Malumfashi Post

Malumfashi Post Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Malumfashi Post, Newspaper, Malumfashi.

Malumfashi-Post, sabon shafin Jarida ne da aka kirkira dan tallata hajar yan, kasuwa yan,siyasa, ko tofa albarkacin baki, tare da kawo muku sabbin rahotanni na labaran duniya a cikin harshen Hausa kyauta, idan kun kasance masu yin Like & Follow din shafin

Ministan Tsaro Najeriya, Mohammed Badaru Abubakar, Ya Halarci Taron Horar Da Ƙwararrun Akanta Na Ƙasa (ANAN) a AbujaBabb...
13/02/2025

Ministan Tsaro Najeriya, Mohammed Badaru Abubakar, Ya Halarci Taron Horar Da Ƙwararrun Akanta Na Ƙasa (ANAN) a Abuja

Babban Ministan Tsaro na Najeriya, Mai Girma Mohammed Badaru Abubakar, CON, mni, ya halarci taron farko na horar da Ƙwararrun Akanta na Ƙasa (MCPD) na Ƙungiyar Ƙwararrun Akanta ta Najeriya (ANAN) a ranar Laraba, 12 ga Fabrairu, 2025, a babban birnin tarayya, Abuja.

A yayin taron, Ministan ya gabatar da saƙon gaisuwa ga mahalarta taron, inda ya jaddada mahimmancin ci gaban ƙwararrun aiki da kuma ƙarfafa ƙwararrun akanta na ƙasa don haɓaka ingantaccen gudanar da harkokin kuɗi a Najeriya. Ya kuma bayyana cewa gwamnatin tarayya ta ƙudura aniyar tallafawa duk wani shiri da zai haifar da ingantaccen gudanar da ayyukan gwamnati da kuma bunƙasa tattalin arzikin ƙasa.

Taron ya tattaro ƙwararrun akanta daga sassa daban-daban na ƙasar domin yin tarurruka da tattaunawa kan sabbin hanyoyin da za a bi don inganta aikin akanta da kuma dacewa da ka'idojin ƙasa da ƙasa.

Mai Girma Ministan Tsaron Najeriya Mohammed Badaru Abubakar, CON, mni, ya karɓi baƙuncin Shugaban Kungiyar Masanan Lissa...
12/02/2025

Mai Girma Ministan Tsaron Najeriya Mohammed Badaru Abubakar, CON, mni, ya karɓi baƙuncin Shugaban Kungiyar Masanan Lissafin Kudi ta Najeriya (ANAN), Dr. James Ekerare Neminebor, tare da wasu manyan shugabanni, a ofishinsa a ranar Talata, 11 ga Fabrairu, 2025.

A yayin wannan ziyara, Dr. Neminebor ya tattauna da Minista kan hanyoyin haɗin gwiwa don ci gaban fannin kudi a faɗin Najeriya.

Ministan Tsaro Ya Jagoranci Jiga-Jigan Jam'iyyar APC Na Jihar Jigawa Zuwa Ɗaurin Auren 'Yar Tsohon Kakakin Majalisar Jih...
08/02/2025

Ministan Tsaro Ya Jagoranci Jiga-Jigan Jam'iyyar APC Na Jihar Jigawa Zuwa Ɗaurin Auren 'Yar Tsohon Kakakin Majalisar Jihar

Mai girma Ministan Tsaro na Nigeriya HE Mohammed Badaru Abubakar CON, mni ya jagoranci dukkanin masu ruwa da tsaki na Jam,iyyar APC na Jihar Jigawa da sauran Mukarraban Gwamnatin Jigawa zuwa wajen Daurin auren diyar tsohon kakakin Majalisar Dokokin Jihar, Alh. Idris Garba Jahun wanda aka daura auren a ranar asabar-8-ga wannan wata na Fabarairu a Babban masallacin Juma,a na garin Jahun.

Mai girma Ministan ya sami tarya ta musanman daga Mataimakin Gwamnan Jihar Jigawa, Alh. Aminu Usman Gumel a madadin Gwamnan Jiha, Mallam Umar A Namadi fca, sauran wanda s**a rufa masa baya sun hada da Sakataren Gwamnatin Jiha Mallam Bala Ibrahim da Shugaban Ma,aikatan a Fadar Gwamnatin Jiha Alh. Mustafa Makama da Yan Majalisar zartarwa dana Dokoki na Jihar Jigawa, da Yan Majalisar Tarayya da sauran mukarraban Gwamnatin Jiha.

