Jarida Online

Jarida Online Jarida Online

Mai gidana ya bar min wasiyyar cewa in roƙa masa gafarar ƴan Najeriya kafin ya rasu—Aisha BuhariMai ɗakin marigayi tsoho...
13/07/2025

Mai gidana ya bar min wasiyyar cewa in roƙa masa gafarar ƴan Najeriya kafin ya rasu—Aisha Buhari

Mai ɗakin marigayi tsohon shugaban Najeriya Muhammad Buhari Aisha, ta nemi ƴan ƙasar su yafewa mai gidanta tun gabanin a shigar da shi Kabari, Aisha tace.

"Tunda ya sauka daga mulki maganar da yake yawan faɗa min a duk lokacin da muke fira ita ce, idan ya riga ni mutuwa in isar da saƙon sa ga ƴan Najeriya cewar su yafe masa kura-kuren da yayi a mulkinsa kasancewar sa ɗan adam mai yin dai-dai da rashin dai-dai, saboda haka don Allah ina roƙon kowa da koya ya yafe masa tun kafin a kai shi makwancin sa"—In ji ta

Don Allah kowa ya tura wannan saƙon zuwa sauran groups don kowa ya gani muna fatan Allah ya yafe masa.

Yanzu Yanzu : An k**a Dan bello a KanoRahotanni daga filin jirgin saman Malam Aminu Kano na bayyana cewar jami'an tsaro ...
12/07/2025

Yanzu Yanzu : An k**a Dan bello a Kano
Rahotanni daga filin jirgin saman Malam Aminu Kano na bayyana cewar jami'an tsaro da ake zargin daga Abuja suke sun k**a matashi nan Bello Habib Galadanci da aka fi sani da Dan Bello.

Hamshaƙin attajirin kuma ɗaya daga cikin mutum mafi arziki a nahiyar Afrika, ya rasu a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa bayan ...
28/06/2025

Hamshaƙin attajirin kuma ɗaya daga cikin mutum mafi arziki a nahiyar Afrika, ya rasu a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa bayan fama da rashin lafiya k**ar yadda ɗaya daga cikin ƴaƴansa ya shaida wa BBC.

Ya rasu yana da shekaru 94, ya kuma bar matansa da ƴaƴa da jikoki da dama.

Da dumi'dumi: Masu ruwa da tsakin jam'iyyar APC sun amince da sake zaben Tinubu tare da Nuhu Ribadu.Masu ruwa da tsaki n...
17/06/2025

Da dumi'dumi: Masu ruwa da tsakin jam'iyyar APC sun amince da sake zaben Tinubu tare da Nuhu Ribadu.

Masu ruwa da tsaki na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Adamawa sun kada kuri’ar amincewa da gwamnatin shugaba Bola Tinubu.

Don haka, masu ruwa da tsakin da s**a yi magana a taron shugabannin jam’iyyar a Hong a ranar Talata, sun yi alkawarin goyon bayan sake zaben shugaban kasa a shekarar 2027 domin a samu karin ribar dimokuradiyya.

Mataimakin shugaban jam’iyyar APC na shiyyar Arewa maso Gabas, Salihu Mustapha, ya ce taron an yi shi ne da nufin wayar da kan shuwagabannin jam’iyyar don tabbatar da hadin kai da ci gaban jam’iyyar a jihar da ma kasa baki daya.

Mista Mustapha ya ce jam’iyyar a karkashin jagorancin Tinubu, ta samu gagarumar nasara da ta yi tasiri ga kasar nan.

Ya zayyana wasu nasarorin da aka samu da s**a hada da: aiwatar da mafi karancin albashi na N70,000, biyan bashi, cin gashin kan kananan hukumomi, cire tallafin mai da yaki da cin hanci da rashawa.


Shugaban kwamitin sasantawa da kawo sauyi a shiyyar Adamawa ta tsakiya, Yusuf Captain-Buba, ya kuma yabawa Tinubu bisa gagarumin kokarinsa na farfado da tattalin arziki da kawo sauyi a harkar noma.

“Tare da wadannan da wasu da dama wadanda ba za mu iya ambata a nan ba, mun kada kuri’ar amincewa da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da kuma mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, kan dakile matsalar rashin tsaro da ke addabar wasu sassan kasar nan,” inji shi.

Mista Captain-Buba ya ce aikin kwamitin na sa shi ne sulhunta ‘ya’yan jam’iyyar da s**a ji ra’ayinsu, tara jama’ar da s**a zabe su, da kwato kujerar gwamnan jihar da kuma sake zaben Tinubu a karo na biyu a shekarar 2027.

Don haka ya yi kira ga shugabannin kananan hukumomin jam’iyyar a fadin jihar da su tabbatar da adalci da kuma hakuri da juna a tsakanin ‘ya’yan kungiyar.

