Allura Newspaper

Allura Newspaper Allura is a Hausa Online Newspaper. Allura jarida ce da ake bugawa da Hausa. Ta na dauke da:
Labara

RAHOTON MUSAMMAN: Mun Zabi Gwamnati ta Kone Mana Jari Karkaf -Kungiyar Bola-bolaDaga WakilinmuDubban 'yan Kungiyar Bola-...
20/10/2019

RAHOTON MUSAMMAN: Mun Zabi Gwamnati ta Kone Mana Jari Karkaf -Kungiyar Bola-bola

Daga Wakilinmu

Dubban 'yan Kungiyar Bola-bola, Metal Scrab and Craftmanship da ke Abuja, masu aikin sarrafa tsoffin karafuna, robobi da irin su alminiyan, ba za su taba mantawa da ranar Asabar, 5 Ga Oktoba, 2019 ba.

A wannan rana ce gangamin jami'an tsaro na JTF daga Hukumar Tsaftace Abuja, s**a yi wa kasuwar wadda ke Jabi ko kuma masana'antar dirar dakarun yaki, su ka banka mata wuta, ta kone kurmus.

Ba karamar asara daruruwan masu harkoki su ka yi a wannan kasuwa da za a iya raina-kama-ka-ga-gayya ba.

Dalili, wuri ne da ake saye, sayarwa da kuma sarrafa kayan karambosuwa, a takaice dai jari-bola kenan. Amma dubban jama'ar da ke harkar da kuma irin dimbin dukiyar da aka yi asara, ta na da yawan gaske.

Makonni uku kafin a kone kasuwar kurmus, jami'an tsaron sun je da katafita s**a ruguje dukkan wurin kakaf. Amma ba a kone musu wurin ba.

Sai dai kamar yadda wakilin mu ya ji da bakin sa daga wasu da s**a yi dimbin asara a wurin, sun tabbatar da cewa an yi musu satar kayayyaki a wurin, kuma sun zargi ma'aikatan rusau din.

Musa Amadu, wanda aka fi sani da suna Dogo, ya shaida wa wakikin mu cewa ya dibga asara ta kudi ba kadara ba, naira milyan 1,600,00, kuma sace kudin aka yi.

"Sun zo su na harbe-harbe, har da dukan mu a ranar. S**a hana kowa shiga. Sannan s**a sa katafila s**a rika rushe mana wuri. Ba su bar mu mun shiga ba. Bayan sun tafi na shiga na samu an kwashe min kudi na."

Ya ci gaba da cewa akwai jami'an da s**a je da jaka, s**a rika kwasar wayoyin mutane su na zubawa jakar su.

"Sau hudu kenan ana kawo mana hari ana rushe mu tun daga hawan Shugaba Muhammadu Buhari a 2015. Amma wannan na baya da s**a kona mana dukiya, ya fi muni matuka. Saboda sun zo da katafila ta masu yawan gaske.

GWAMNATIN APC TA WULAKANTA MU -Salisu Adamu

Mataimakin Shugaban Kungiyar na Jabi da ke kasuwar kayan karambosuwar da aka kona, Salisu Adamu, ya shaida cewa sun yi amfani da karfin su da dukiyar su da kuri'in su, sun zabi Gwamnatin APC har a 2019. Amma ta kwance musu zani a kasuwa. Ta talauta dubban masu harkar jari-bola.

"Kafin zaben 2019, har gagarimin taro 'yan kungiyar mu ka shirya 'Parade Ground', wanda dubban mu mu ka je domin nuna goyon baya ga Buhari da APC. Haka da zabe ya zo duk mu ka je mu ka zabi APC.

" Amma tun ba a je ko'ina ba, an rushe mana wurin sana'a, an kone mana jari na milyoyin nairori. Kuma gwamnatin da mu ka sha wahalar zabe. Shin yaya ta ke son dubban matasan da ke wannan harkokin su yi ne a rayuwar su?"

Shi kuwa daga daga cikin mambobi, kuma iyayen kungiyar, Alhaji Babangida Bature, ya shaida wa wakilin mu cewa, ya kamata Gwamnati ta sani cewa ta haddasa wa matasa dubbai asarar rashin aikin yi.

"Wadannan matasa da aka kona wa kaya, a karkashin kungiya su ke. Kuma ta na da rajista da CAC. Kungiyar nan ta na bada hadin kai ga jami'an tsaro. Akwai jarin sama da milayan 300 a cikin harkar nan a Abuja da sauran jihohi.

"Duk wani kokarin tsaftace harkar ana yi, kuma hukuma ta sani. Yaran nan su na taimakawa wajen tsaftace Abuja da kewaye.

"Na san a ko'ina akwai batagari da na kwarai. To kungiya na kokarin ta, kuma ba a sayen kayan sata. Ya kamata gwamnati ta sake tunanin yadda za ta gyara wannan harka, ba wai a raba dubban jama'a da sana'ar su ba.

Binciken da wakilin mu ya yi, ya gano cewa akwai masana'antun sarrafa karafuna da yin robobi wadanda ke sayen kayan karafa da tsoffin robobi a wurin su.

Akwai Rida National Plastic, Lagos, Hart Plastic, Kano, Songhai Plastic, Ogun, Saz EPZ, Kano, BBY Plastic, Kano da kuma Rumbu Sacks, Kano.