Haka zalika mai girma Ministan ya sami rakiyar, Shugaban Jam'iyyar APC na Jiha Alh. Aminu Sani Gumel, da Ma,ajin Jam, iyyar APC na Kasa Alh. Basheer Usman Gumel, da Jigo a Jam,iyyar APC na Jiha Alh. Isah Gerawa, da Darakta Janar na yakin neman zaben APC a shekarar 2025 Alh.Lawan Ya,u Roni da Alh. Ubale Hashim da Tsafaffin Shugabanin Kananan Hukumomin Jihar da sauran dubban magoyabayan Jam, iyyar APC.

Mati Ali.
PA Media & Publicity to the Hon. Minister of Defence

07/02/2025

Zarge-zargen Naja'atu Muhammad akan Nuhu Ribadu cike suke da rashin makama.

07/02/2025

Fitaccen ɗan gwagwarmaya Comr Hamza Saulawa ya caccaki Naja'atu Muhammad kan zarge-zargen da ta yi ga Malam Nuhu Ribadu

07/02/2025

Dole ki fito ki kawo hujjoji masu karfi ko ki fuskanci hukunci a kotu ~ Kiran shugaban hukumar wayar da kai kan cin hanci da rashawa ga Naja'atu Muhammad

Ku Haɗa Kai Ku Yaƙi Matsalolin Tsaro A Najeriya ~ Umarnin Shugaba Tinubu Ga Rundunonin TsaroShugaban kasa Bola Ahmed Tin...
06/02/2025

Ku Haɗa Kai Ku Yaƙi Matsalolin Tsaro A Najeriya ~ Umarnin Shugaba Tinubu Ga Rundunonin Tsaro

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci rundunonin sojoji, hukumomin tsaro da na leeken asiri su hada kai wajen yakar kalubalen tsaro da ke kunno kai a Najeriya.

Shugaban kasar, wanda Ministan Tsaro Mohammed Badaru Abubakar CON, mni ya wakilta a taron kwamandojin rundunar hadin gwiwa da aka gudanar a Abuja, ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa da amfani da sabbin fasahohi wajen inganta tsaro.

Ya yabawa sojojin Najeriya bisa jajircewarsu wajen kare kasa tare da tabbatar da cewa gwamnatinsa na ba su cikakken goyon baya.

Mati Ali
Mai Taimaka wa Ministan Tsaro Kan Harkokin Yada Labarai

MATSALAR TSARO A MALUMFASHIYau  Kimanin Wata Ɗaya Kenan Kusan Kullum Sai Ƴan ta'adda Sunci Karen,su Ba Babbaka A Ƙaramar...
05/02/2025

MATSALAR TSARO A MALUMFASHI

Yau Kimanin Wata Ɗaya Kenan Kusan Kullum Sai Ƴan ta'adda Sunci Karen,su Ba Babbaka A Ƙaramar Hukumar Malumfashi Dake Jihar Katsina.

Koda yanzu ban fiye yawan zama a cikin yankin gari na ba ƙaramar hukumar Malumfashi dake jihar Katsina amman ina bibiyar lamarin dake gudana acikin garin, kuma ina takaicin samun rahotannin yanda ƴan ta'adda ke yawaita kai hare-harekullum babu dare babu rana a yankunan dake cikin karamar hukumar ta Malumfashi.

A wannan rubutu saƙon da ni Kamalancy nake son isarwa zuwa ga gomnatin tarayya shine tasan cewar fa maganar gaskiya wannan aikin na yaƙin ƙawar da waɗan nan miyagun mutane a doran ƙasa ba ƙaramin aiki bane da zata zurawa mutanan gari ido, ko ace za'a barmu da ƙoƙarin gommatin jiha kadai bare na ƙaramar hukuma.

Domin matsalar ta munana tayanda dole saida ƙoƙari da taimakon gomnatin tarayya, tunda itace ke da iko da mallaki ga jiragen yaki da hafsanonin tsaro, amman Malumfashi bamu taba ganin ko da Helkoftan yaƙi ɗaya yazo nan kawo ɗauki ba, ya kamata muga ƙoƙarin ta a zahirance indai har daman da gaske take wajen ƙoƙarin ta na yaki da wadan nan miyagun mutane a cikin al,ummah.