A nasa jawabin dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Gombi a majalisar dokokin jihar, Rufa'i Umar, ya ce taron ya bayyana wasu dabarun tunkarar kalubalen da ke fuskantar jam'iyyar.

NAN

YANZU YANZU: Asiri ya Tonu firaministan ƙasar Isr@'ila ya Fara Neman Sulhu ta Bayan Fage, inda ya Nemi Shugaban ƙasar R@...
14/06/2025

YANZU YANZU: Asiri ya Tonu firaministan ƙasar Isr@'ila ya Fara Neman Sulhu ta Bayan Fage, inda ya Nemi Shugaban ƙasar R@sha ya Shiga tsakanin su yayi Musu Sulhu da ƙasar Iran.

firaministan ƙasar Isr@'ila ya Nemi Ayi Zaman Sulhu tsakaninsa ƙasar Iran, Sai dai Shugaba Vladimir Putin ya ki amincewa da bukatar Netanyahu na yin sulhu da Iran don dakatar da yakin!

Isr@'ila ta yi kokarin kaucewa martanin da Iran ta mayar ta hanyar Moscow, amma Rasha ta dau matsaya ta ki shiga tsakani

Kada kumanta kudunga Shan yayi Mai zafi katinnan da gobe Israel tazama tarishin da yardar Allah i suntabo gidan Rina tsoho Mai rankarfe, Kunsandai manjor is coming soon ko

DA ƊUMI-ƊUMI; Ana dab da shafa Fatiha tsakanin fitattun jaruman kannywood Mansura Isah da Aminu Sharif Momo.Wana fata ku...
12/06/2025

DA ƊUMI-ƊUMI; Ana dab da shafa Fatiha tsakanin fitattun jaruman kannywood Mansura Isah da Aminu Sharif Momo.

Wana fata kuke yi wa jaruman?

Jiya wani ma'aikacin Gidan Yari (Correctional Service officer) Mai Babban mukami na CCA wato Chief Correctional Assistan...
12/06/2025

Jiya wani ma'aikacin Gidan Yari (Correctional Service officer) Mai Babban mukami na CCA wato Chief Correctional Assistant Abdullahi Nura dake aiki a Gidan Yari na Gusau yayi yunkurin k@she kanshi amma cikin taimakon Allah an ceto shi Bai mutu ba.

Wani bayani daga Gidan Yarin Mai dauke da SA hannun Mai magana da hukumar Gidan Yarin ASC1 Mustapha Abubakar yace da safiyar jiya Laraba Sai da Abdullahi Nura yaje Wurin aiki, Sai Kuma ya fita ya hau kabu kabu aka kaishi Dam din Baga na Hanyar Wanke, kawai sai yayi Tuma ya fada a cikin Ruwan. Nan take Dan Kabu-Kabun yayi gudu ya shaidawa ma'aikatan Wurin inda s**a kokari matuka s**a ceto shi.

KO da aka fito da shi Yana sanye da Uniform din shi waton Kayan aiki da I.D Card din shi sai aka kai shi Asibiti inda yanzu haka yake karbar Magani.

Har yanzu ba a San Dalilin Shi ba.

A.B.Kaura

Subhanalillah: Adam a zango ya gamu da hatsari a hanyarsa ta zuwa kano daga kaduna.Hatsarin daya rutsa da Fitaccen jarum...
09/06/2025

Subhanalillah: Adam a zango ya gamu da hatsari a hanyarsa ta zuwa kano daga kaduna.

Hatsarin daya rutsa da Fitaccen jarumin da wasu abokan sana’arsa ya afku ne a kwanar dan Gora kafin maiyaki, daga nan alummar yakin s**ayi gaggawar kaishi wani asibiti dake garin Kwankwaso a Karamar hukumar Madobin jihar kano, daga nan ake sa ran wucewa dashi wani babban asibitin k**ar yanda daya daga cikin yaransa da s**a gamu da hatsarin tare ya sanar dani a daren yau.

Ko dayake jarumin ya fito ya bayyana godiyarsa ga masoyansa a shafinsa na fesibuk bisa ga addu’o’in da suke masa.ll

✍🏻✍🏻✍🏻Abdussamad Ishaq

Tsohon Sanatan Adamawa ta Arewa, Dr. Ishaku Elisha Abbo, ya tabbatar da mutuwar aurensa da matarsa, Patience, bayan shaf...
09/06/2025

Tsohon Sanatan Adamawa ta Arewa, Dr. Ishaku Elisha Abbo, ya tabbatar da mutuwar aurensa da matarsa, Patience, bayan shafe shekaru biyu da rabi da aure.

Wannan na zuwa ne bayan Patience Abbo din ta wallafa sako a shafinta na Facebook a safiyar Talata, 3 ga Yuni, 2025, inda ta ce:

“Mun shafe shekaru biyu da rabi tare. Mun yi ƙoƙari, amma yanzu ya fi dacewa mu rabu juna, Lallai mun fita daga rayuwa mara dadi, Ina yi maka fatan alheri, wannan shafin kuma an rufe shi.”