Sakataren kungiyar, Malam Misbahu, ya shaida wa wakilin mu cewa akwai ka'idojin shiga kungiyar da s**a hada da rajista, wanda zai tsaya wa sabon mamba, hoto, fam, sannan sai ID card, bayan an gamsu da halin sa. Ya ce su na da mambobi a Abuja za su kai 10,000.
"Amma idan aka hada da na Kananan Hukumomin Abuja shida, mun fi 200,000." Inji Misbahu.

Shi kuwa Shugaban Kungiyar, Auwalu Abdullahi, ya shaida wa wakilin mu cewa kungiyar su mai hedikwata a Jabi, kusa da ofishin Jaridar THISDAY a Abuja, sananne ne a kasar nan, domin cikin iyayen su ma har da Gwamnan Katsina, Aminu Bello Masari.

Ya ce bai kamata gwamnatin da ta yi wa al'umma alkawari samar wa milyoyin matasa aiki, kuma ta koma ta na ruguza sana'o'in da dubban matasa s**a kirkirar wa kan su da kan su ba.

Ya yi kira da a ja matasa a jika, domin rashin aikin yi na kara yawaitar kangararrun yara a cikin al'umma.

Ko ma dai me kenan, a ranar 10 Ga Oktoba, wannan kungiya ta rubuta takardar korafi zuwa ofishin Ministan Babban Birnin Tarayya, Abuja.

Dama kuma ko a can baya kungiyar ta sha yin taruka da jami'an tsaro, har ma da shi ministan kan sa sun yi.

Kokarin jin ta bakin sauran wadanda abin ya shafa bai yiwu ba. Amma za mu kawo mu ku na su ba'asin nan gaba.

Shin ya gwamnati za ta yi da dubban matasan da s**a rasa sana'a, abinci da sauran kudin yin bukatu na dole, sanadiyyar rushe 'yan Bola-Bola da ke Jabi?

AIKIN ZABE: Yadda INEC ta ja nakasassu 81 a jikaDaga WakilinmuHukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC ta bayyana cewa...
17/10/2019

AIKIN ZABE: Yadda INEC ta ja nakasassu 81 a jika

Daga Wakilinmu

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC ta bayyana cewa akwai matasa masu ilmi, amma nakasassu har 81 da ta dauka domin aikin zaben gwamna a Jihar Kogi.
Za a gudanar da zaben gwamna a jihohin Kogi da Bayelsa a ranakun 16 Ga Nuwamba.

Daraktan wayar da kai dangane da al’amurran zabe na jihar Kogi, Ahmed Biambo ne ya bayyana haka a jiya Laraba, a wurin wani taron wayar dan masu nakasa da za su gudanar da aikin zabe a jihar ta Kogi.

Biambo ya shaida wa manema labarai cewa wadannan nakasassu 81 an dauke su ne a matsayin jami’an zabe da mataimakan jami’an zabe.

Daga nan sai ya ce duk za a tura su a jihohi 21 na jihar, amma ba za a tura su a yankunan da ake zaman dar-dar din kaffa-kaffa da barkewar rikici ba.

Biambo ya ce Kwamishinan Zabe na Tarayya a Jihar Kogi (REC), ya umarce su da a tura nakasassun a yankunan da ba a tunanin wata tashin-tashina.

Shi kuwa Shugaban Hadaddiyar Kungiyar Nakasassu ta Kasa (JONAPWD), Solomon Yahaya, ya tabbatar da daukar nakasassun aikin zaben a Jihar Kogi ga PREMIUM TIMES.
Ya gode wa INEC dangane da kaifin tunanin da ta yi wajen daukar nakasassun yin aikin zabe. Hakan inji shi ya kara tabbatar wa nakasassun cewa a ba maida su saniyar-ware ba.

Sannan ya yi kira ga dukkan nakasassun da aka dauka aikin zaben su yi aiki tsakanin su Allah tare da kishi ba tare da son kai ba.

Can a Jihar Bayelsa kuma, inda za a gudanar da zaben gwamna a rana daya da Kogi, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC ta yi kakkausan gargadin cewa Dimokradiyya ba kayan sayarwa ba ce. Don haka duk mai kokarin sayen kuri’u a loakcin zaben gwamna, to ya kuka da kan sa.

Shugaban Hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya yi wannan dangane da gabatowar zaben gwamna a Jihar Bayelsa.

Yakubu ya yi wannan gargadi a lokacin da ya ke taron ganawa da sarakunan gargajiya na Jihar Bayelsa, inda ya fassara sayen kuri’u tamkar cefanar da dimokradiyyar Najeriya ce a kasuwar ‘yan gwan-gwan.

A taron wanda aka gudanar a Yenagoa, babban birnin Jihar Bayelsa, Yakubu ya ce sayen kuri’u na daya daga cikin kalubalen da INEC ke fama da shi a lokutan zabe a kasar nan.

“Damuwar mu ta farko ita ce kalaman da ka iya haddasa barkewar rikici a lokutann kamfen, lokutan gudanar da zabe da kuma lokutan da ake tattara sakamakon zabe.