Jami'an tsaron ƙasar mu Nigeria mun san nagarta da ingancin su a fannin yaƙi, suna da kwarewa ta nunawa da duk duniya tana alfahari dasu, dan haka muna kyautata zaton zasu iya aikin kawar da waɗan,nan tsirarun ƴan ta'adda cikin dan lokaci ƙalilan a duk inda suke indai gomnati ta basu dama da kayan aikin yin hakan da gasken gaske.

Bayaga harin da s**a kai gidan shugaban ƙaramar hukumar garin, Harin da har s**a kashe ɗaya acikin ƴan sanda masu tsaron gidan kuma s**a tafi da ƙaramin ɗan sa ɗaya, a daren Litinin ɗin nan ma sun kuma ƙara shiga Hayin gada Unguwar dake kusan cikin gari, nanma sun kwashi mutane duk da an nasarar ceto wasu, amma har yanzu akwai wasu nacen tsare a hannayen su.

Akwai kuma wani gari Unguwar Kire, da shima duk yana a ƙarkashin ƙaramar hukumar ta Malumfashi ƴan ta'addan sun kai harere har sau 4 cikin sati ɗaya, amma harin da yan ta'addan s**a kai na ranar Litinin, yafi muni sosai, sbd ƴan ta'addar sunbi har gida gida a garin suna karbe kudade mashina da wayoyi tare da kore kimanin dabbobi guda Dari ukku da hamsin.

Sannan a jiya Talata ma da safe sun kuma sake komawa garin sunyi garkuwa da mutum shidda tare da kore awaki da zasu iya kaiwa akalla 150 zuwa 200, da daddare kuma s**aje garin Marabar Ƙanƙara, nanma s**a kashe wani mutum daya kuma sauka tafi da direban motar, duk a jiyan.

Yanzu haka dai Al'ummar garin na Kire, na ta kwashe kayayyakin su wasu kuma na nan sun fito mata da maza hadi da ƙananan yara ɗauke da kayayyakin nasu sun tsaya zube a bakin t**i
tare da dan abinda ya rage masu na dukiyar su, suna shirin barin garin dan su samu su tsira da rayukansu, koda basu san inda zasu dosa ba.

Haka ma a rahotan,nin da nake yawan samu yankin Malumfashi ta gabas musamman garin Na'alma nan ma waɗan nan ƴan ta'addan kusan kullum suna fitowa kai musu hare-hare dan ko a cikin satin nan da muke ciki al,ummar garin sunce daren jiya ne kaɗai basu jiyo ɗuriyar fitowar su ba.

Cikin hare-haren da suke kaiwa yankin akwai harin da s**a kaiwa garin daren lahadin nan da ta gabata misalin karfe 11:30 Pm duk da dai daga ƙarshe mutanan gari sun samu taimakon C-W wajen korar ƴan ta'addan, amma harin ya munana, sbd sun kashe mutum ɗaya kuma sun tafi da matan aure 2 da wataƙ ƙaramar yarinya ɗaya yar shekara 9.

A ƙarshe ina mai kara yin kira da rogo gommatin da hukumomin tsaro da su taimakawa rayuwar al,ummar da ke a ƙarƙashin kulawar su, dan Allah su kara zage damtsin ƙoƙari da tashi tsaye sosai akan wanda s**ai, dan ganin an kawo ƙarshen waɗan,nan azzaluman mutane a cikin Al,ummah.

Allah ubangiji ya dawo mana da zaman lafiya dawwamamme yankin gari na, na Malumfashi da jiha ta Katsina da dukka Arewa har dama ƙasar mu Najeriya baki ɗaya da bamu da inda ya fita.

Daga| It'z Kamalancy
05| Feb| 2025

Masu rajin haɗa maja don kada APC na yin hakan ne don ba su samu muƙami ba - Masari Aminu Masari, tsohon gwamnan jihar K...
03/02/2025

Masu rajin haɗa maja don kada APC na yin hakan ne don ba su samu muƙami ba - Masari

Aminu Masari, tsohon gwamnan jihar Katsina, ya ce babu wata madafa a Nijeriya sama da jam’iyyar APC.

Masari ya yi wannan jawabi ne a jiya Lahadi a garin Kafur, karamar hukumar Kafur ta Katsina, yayin kaddamar da yakin neman zaben ƙananan hukumomi da aka shirya gudanarwa a ranar 15 ga watan Fabrairu.