Awa guda bayan hakan, tsohon Sanatan ya wallafa nasa sakon inda ya ce:

“Ina sanar da mutuwar aurenmu ni da Patience. Don Allah a girmama sirrinmu, Allah ya albarkaci kowa. Na gode.”

Mutuwar auren nasu ta janyo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta, inda jama’a ke tofa albarkacin bakinsu kan dalilan rabuwarsu.

An k**a ‘yan kasar Pakistan din ne yayin da rundunar ta kai wani farmakinta a wasu sansanonin ‘yan ta’adda. Bincike na f...
30/05/2025

An k**a ‘yan kasar Pakistan din ne yayin da rundunar ta kai wani farmakinta a wasu sansanonin ‘yan ta’adda.

Bincike na farko ya nuna cewa wadannan mutanen na da hannu a sayar da mak**ai da kuma horar da 'yan ta'adda irin su Boko Haram da ISWAP.

Sanata mai wakiltar yankin Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta bayyana cewa tana da cikakken shiri na fuskantar...
29/05/2025

Sanata mai wakiltar yankin Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta bayyana cewa tana da cikakken shiri na fuskantar shari’ar batanci da gwamnatin tarayya ta shigar a kanta, amma ta dage cewa dole ne hukumomi su binciki zarge-zargen da ta yi wa Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, da tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello.

Akpoti-Uduaghan, wadda ke kasashen waje a halin yanzu bisa wasu harkokin kashin kanta, ta tabbatar da samun sammaci daga kotu, kuma ta bakin lauyoyinta ta bayyana cewa za ta amsa kiran kotu idan aka tsara ranar shari’ar

“Ta na da cikakken kuduri wajen bin doka kuma za ta kare kanta a gaban kotu,” in ji lauyanta, Uju Nwoduwu, cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba. “Amma dai adalci bai k**ata ya zama na bangare guda ba. ’Yan sanda su binciki dukkan korafe-korafen da aka shigar—musamman wadanda s**a shafi manyan jami’ai irin su Akpabio da Bello.”

Tawagar lauyoyin sanatar sun nuna damuwa kan abin da s**a kira "biyayya ga masu iko", inda s**a ce sun gabatar da takwas zuwa goma sha biyu na korafe-korafe tsakanin watan Maris da Mayu 2025, wadanda s**a hada da zarge-zargen cin mutunci ta intanet, batanci, barazana ga rayuwa, cin zarafin jima’i da ma yunkurin kisa—amma dukkansu ba su samu kulawa daga ’yan sanda ko hukumomin tsaro ba.

A bangare guda kuma, sun ce korafe-korafen da Akpabio da Bello s**a shigar kan sanatar an dauka da gaggawa, kuma hakan ya kai ga gurfanar da ita a gaban kotu.

Lauyoyin sun bayyana hakan a matsayin “bambancin adalci da ke kara jefa shakku ga tsarin shari’a”, inda s**a bukaci Sufeto Janar na ’Yan Sanda da Attoni Janar na Tarayya su tabbatar da bin doka daidai ba tare da nuna bambanci ba.

Gwamnatin tarayya ta shigar da karar ne a ranar 16 ga Mayu bisa sashe na 391 na dokar Penal Code, tana zargin Natasha da furta kalaman batanci a wata hira da aka yi da ita a talabijin.

Zargin da ke kunshe a karkashin sashe na 392 na hukuncin dokar ya ambaci Akpabio da Bello a matsayin shaidu na bangaren masu kara.

Ana zargin Akpoti-Uduaghan da cewa ta yi ikirarin cewa Akpabio da Bello sun hada baki don kashe ta—zargi da ta danganta da dakatarwar da aka yi mata daga majalisa sak**akon sabani da aka samu kan wurin zama.

Haka kuma, ta zargi Akpabio da cin zarafin jima’i kuma ta riga ta shigar da korafi ga hukumomi domin a gudanar da cikakken bincike.

“Ina sa ran jami’an tsaro za su gudanar da aiki da adalci da daidaito,” in ji lauyoyinta. “Adalci dole ne ya tabbata, kuma mutane su ga an yi shi—ba tare da la’akari da mukami ko tasirin siyasa ba.”

Yayin da s**a gode wa jama’a bisa goyon bayan da suke baiwa sanatar, lauyoyin sun sake jaddada bukatarta ta cewa lallai ne a binciki dukkan korafe-korafen da ke gabanta da irin gaggawar da aka nuna wajen shigar da kara a kanta.

Wata Mahajjaciyar Nijeriya Ta Haihu A Saudiyya
27/05/2025

Wata Mahajjaciyar Nijeriya Ta Haihu A Saudiyya

Address

Maiduguri

Telephone

+2348030452850

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jarida Online posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jarida Online:

Share

Category