a Kaduna da ta kwaleji BOC da ke kasar Amurka. Ya samu shaidar difloma ta harkokin kasuwancin sufurin jiragen sama.

Ya sha gwagwarmaya da dama a fannin aiyuka, daga cikin gida zuwa ƙasashen ƙetare tun daga matsayin me kula da jirgi har ya zamo mai bada abinci a cikin jirgi, har ya kai ga matakin mallakar jirgin kansa da kamfanin sa na Kabo Air.

Jarman Kano Adamu Dankabo ya fito da sunan jihar Kano dama Najeriya baki ɗaya a harkar sufurin jirgin sama, saboda wannan hidima tare da gwagwarmaya wacce Dankabo ya yi, ya sanya marigayi martaba Sarkin Kano Ado Bayero ya naɗa shi sarautar Jarman Kano na farko a Kano.

Ya kuma ba shi hakimin sabuwar ƙaramar hukumar Kabo da aka kirkiro daga karamar hukumar Gwarzo wanna aiki yayi har Allah ya kari kwanansa a ranar 4 ga watan Afrilun shekarar 2002.

Marigayi Jarman Kano Alhaji Muhammad Adamu Dankabo ya rasu a ranar 4 ga watan Afrilun shekarar 2002 yana da shekara 60. Muhammad Adamu Dankabo ya rasu ya bar iyalansa da dama.

Kabo Air

Kabo Air ya kasance wani kamfanin jiragen sama na Najeriya wanda ke gudanar da zirga-zirgar jiragen sama, musamman ma a lokutan aikin hajji. Dokta Alhaji Muhammadu Adamu Dankabo ne ya kafa shi a watan Fabrairun shekarar 1980, ya fara aiki a watan Afrilun shekarar, kuma ya daina aiki a shekarar 2017 saboda rashin biyan haraji. Kabo Air yana da hedikwata a Kano da filin jirgin Mallam Aminu Kano.

Kamfanin Kabo Air ya shahara da rawar da ya taka wajen jigilar alhazan Najeriya zuwa kasar Saudiyya don gudanar da aikin hajji. Kabo Air ya yi amfani da jiragen sama iri-iri da s**a hada da samfurin Boeing 747s da Boeing 737s, kuma a baya yayi amfani da BAC 1-11.

Ayyukan Kabo Air sun dai na aiki sak**akon rashin biyan haraji wanda ya sa aka rufe kamfanin a shekarar 2017. Hukumar tattara kudaden shiga ta Najeriya ta rufe ofisoshin kamfanin a watan Maris din 2017.

Daga Muhammad Cisse

Tohfa!! Kai dai sarkin far!ya ne, Rarara ne sarkin waka na gaske! Wallahi ko kaso ko kaki, Rarara ya yi maka nisa sosai ...
06/07/2025

Tohfa!! Kai dai sarkin far!ya ne, Rarara ne sarkin waka na gaske! Wallahi ko kaso ko kaki, Rarara ya yi maka nisa sosai — cewar Rashida Maisa’a ga Naziru Sarkin Waka

Mi zaku ce ??

MUHAWARA: Tsakanin Rarara Da Naziru Sarkin Waƙa Waye Yafi Taimakawa Mabuƙata ?A kafta....
03/07/2025

MUHAWARA: Tsakanin Rarara Da Naziru Sarkin Waƙa Waye Yafi Taimakawa Mabuƙata ?

A kafta....

Farashin motar da Sarkin Waka ya siya sabuwa tana farawa ne daga miliyan 500 wato 500M zuwa miliyan 750, 750M.Tabbas wan...
03/07/2025

Farashin motar da Sarkin Waka ya siya sabuwa tana farawa ne daga miliyan 500 wato 500M zuwa miliyan 750, 750M.

Tabbas wannan motar zata siyi ta Rarara sau uku harda ƙari, domin motar Rarara $40,000 ce da wani abu kudin ta dai baifi 80m ba.

Inji Gwanin Mota

Takardar amincewa da Sallah tare da bisina Alhaji Aminu Dantata a makabartat Baiqi'u Garqad  da ke Madina wacce aka binn...
29/06/2025

Takardar amincewa da Sallah tare da bisina Alhaji Aminu Dantata a makabartat Baiqi'u Garqad da ke Madina wacce aka binne sahabban Manzon Allah s.a.w. sama da dubu Goma inji Malamin Tarihi.Ibnu Zubalah!

Address

Kano

Telephone

+2347044444645

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Halarci Online Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share