“Wani kalubalen kuwa shi ne saye da sayar da kuri’u. Bai yiwuwa a bar wasu ‘yan gwan-gwan masu kokarin saida dimokradiyya a tsakiyar kasuwa; ya zama tilas a bar kowane dan Najeriya ya zabi wanda ya ke ra’ayi a ranar zabe, ba tare da an cunna masa kudi ya saida ‘yancin sa ba.
“Ya kamata mu tashi tsaye mu dakile annobar sayen kuri’u. INEC ba jam’iyyar siyasa ba ce, kuma ba ta goyon bayan kowace jam’iyya, ko wani dan takara. Wanda jama’a s**a zaba, shi ne zai wakilce su.”

AIKIN ZABE: Jihohin Kogi da Bayelsa na da wuyar sha’ani –Farfesa YakubuDaga WakilinmuShugaban Hukumar Zabe (INEC), Farfe...
16/10/2019

AIKIN ZABE: Jihohin Kogi da Bayelsa na da wuyar sha’ani –Farfesa Yakubu

Daga Wakilinmu

Shugaban Hukumar Zabe (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa idan ana batun sha’anin gudanar da zabe, to jihohin Kogi da Bayelsa na da wahalar sha’ani.

4. Yakubu ya bayyana haka a jiya Talata, a yayin wani taron neman goyon bayan sarakunan gargajiyar Jihar
Bayelsa, wajen tabbatar da ganin cewa an gudanar da zaben gwamnan jihar lami lafiya, a ranar 16 Ga Nuwamba mai zuwa.

5. Yakuwa wanda kuma ya yi magana da wakilan jam’iyyun da s**a fito takara a jihar, ya ce halayyar da manyan ‘yan siyasar jihohin biyu ke nunawa a lokutan zabe abu ne mai kawo wa INEC Kalubale ba karami ba.

6. Ya ce a yau saura kwanaki 1 a gudanar da zaben gwamna a jihohin biyu. Gaba daya idon duniya duk ya komawa a kan wadannan jihohi biyu, domin ganin yadda INEC za ta gudanar da zabe.

7. Yakubu ya ce duk an ga yadda aka yi kakudubar gudanar da zabukan fidda-gwani a jihohin biyu, an kuma fara kamfen na neman kuri’un jama’a a ranar zabe, za a ci gaba da kamfen har ana saura sa’o’i 24 a fara zabe. Cewar Yakubu.

8. Farfesan kuma shugaban na INEC, ya ce za a yi amfani da ma’aikatan INEC 10,000 A Jihar Bayelsa, jihar Kogi kuma 14,000.

9. Haka nan kuma, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC ta yi kakkausan gargadin cewa Dimokradiyya ba kayan sayarwa ba ce. Don haka duk mai kokarin sayen kuri’u a loakcin zaben gwamna, to ya kuka da kan sa.

10. Shugaban Hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya yi wannan dangane da gabatowar zaben gwamna a Jihar Bayelsa.

11. Yakubu ya yi wannan gargadi a lokacin da ya ke taron ganawa da sarakunan gargajiya na Jihar Bayelsa, inda ya fassara sayen kuri’u tamkar cefanar da dimokradiyyar Najeriya ce a kasuwar ‘yan gwan-gwan.

12. A taron wanda aka gudanar a Yenagoa, babban birnin Jihar Bayelsa, Yakubu ya ce sayen kuri’u na daya daga cikin kalubalen da INEC ke fama da shi a lokutan zabe a kasar nan.
13. “Damuwar mu ta farko ita ce kalaman da ka iya haddasa barkewar rikici a lokutann kamfen, lokutan gudanar da zabe da kuma lokutan da ake tattara sakamakon zabe.

14. “Wani kalubalen kuwa shi ne saye da sayar da kuri’u. Bai yiwuwa a bar wasu ‘yan gwan-gwan masu kokarin saida dimokradiyya a tsakiyar kasuwa; ya zama tilas a bar kowane dan Najeriya ya zabi wanda ya k era ra’ayi a ranar zabe, ba tare da an cunna masa kudi ya saida ‘yancin sa ba.

15. “Ya kamata mu tashi tsaye mu dakile annobar sayen kuri’u. INEC ba jam’iyyar siyasa ba ce, kuma ba ta goyon bayan kowace jam’iyya, ko wani dan takara. Wanda jama’a s**a zaba, shi ne zai wakilce su.”

16. Yakubu ya nuna damuwa dangane da irin yadda jihar Bayelsa ke da wahalar gudanar da zabe, saboda yadda jihar ta ke.

17. Shi kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Bayelsa, Alfred Diete-Spiff, ya nuna damuwa ganin yadda sojoji ke karaikaina a jihar a duk lokacin da zabe ya zo.

18. Ya kuma nuna damuwa ganinn yawan masu gudun hijirar da s**a rasa muhallin su a wasu sassan jihar ta Bayelsa.

GARGADI: Dimokradiyya Ba Kayan Sayarwa Ba Ce –Inji INECDaga WakilinmuHukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC ta yi ka...
16/10/2019

GARGADI: Dimokradiyya Ba Kayan Sayarwa Ba Ce –Inji INEC

Daga Wakilinmu

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC ta yi kakkausan gargadin cewa Dimokradiyya ba kayan sayarwa b ace. Don haka duk mai kokarin sayen kuri’u a loakcin zaben gwamna, to ya kuka da kan sa.

Shugaban Hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya yi wannan dangane da gabatowar zaben gwamna a Jihar Bayelsa.

