Gobenmu media

Gobenmu media im abbakar dan masani from borno state Kwaya Kusar

Idan wani ya tambayeku BASHIN kudi, idan da hali kabashi abunda zaka iya kyauta kawai! Misali, Mai neman 50k to idan da ...
22/09/2025

Idan wani ya tambayeku BASHIN kudi, idan da hali kabashi abunda zaka iya kyauta kawai!

Misali, Mai neman 50k to idan da Hali ka bashi 20k kyauta ko abunda ya sawwaka, ka bashi Hakuri.

Biyan Bashi a wannan zamanin sai mai matukar tsoron Allah!

Lokacin da ake neman bashi mutum zai zama abun tausayi, Anma wajen Biya kuma zai zamo Fada.

Ina da cases na Bashi Babu adadi. Daga karshe A kai sunanka wajen Malamai don A toshe bakinka wani Sa’ain Har sunan Loyoyi ma ana hadawa ! Don toshiyar baki!!!

Shawara Kyauta! A daina kai sunan lawyer wahen bokaye ko malamai!

Barr. Hamza Nuhu Dantani ✍️

Nan Fa Ba Kasuwar Kurmi Ba Ce Dake Kano, Ko Kuma Kasuwar Barci Dake Kaduna, Wata Kasuwa Ce Ta 'Yan Arewa A Saudiyya .***...
21/09/2025

Nan Fa Ba Kasuwar Kurmi Ba Ce Dake Kano, Ko Kuma Kasuwar Barci Dake Kaduna, Wata Kasuwa Ce Ta 'Yan Arewa A Saudiyya

.
************* SASHEN TALLA**********************

Kuyi Download din Application din ABBA PANTAMI DATA ta wannan link din a PlayStore da kuma AppStore
👇👇
Ga link din PlayStore
https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.com.abbapantamidata.app

Ga link din AppStore
https://apps.apple.com/us/app/abba-pantami-data-ltd/id6744061271

Mai bukatan karin bayani, ya tuntubi daya daga cikin customer care ta WhatsApp;
09138275183
08126081967
07046868000
07061347599.

Shettima ya tafi New York domin halartar taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 80Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shetti...
21/09/2025

Shettima ya tafi New York domin halartar taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 80

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya bar Abuja zuwa birnin New York a Amurka domin halartar babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 80 (UNGA). Taron zai gudana daga Litinin 22 ga Satumba zuwa Lahadi 28 ga Satumba. Shettima na wakiltar Shugaba Bola Tinubu a taron, inda zai gabatar da jawabin ƙasa na Najeriya tare da halartar tattaunawar shugabanni da wasu muhimman taruka a gefen babban taron.

A cewar mai taimaka wa mataimakin shugaban ƙasa kan yaɗa labarai, Stanley Nkwocha, Shettima zai sanar da sabbin manufofin Najeriya (NDCs) ƙarƙashin yarjejeniyar Paris a taro na musamman kan sauyin yanayi. Haka kuma zai shiga wasu taruka da aka tanada na musamman a gefen babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya.

WATA SABUWA: Jagoran ƴan Shi'a a Najeriya Sheikh Zakzaky ya jagoranci ɗaura auren Musawi Hayatuddeen tare da matarsa Zak...
20/09/2025

WATA SABUWA: Jagoran ƴan Shi'a a Najeriya Sheikh Zakzaky ya jagoranci ɗaura auren Musawi Hayatuddeen tare da matarsa Zakiyya Abubakar akan sadaki Naira Million 26, ango ya biya lakadan.

An ɗaura auren yau Asabar a gidansa dake babban birnin Tarayyar Najeriya, Abuja.

Me Zaku Ce?

One News Hausa
2 0 — 0 9 — 2 0 2 5

20/09/2025

YEIDEP 🔥🔥🔥🔥
If your hope is on yeidep, kindly be hopeless.
Don't say we didn't inform you.

Barcelona na zawarcin Harry Kane, Manchester United na son Elliot Anderson, Real Madrid na zawarcin Ryan Gravenberch na ...
20/09/2025

Barcelona na zawarcin Harry Kane, Manchester United na son Elliot Anderson, Real Madrid na zawarcin Ryan Gravenberch na Liverpool.