Tsohon gwamnan ya yi watsi da labarin ‘yan siyasa masu shirin kafa jam'iyyar maja domin kawar da jam’iyyar APC mai mulki, yana mai bayyana hakan a matsayin gungun wasu fusatattu da su ka rasa muƙamai a cikin jam’iyyar.

“Labarin da ake yadawa a kafafen sada zumunta na zamani cewa wasu ‘yan siyasa na nan na hada kai don kafa maja ba komai ba ne illa taron wasu fusatattu da su ka rasa muƙamai a jam’iyyar APC,” in ji Masari.

"Yunkurin nasu na kulla kawance ba zai kawar da hankalin APC daga tunani aiwatar da ayyukan ci gaba da za su rage radadin talaka ba,".

Masari ya ce a matsayinsa na wanda da shi aka kafa jam’iyyar APC, zai ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da manufofin jam’iyyar.

Ɓarnar Kuɗin Jihar Kano Ne Wawure Naira Biliyan 2.5 Don Aurar Da ZawarawaGwamnatin Kano ta sake nuna fifikon akan abinda...
02/02/2025

Ɓarnar Kuɗin Jihar Kano Ne Wawure Naira Biliyan 2.5 Don Aurar Da Zawarawa

Gwamnatin Kano ta sake nuna fifikon akan abinda ba shi da amfani ga ci gaban al'umma, inda ta ware naira biliyan 2.5 domin gudanar da auren zawarawa a shekarar 2025. A yayin da wasu jihohi kamar Lagos ke amfani da biliyan 3.5 domin inganta wutar lantarki, wanda hakan zai kawo ci gaba a bangarori da dama na tattalin arziki da walwalar jama’a a jihar.

Shin aurar da zawarawa da kimanin kudi biliyan 2.5 shi ne mafi muhimmanci a lokacin da al’umma ke fama da matsalolin rashin aikin yi, karancin ruwan sha, lalacewar hanyoyi, da kuma matsalolin ilimi? Me yasa gwamnati za ta zuba irin wannan kudi kan abu da ba zai samar da dogon tasiri ga ci gaban jihar ba?

Gwamnatin da ke da ikon magance matsalolin tattalin arziki, samar da ayyukan yi, da inganta rayuwar al'umma, sai ta fi dacewa ta mayar da hankali kan abubuwan da za su inganta rayuwar kowa da kowa, ba wai yin fashin kudi kan abubuwan da za su kare nan da nan ba.

Lagos na kokarin inganta wutar lantarki domin bunkasa masana'antu da kasuwanci, Kano kuma na kokarin aurar da zawarawa da makudan kudi. Wannan ba komai ba ne illa nuna rashin fifita ci gaba da dogon tunani a ɓangaren jagoranci.

Kano na bukatar shugabanci mai cike da hangen nesa, ba wai mai auren zawarawa da biliyoyi ba.

Wike Rusa Gwamnatin Tinibu Yake Ba Taimakonta Ba, Domin Mayaudari Ne ~ Martanin Gwamnatin Bauchi.... Ministan babban bir...
29/01/2025

Wike Rusa Gwamnatin Tinibu Yake Ba Taimakonta Ba, Domin Mayaudari Ne ~ Martanin Gwamnatin Bauchi
.... Ministan babban birnin tarayya Abuja Nyesom Wike ya sha kakkausar s**a daga gwamnatin jihar Bauchi kan salonsa na yaudara da cin amana, wanda gwamnatin Jihar Bauchi ta kira Wike da mutumin da ya rasa amincinsa a cikin al'umma saboda halin rashin tsayayyen manufa da rashin tabbas da yake da ita a siyasar Najeriya

Fagen siyasar Najeriya yana cike da hadin kai na wucin gadi da rikice-rikicen siyasa. Sabbin zarge-zarge da Ministan Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya yi wa Gwamnan Bauchi, Bala Mohammed, wanda kuma shi ne shugaban kungiyar gwamnonin PDP, sun kara bayyana wannan hali na rudani. Duk da cewa zarge-zargen Wike suna bukatar a bincika su sosai, zurfafa bincike da dubawa ya nuna wani tsari na rashin karko da neman riba wanda ya raunana amincinsa kuma zai iya kawo illa ga gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Zarge-zargen Wike kan Bala Mohammed sun ta’allaka ne kan gazawar PDP da zargin rashin biyayya. Sai dai tsananin zarge-zargen nasa ya zarce hujjojin da ya gabatar, yana haifar da tambayoyi game da dalilansa na asali. Tarihin Wike ya nuna cewa yana fifita moriyarsa sama da biyayya da tsayayyen ra’ayi. Wannan hali ya raunana amincinsa, musamman idan aka yi la’akari da tarihi mai rubuce da ya nuna wannan dabi’a.