Yakubu yay i wannan gargadi a lokacin da ya ke taron ganawa da sarakunan gargajiya na Jihar Bayelsa, inda ya fassara sayen kuri’u tamkar cefanar da dimokradiyyar Najeriya ce a kasuwar ‘yan gwan-gwan.

A taron wanda aka gudanar a Yenagoa, babban birnin Jihar Bayelsa, Yakubu ya ce sayen kuri’u na daya daga cikin kalubalen da INEC ke fama da shi a lokutan zabe a kasar nan.
“Damuwar mu ta farko ita ce kalaman da ka iya haddasa barkewar rikici a lokutann kamfen, lokutan gudanar da zabe da kuma lokutan da ake tattara sakamakon zabe.

“Wani kalubalen kuwa shi ne saye da sayar da kuri’u. Bai yiwuwa a bar wasu ‘yan gwan-gwan masu kokarin saida dimokradiyya a tsakiyar kasuwa; ya zama tilas a bar kowane dan Najeriya ya zabi wanda ya k era ra’ayi a ranar zabe, ba tare da an cunna masa kudi ya saida ‘yancin sa ba.

“Ya kamata mu tashi tsaye mu dakile annobar sayen kuri’u. INEC ba jam’iyyar siyasa ba ce, kuma ba ta goyon bayan kowace jam’iyya, ko wani dan takara. Wanda jama’a s**a zaba, shi ne zai wakilce su.”

Yakubu ya nuna damuwa dangane da irin yadda jihar Bayelsa ke da wahalar gudanar da zabe, saboda yadda jihar ta ke.

Shi kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Bayelsa, Alfred Diete-Spiff, ya nuna damuwa ganin yadda sojoji ke karaikaina a jihar a duk lokacin da zabe ya zo.

Ya kuma nuna damuwa ganinn yawan masu gudun hijirar da s**a rasa muhallin su a wasu sassan jihar ta Bayelsa.

Ya yi rokon kada sojoji su yi irin aika-aikar da s**a yi a lokacin zaben 2015 a jihar ta Bayelsa.

An kai INEC kara sau 1600 a kan zaben 2019 –YakubuDaga WakilinmuShugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Fa...
11/10/2019

An kai INEC kara sau 1600 a kan zaben 2019 –Yakubu

Daga Wakilinmu

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa an hada da sunan INEC an kai kararrakin zabe har sau sama da 1600 a sanadiyyar zaben 2019.

Yakubu ya ce wadannan kararraki duk sun bijiro ne bayan zaben 2019 da aka gudanar cikin watan Fabrairu da kuma Maris.

Ya yi wannan bayani a yau Alhamis, lokacin da ya bayyana a taron farko da shugaban na INEC ya yi da Kwamitin Majalisar Dattawa na INEC.

Farfesa Yakubu ya yi wa kwamitin bayanai daban-daban a lokacin da ya ke ba su rahoton hukumar sa tun bayan kammala zaben 2019.

Da aka tambaye shi ta ina INEC ke dibar kudin daukar nauyin sha’anin kararrakin da aka maka ta, sai Yakubu ya ce akasari sun a amfani ne da lauyoyin su da ke karkashin hukumar, wadanda yawan su bai kai yawan wadanda ake bukata domin kula da shari’un da ke gaban INEC din ba.

“Misali, bayan an kammala zaben fitar-da-gwani kafin zaben 2019, an maka INEC kara a kotuna daban-daban, sama da sau 800.

“Akwai kararraki 809 a gaban mu da s**a bijiro kafin zabe, sannan kuma akwai wasu 807 da s**a bijiro bayan zaben 2019. Kai ko jiya ma an maka INEC kara kotu sau uku, sakamakon abin da ya biyo bayan zaben fidda-gwani a jihohin Bayelsa da Kogi.” Inji Yakubu.

Daga nan kuma ya sanar da sanatocin irin shirin da INEC ta yi domin tunkarar zabukan gwamna a Bayelsa da Kogi da za a gudanar rana daya, cikin watan Nuwamba.

Sannan kuma Farfesa Yakubu ya yi watsi da ikirarin da wasu ke yi cewa INEC na fama da matsalar kudaden shirya zaben gwamna a Bayelsa da Kogi.

Ya ce ai akwai kudaden kasafin kudi na INEC din daban, wadanda daban su ke da kasafin kudaden zabe.

A yanzu dai akwai kararraki sama da 1600 da da s**a danganci zaben 2019, kuma kowace kara sai an hada da INEC an maka kotu.

Kusan an kammala shari’un zaben gwamna, wanda har yau babu wani gwamna da kotun Daukaka Kararrakin Zaben Gwamna ta tsige.

Yayin da PDP da kuma dan takarar ta Atiku Abubakar s**a garzaya Kotun Koli, domin nuna rashin gamsuwa da hukuncin da Kotun Daukaka Kararrakin Zaben Shugaban Kasa ta yanke.

Kotun dai ta yanke hukucin cewa Atiku da PDP sun kasa gabatar da kwararan shaidun zarge-zargen da s**a yi wa zaben 2019, ballanatana har kotu ta soke nasarar da APC da dan takarar ta s**a samu, a bai wa Atiku da PDP.

ZABEN 2019: Rashin tabukawar da mata s**a yi abin damuwa ne -INECDaga WakilinmuShugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta ...
30/09/2019

ZABEN 2019: Rashin tabukawar da mata s**a yi abin damuwa ne -INEC

Daga Wakilinmu

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ya bayyana damuwar hukumar dangane da rashin damawar da ba a yi da mata sosai a siyasar 2019 ba.

Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa baya ga rashin yawaitar mata shiga takarar zabe, hatta a wajen jefa kuri'a ma ba ta ba su fito kamar yadda aka yi zato ba.

Yakubu ya yi wannan bayani ne a ranar Juma'a, wurin taron bitar yadda Zaben 2019 ya kasance.

Da ya ke jawabi, wanda ya wakilci shugaban na INEC, wato Adekunle Ogunmola, ya ce dukkan kokarin da INEC ta yi wajen wayar da kan mata da su shiga a dama da su, bai shiga kunnuwan matan yadda ake so ba.

Ya ce irin fitowar da mata s**a yi domin fafatawa a zaben 2019, ba ta yi armashi ba, domin abin da tsarin daidaito ya nuna shi ne a bai wa mata damar akalla kashi 35 bisa 100.

Sai dai kuma ya yi hasashen cewa akwai matsaloli ko dalilan da su ka haddasa rashin tabukawar da matan s**a yi. Ya ce yawancin su ba a kan mulki su ke ba, sannan kuma akwai rashin kudade tare da su.

A bayanin sa, ya ce mata da dama sun fito takara, amma yawanci ba su yi nasara a zabukan fidda-gwani ba saboda zabukan sun zo da rudani da giribtu da kuma hauma-hauma.

Ya ce an samu mata a takarar shugaban kasa su 5 kadai, daga cikin 'yan takara 73. Sannan mata 232 daga cikin masu takarar sanata 1,665.

A takarar majalisar tarayya kuwa, mata 533 aka samu daga cikin masu takara 4,139. Yakubu ya ce an samu mata 7 sanatoci daga cikin 109. Sai kuma mata 11 a Majalisar Tarayya daga cikin mambobi 390.

Babu mace gwamna, amma an samu mata 4 a mukamin mataimakin gwamna.

Yakubu ya ce INEC ba za ta gajiya ba, za ta ci gaba da tunatar da mata domin shiga a dama da su.

ZABEN KOGI: Ba mu soke kowane dan takara ba –INEC Daga WakilinmuHukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, ta bayyana c...
24/09/2019

ZABEN KOGI: Ba mu soke kowane dan takara ba –INEC

Daga Wakilinmu

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, ta bayyana cewa ba ta soke kowane dan takarar gwamnan Jihar Kogi ba.
INEC ta bayyana cewa wannan batu bai ma taso ba, ballantana har a ce an soke takarar wani.

Kakakin Yada Labarai na INEC, Rotimi Oyekanmi, ya ce amma dai wa’adin ranar canja sunan dan takara a maye gurbin sa da wani, ya wuce tun ranar Litinin, 23 Ga Satumba.
“Jadawalin harkokin zaben gwamnan Jihar Bayelsa da Kogi ya nuna cewa INEC za ta lika sunayen ‘yan takara a ranar 17 Ga Oktoba. Wa’adin ranar sauya sunan dan takara ya wuce tunn jiya Litinin, 23 Ga Satumba. Sannan kuma a ranar 2 Ga Oktoba za a rufe karbar fam wanda ‘yan takara s**a cike daga jam’iyyun su.

“Don haka ba ma daidai ba ne a rika yin azarbabi tun yanzu ana cewa INEC ta soke sunayen wasu ‘yan takara.

Rotimi ya ce har yanzu lokacin tunanin soke dan takara bai ma zo ba tukunna.

A tsarin INEC dai san shekara 35 ne abin da ya yi sama zai iya tsayawa takarar gwamna.

Duk da cewa INEC ba ta da hurumin soke dan takarar da jam’iyya ta gabatar mata sa sunan sa, duk da haka ta ce za ta sanar da jam’iyyar da abin ya shafa da kuma tunanin matakin da za ta dauka a gaba.


12:01 ·

ZABEN GWAMNAN KOGI DA BAYELSA: INEC Ta Bai Wa Jami’an Tsaro Da Masu Sa-ido Horo

Daga Wakilinmu

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta Ta Kasa (INEC), ta bada horo na kwanaki biyu ga jami’an tsaro da masu sa-ido kan yadda zabe ke gudana a zaben gwamna da za a yi a Jihar Bayelsa.

Cibiyar TEI da ke karkashin Hukumar INEC ce ta bada hoton tare da hadin-guiwar Gamayyar Hukumomin Sa-ido Kan Zabe (ICCES), domin shirya wa nasarar gudanar da zaben jihar ta Bayelsa.

Da ya ke magana a wurin bada horon, Shugaban Hukumar INEC, Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa makasudin horon dais hi ne domin a tabbatar da an gudanar da zaben lami lafiya ba tare da hargitsi ba.

Yakubu, wanda Kwamishinan Tarayya na Zaben Jihar Bayelsa, Monday Udoh ya wakilta, y ace INEC ta dauki jami’an tsaro da kuma samar samar da tsaron a matsayin daya daga cikin manyan ginshikan shirya zabe.

Daga nan kuma ya kara da cewa samar da tsaro na daga cikin abin da ke kara tabbatar da sahihanci da ingancin zabubbuka.