Tinubu ya ziyarci iyalan marigayi Buhari a KadunaDan masani
19/09/2025

Tinubu ya ziyarci iyalan marigayi Buhari a Kaduna

Dan masani

Jiragen yaki na Rundunar Sojin Sama na Masarautar Saudiyya,  sun yi jerin gwano don raka jirgin da ke ɗauke da Firaminis...
18/09/2025

Jiragen yaki na Rundunar Sojin Sama na Masarautar Saudiyya, sun yi jerin gwano don raka jirgin da ke ɗauke da Firaministan Pakistan, Shehbaz Sharif, tun daga shigarsa cikin sararin samaniyar Saudiyya har zuwa lokacin da ya sauka a Filin Jirgin Sama na Ƙasa na Sarki Khalid da ke birnin Riyadh.

HOTO📸 ATP Hausa

Kuskuren Da Wasu Iyaye Mata Keyi Akan Tarbiyyar 'Ya'yansu‎‎Uwa itace makaranta ta farko a rayuwar yaron, kasancewar iyay...
18/09/2025

Kuskuren Da Wasu Iyaye Mata Keyi Akan Tarbiyyar 'Ya'yansu

‎Uwa itace makaranta ta farko a rayuwar yaron, kasancewar iyaye Maza basu cika zama gida ba sai zamana tarbiyar yaya iyaye mata ke kula dashi. Wasu daga cikin kuskuren da ake yi a gida suna barin mummunan tasiri a rayuwar yara har zuwa girman su. Ga wasu daga cikin su:

‎1. Yawan Zagi da La’antar Yaro:
‎Iyayen mu na Hausawa sun kware a Zagi, zagi ba tarbiyya ba ce. Kalmar da uwa ke furtawa kan ɗanta tana iya zama addu’a ko la’ana. Idan kika saba cewa "kai maras amfani ne" to ki sani wannan kalmar Kai tsaye take zuwa zuciyarsa.

‎2. Bambanta Soyayya Tsakanin 'Ya'ya:
‎Yin fifiko tsakanin yara na janyo kiyayya, kaskanci, da rashin gaskiya. Yaro zai iya zama mai kishi ko ma ya fara ɗaukar hanyar da bata dace ba domin ya jawo kulawar ki a gareshi.

‎3. Rashin Jin Damuwar Yaro:
‎Yaro yana da damuwa. Idan uwa bata ware wasu lokutan sauraren yaro ba, hakan na sa suje neman shwara daga waje, wanda kan iya jefa su cikin hatsari.

‎4. Kadaici da Rashin Kyakkyawar Mu'amala:
‎Wasu uwayen suna barin yaransu ga telabiji, wayar salula ko masu aikin gida. Rashin kusanci tsakanin uwa da yaro na hana samun tarbiyya mai kyau.

‎5. Koya Musu Tsoro maimakon Soyayya:
‎Tarbiyya ta gaskiya ita ce tsoron Allah da fahimta, ba firgita yaro har ya kasa gaya miki damuwarsa ba.

‎Shawara ga iyaye mata:
‎ -Ki yawai ta addu’a akansu fiye da dura musu ashar.
‎ -Ki zama uwar da za a iya tattaunawa da ita.– Ki dinga bayyana soyayyar ki da kulawa a garesu.
‎ -Kada ki bari su koyo wani abu daga waje Wanda ba ke kika koya musu ba.

‎ Uwa tana iya gina alumma ta hanyar tarbiyyantar danta ta hanya Mai kayu. Matakin da kika dauka yau, itace zata Gina rayuwarsu ko kuma rusa ta🤲

‎ Gobenmu media

Attajirin Nahiyar Afrika Alhaji Aliko Ɗangote ya ce Kamfanin samar da ƙarafa na Ajaokuta na Najeriya ba zai taɓa yin aik...
17/09/2025

Attajirin Nahiyar Afrika Alhaji Aliko Ɗangote ya ce Kamfanin samar da ƙarafa na Ajaokuta na Najeriya ba zai taɓa yin aiki ba matuƙar yana ƙarƙashin gwamnati.

Ƙarin bayani: https://rfi.my/C1Ge

Najeriya ta saka harshen China a jerin darussan da ake koyarwa a manyan makarantun sakandare - Dakta Danlami Hayyo, saka...
17/09/2025

Najeriya ta saka harshen China a jerin darussan da ake koyarwa a manyan makarantun sakandare - Dakta Danlami Hayyo, sakataren ma'aikatar ilimi ta Abuja

Address

Kwaya Kusar
Maiduguri

Telephone

+2348103800353

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Gobenmu media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Gobenmu media:

Share