“Mafi yawan gyare-gyaren da aka yi wa shirye-shiryen zabe a hukumar INEC ya bambanta da abin da mu ka sani a baya. Don haka akwai matukar muhimmancin dukkan masu ruwa da tsaki a harkokin gudanar da zabe, musamman jami’an tsaro su gane kuma su fahimci wadannan matakai kuma a sanar da su sabbin abubuwan da aka bijiro da su.

A daya gefen kuma, Hukumar INEC ta umarci jami’an ta su gano duk wata hanya da za a iya kawo wa zaben gwamnan jihar Kogi da za a gudanar a ranar 16 Ga Nuwamba.
Za a gudanar da zaben a rana daya da na gwamnan jihar Bayelsa.

Kwamishinar INEC ta Kasa, Amina Zakari ce ta bada wannan umarnin a jiya Alhamis a Lokoja, babban birnain Jihar Kogi a lokacin da ta ke bude taron kwanaki biyu da aka shirya wa Jami’an Zabe da Mataimakan Jami’an Zabe da kuma wasu ma’aikata daga jiha da kuma hedikwatar hukumar zabe ta kasa.

Amina ta ce gano wannan barazana zai taimaka wajen kawar da ita tun yanzu da wuri, ba sai wuri ya kure ba.
Ta kara da cewa INEC ta dogara kacokan a kan jami’an ta da za su gudanar da aikin zaben, wajen samun nasarar gdanar da sahihin zabe.

Daga nan sai ta yi kira da su cewa su kasance sun samu masaniyar yadda al’amurra ke gudana a yankunan da za su yi aikin zabe.

Idan ba a manta ba, farkon wannan makon ne Hukumar INEC ta nuna fargabar samun barazana a zaben gwamnan jihar Kogi.

Kwamishinan Zabe na Jihar Kogi, Farfesa James Apam, a ranar Talata, 17 ga watan Satumba ya nuna damuwa akan yiwuwar barkewar rikici a lokacin zaben gwamna da za a yi a ranar 16 ga watan Nuwamba, a jihar.

Apam ya bayyana hakan ne a wajen wani taron masu ruwa da tsaki da aka yi a Lokoja. Ya bayyana cewa a karo da dama hukumar INEC ta shirya gudanar da zabe na gaskiya sannan kuma a koda yaushe tana daukar matakan da ya kamata don tabbatar da zabe na gaskiya da amana, kawai sai a zo a tarwatsa shi da rikici.

Kwamishinan zaben ya bayyana cewa hukumar na da niyyar gyara matsalolin da aka gane a zabukan da s**a gabata a zabe mai zuwa. Apam ya yi kira ya iyaye musamman mata da su taimaka wajen yi wa yaransu magana akan guje na rigima,

Ya kara da cewa idan har babu rikici, to mutane za su fito sosai a lokacin zabe sannan shirin zai kasance mai sauki. Kwamishinan zaben ya kuma bukaci masu zabe da su kimtsa kansu yadda ya kamata a lokacin zaben domin saukaka komai

ZABEN GWAMNAN KOGI DA BAYELSA: INEC Ta Bai Wa Jami’an Tsaro Da Masu Sa-ido HoroDaga WakilinmuHukumar Zabe Mai Zaman Kant...
20/09/2019

ZABEN GWAMNAN KOGI DA BAYELSA: INEC Ta Bai Wa Jami’an Tsaro Da Masu Sa-ido Horo

Daga Wakilinmu

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta Ta Kasa (INEC), ta bada horo na kwanaki biyu ga jami’an tsaro da masu sa-ido kan yadda zabe ke gudana a zaben gwamna da za a yi a Jihar Bayelsa.

Cibiyar TEI da ke karkashin Hukumar INEC ce ta bada hoton tare da hadin-guiwar Gamayyar Hukumomin Sa-ido Kan Zabe (ICCES), domin shirya wa nasarar gudanar da zaben jihar ta Bayelsa.

Da ya ke magana a wurin bada horon, Shugaban Hukumar INEC, Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa makasudin horon dais hi ne domin a tabbatar da an gudanar da zaben lami lafiya ba tare da hargitsi ba.

Yakubu, wanda Kwamishinan Tarayya na Zaben Jihar Bayelsa, Monday Udoh ya wakilta, y ace INEC ta dauki jami’an tsaro da kuma samar samar da tsaron a matsayin daya daga cikin manyan ginshikan shirya zabe.

Daga nan kuma ya kara da cewa samar da tsaro na daga cikin abin da ke kara tabbatar da sahihanci da ingancin zabubbuka.

“Mafi yawan gyare-gyaren da aka yi wa shirye-shiryen zabe a hukumar INEC ya bambanta da abin da mu ka sani a baya. Don haka akwai matukar muhimmancin dukkan masu ruwa da tsaki a harkokin gudanar da zabe, musamman jami’an tsaro su gane kuma su fahimci wadannan matakai kuma a sanar da su sabbin abubuwan da aka bijiro da su.

ZABEN KOGI: INEC Ta Yunkura Domin Gano Inda Zaben Gwamna Zai Samu Barazana

Hukumar INEC ta umarci jami’an ta su gano duk wata hanya da za a iya kawo wa zaben gwamnan jihar Kogi da za a gudanar a ranar 16 Ga Nuwamba.
Za a gudanar da zaben a rana daya da na gwamnan jihar Bayelsa.

Kwamishinar INEC ta Kasa, Amina Zakari ce ta bada wannan umarnin a jiya Alhamis a Lokoja, babban birnain Jihar Kogi a lokacin da ta ke bude taron kwanaki biyu da aka shirya wa Jami’an Zabe da Mataimakan Jami’an Zabe da kuma wasu ma’aikata daga jiha da kuma hedikwatar hukumar zabe ta kasa.

Amina ta ce gano wannan barazana zai taimaka wajen kawar da ita tun yanzu da wuri, ba sai wuri ya kure ba.
Ta kara da cewa INEC ta dogara kacokan a kan jami’an ta da za su gudanar da aikin zaben, wajen samun nasarar gdanar da sahihin zabe.

Daga nan sai ta yi kira da su cewa su kasance sun samu masaniyar yadda al’amurra ke gudana a yankunan da za su yi aikin zabe.

Idan ba a manta ba, farkon wannan makon ne Hukumar INEC ta nuna fargabar samun barazana a zaben gwamnan jihar Kogi.

Kwamishinan Zabe na Jihar Kogi, Farfesa James Apam, a ranar Talata, 17 ga watan Satumba ya nuna damuwa akan yiwuwar barkewar rikici a lokacin zaben gwamna da za a yi a ranar 16 ga watan Nuwamba, a jihar.

Apam ya bayyana hakan ne a wajen wani taron masu ruwa da tsaki da aka yi a Lokoja. Ya bayyana cewa a karo da dama hukumar INEC ta shirya gudanar da zabe na gaskiya sannan kuma a koda yaushe tana daukar matakan da ya kamata don tabbatar da zabe na gaskiya da amana, kawai sai a zo a tarwatsa shi da rikici.

Kwamishinan zaben ya bayyana cewa hukumar na da niyyar gyara matsalolin da aka gane a zabukan da s**a gabata a zabe mai zuwa. Apam ya yi kira ya iyaye musamman mata da su taimaka wajen yi wa yaransu magana akan guje na rigima,

Ya kara da cewa idan har babu rikici, to mutane za su fito sosai a lokacin zabe sannan shirin zai kasance mai sauki. Kwamishinan zaben ya kuma bukaci masu zabe da su kimtsa kansu yadda ya kamata a lokacin zaben domin saukaka komai

Yadda EFCC Ta Kara Wa Zaben 2019 Inganci  -INECDaga WakilinmuCikin makon da ya gabata ne Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta Ta...
16/09/2019

Yadda EFCC Ta Kara Wa Zaben 2019 Inganci -INEC

Daga Wakilinmu

Cikin makon da ya gabata ne Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta Ta Kasa (INEC), ta jinjina wa irin rawar da Hukumar EFCC ta taka wajen kara wa zaben 2019 inganci.
Kwamishinan Zabe na Jihar Oyo ne, Mutiu Agboke ya yi wannan jinjinar a madadin INEC, a lokacin da ya kai wa EFCC ziyarar godiya a ofishin hukumar da ke Ibadan, babban birnin Jihar Oyo.

Ya ce EFCC ta taka rawa sosai wajen kkarin da ta yi a fannoni daban-daban a lokacin zaben 2019, musamman wajen hana sayen kuri’u da kuma sayar da su.
Agboke ya ce irin yadda jami’an EFCC s**a rika karakaina a lokacin zabe domin hana harkalla da sauran harkokin cuwa-cuwar zabe a ranar zabe, abin a yaba wa hukumar ce kwarai da gaske.

“EFCC ta kara wa zaben 2019 inganci ta yadda a daya gefen hukumar ta rika yaki da masu sayen kuri’u da kuma masu sayar wa. Sannan kuma ta rika dakile masu kokarin ganin sun yi amfani da kudi domin alkaluman zabe ya ba su rinjaye.
Daga nan sai ya ci gaba da bada labarin wasu hanyoyin da EFCC ta taka rawar gani a lokacin zaben, da ya ce sun hada da yadda jami’an hukumar s**a rika sa-ido a wajen tattara alkaluman kuri’u domin kada a yi murda-murda.

“Na lura hatta wajen tantance bambancin adadin yawan kuri’un da ke rata tsakanin ‘yan takara sai da EFCC ta taka rawa. Domin ko a gaba na an yi haka, ni shaida ne. Wannan kuwa baya ga aikin da ke kan hukumar, taimako ne gagarimi EFCC ta bai wa INEC. Saboda haka mu na matukar godiya.
Daga nan sai Agboke ya gode wa Shugaban EFCC, Ibrahim Magu bisa ga amincewar da ya yi domin yin aiki kafada-da-kafada da INEC saboda gudanar da aikin da ‘yan Najeriya za su yaba kuma su gamsu.

“Mu kuma dama a INEC an ba mu umarnin cewa mu yi aiki tare da dukkan hukumomi domin tabbatar da cewa mun gudanar da ingantaccen zabe, wanda zai samar da zaben da al’umma za su gamsu da shi.

Ya ce kuma ya na sane a matakin kasa Shugaban INEC, Mahmood Yakubu na aiki kafada-da-kafada da Shugaban EFCC, Ibrahim Magu.

A karshe ya ce a farkon shekara mai zuwa za a ci gaba da rajistar wadanda ba su yi rajistar zabe ba. Sannan kuma ya ce har yanzu akwai rajistar zabe ta mutane sama da 700,000 da har yanzu ba su je sun karbi abin su ba a jihar Oyo.

Shugaban EFCC Shiyyar Ibadan, Friday Ebelo, ya gode da ziyarar da kuma kwarin guiwar da aka kara musu. Ya ce a kullum ya na shaida wa jami’an sa cewa abu na farko shi ne su tabbatar sunan su bai baci ba, kuma ba su bata sunan kasar nan ba a yayin gudanar da aikin su a kan gaskiya.
Don haka ya ce kofa a bude ta ke domin taimaka wa INEC a ci gaba da tsaftace zabe da kara inganta shi a kasar nan.

SHARI'AR ZABEN 2019: Gaskiyar INEC Ta Kara Fitowa FiliDaga Bashir Shehu Na'ibawaGanin yadda hukuncin Kotun Daukaka Kara ...
15/09/2019

SHARI'AR ZABEN 2019: Gaskiyar INEC Ta Kara Fitowa Fili

Daga Bashir Shehu Na'ibawa

Ganin yadda hukuncin Kotun Daukaka Kara ya kasance, inda tun kafin a kai ga korar karar da PDP da dan takarar ta Atiku Abubakar su ka kai, sai da alkalan biyar su ka fara yin fatali da zargin da Atiku ya yi cewa wai INEC ta tattara bayanan sakamakon zaben 2019 a cikin rumbun na'urar tattara bayanai, wato 'SERVER'.

Alkalan dai dai sun ce Atiku da PDP sun kasa gabatar da kwararan hujjoji da za su gamsar da kotu.

Sannan kuma shaidar da s**a gabatar ya kasa kawo wata kwakkwarar hujja, sai kame-kamen neman nasara a kotu ido-rufe.

Alkalan sun gamsu da hujjar da INEC ta bayar cewa ba a yi amfani da 'SERVER' ba. Kuma duk kididdigar da Atiku da PDP s**a gabatar a kotu shaci-fadi ce da kuma bayanan kanzon-kurege na soshiyal midiya.

To, ba tun yau na na sha nuna cewa INEC ta yi kokari a zaben 2019. Yawanci inda aka samu 'yan matsaloli kuwa, ba laifin ta ba ne, laifin 'yan takara ne, ko magoya bayan su, ko jam'iyyar su ko 'yan bangar siyasar su ko kuma 'yan jagaliyar su.

Kai tsaye ina so na fara da tunatar da masu karatu irin kokarin da INEC ta yi, inda ta shafe shekaru biyu ta na nanata wa jama'a ka'idojin da ya kamata a kiyaye da kuma dokoki kafin zabe da kuma lokacin zabe.

Amma abin takaici, daga cikin wasu muhimman dokoki 30, 'yan siyasa da magoya bayan su sai da s**a karya kusan 28.

YADDA INEC TA YI ADALCI
Kun tuna cewa Shugaba Muhammadu Buhari ya sha kaye a zaben Sanata a Rumfar Zaben sa?

Kun tuna INEC ta hana jam'iyyar APC shiga zabe tun farko a Jihar Katsina?

Kun tuna INEC ta bi umarnin kotu ta hana APC shiga zabe a Jihar Rivers?

Kun tuna yadda 'yan jagaliyar siyasa s**a rika banka wa ofisoshin INEC wuta a fadin kasar nan?

Zaben 'inconclusive' da aka rika kuka a kan sa, a jihohi shida dai duk jam'iyyar adawa ce ta yi nasara. Wato Adamawa, Bauchi, Sokoto, Benue, Taraba da Rivers.

Shin INEC ba ta nuna bacin rai dangane da rawar da jami'an tsaro s**a taka a wasu wurare, musamman a Jihar Rivers ba?

Shin ba a yi wa INEC makarkashiya ba ne wajen kai hare-haren lalata kayan zabe?

Shin ba a rika bi ana banka wa ofisoshin INEC wuta ba, ana kone kayan zabe?

Shin INEC ba ta yi gargadin kada a yi wadannan laifukan ba ne?

WASU DOKOKIN ZABE DA AKA KARYA A 2019

1. Wanda ya yi rajista sau biyu.

2. Sojan-gona, wato yi wa ni rajista, ko yin rajista da sunan wani.

3. Tada hargitsi a lokacin kamfen.

4. Bayyana sakamakon zabe na bogi.

5. Kamfen a ranar zabe.

6. Saye ko sayar da kuri'a ko katin zabe.

7. Neman yin zabe a madadin wani.

8. Jefa kuri'a fiye da sau daya.

9. Hargitsa wurin da ake gudanar da jefa kuri'a.

10. Hana masu zabe yin zabe.

11. Fizgen akwatin zabe ko kayan zabe.

12. Lalata kayan zabe.

13. Aringizon kuri'u da rinton adadin kuri'un da aka jefa.

14. Cin zarafin jami'an zabe ko wasu masu ruwa-da-tsaki a harkar zabe.

15. Hana masu zabe hakkin su.

16. Lalata kayan zabe don kada a yi amfani da su wajen kafa hujja a kotun daukaka karar sakamakon zabe.

Saboda haka, jama'a da dama sun yarda da cewa, babu laifin INEC a yawancin wuraren da aka samu matsaloli a lokacin zabe ko lokacin kidayar kuri'u.

Address

Abuja
Maitama

Telephone

07060895772

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Allura Newspaper posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share