Misalan Rashin Aminci na Wike

1. Rikicinsa da Rotimi Amaechi: Dangantakarsu da Rotimi Amaechi, tsohon abokinsa ne na siyasa, ta lalace zuwa rigima mai tsanani. Wannan ya nuna yadda Wike ke watsar da tsofaffin abokansa na siyasa idan ya ga zai samu riba daga wani bangare.

2. Sauyawa a PDP: Wike ya canza daga kasancewa mai biyayya ga PDP zuwa wata rukuni mai s**ar shugabannin jam’iyyar, yana kafa kawance da lalata su cikin rashin tsayayyen manufa irin na shi.

Halin Neman Moriyar Kai

Ayyukan Wike suna nuna cewa burinsa ya ta’allaka ne kan samun riba ta kansa, ba don kishin jam’iyya ba ko ra’ayoyin siyasa. Samun mukamin Ministan FCT duk da cewa ya rika s**ar APC yana nuna yadda yake amfani da damar siyasa don amfaninsa. Wannan ya yi karo da s**ar da yake yi wa wasu game da rashin biyayya.

Wike ya sha sauya ra’ayinsa da yin magana da ke saba wa matsayinsa na baya, yana bin abin da zai kawo masa riba. Wannan rashin daidaito yana sanya wahalar yanke hukunci game da gaskiyar zarge-zargensa. Tambaya ita ce: Wike yana damuwa da makomar PDP ne ko yana son amfani da wannan lokacin don karfafa matsayinsa? Wannan rashin tabbas yana haifar da shakku sosai.

Bambancisa Da Bala Mohammed

A gefe guda, Bala Mohammed ya kasance mai karko a tafiyarsa ta siyasa, yana rike da dangantaka mai kyau da PDP da kuma abokan siyasa. Wannan karko da tsayayyen tsari sun bambanta shi da Wike, wanda yake yawan sauya matsaya.

Tasirin Halin Wike Kan Gwamnatin Tinubu

Halin Wike na rashin karko da yawan rikici zai iya kawo baraka a cikin gwamnatin Tinubu. Yawan zarge-zargensa marasa tushe da shiga rigingimu a bainar jama’a na iya rage ingancin gwamnati da dagula aikinta. Wannan hali zai iya kawar da hankalin gwamnati daga manyan ayyukanta kuma ya lalata martabarta a idon jama’a.

Kammalawa

Zarge-zargen Wike kan Bala Mohammed ya kamata a duba su tare da tarihin Wike na rashin karko da neman riba. Rashin daidaito da rashin biyayya ga tsari sun raunana amincinsa da hujjojin zarge-zargensa. Halinsa ya nuna cewa burin kansa yana fin kowanne abu muhimmanci a gare shi, fiye da kishin jam’iyya ko ra’ayin siyasa. Don haka, dole ne a yi taka-tsantsan kan duk wani magana daga gare shi har sai ya nuna tsayayyen biyayya ga tsari da ka’ida. Wannan bambanci da Bala Mohammed ya bayyana muhimmancin karko da tsayayyen shugabanci, musamman ga sabuwar gwamnati da ke kokarin cimma nasara.

INNAHLILLAHI WAINNAH ILAIHIR RAJI,UN !!!Daren jiya wasu ƴan ta'adda sun kai hari gidan shugaban karamar hukumar Malumfas...
28/01/2025

INNAHLILLAHI WAINNAH ILAIHIR RAJI,UN !!!

Daren jiya wasu ƴan ta'adda sun kai hari gidan shugaban karamar hukumar Malumfashi, harin da yay sanadiyyar rasa ran daya daga cikin jami ai masu tsaron gidan mai suna CPL Shamsu Lawal.

Karamar hukumar Malumfashi dake jihar Katsina, na fuskantar matsanancin matsala ta rashin tsaro musamman a wannan lokutan da kusan kullun sai anjiyo ɗuriyar ƴan ta'adda sun shiga wani yanki acikin yankuna dake ƙaramar hukumar garin.

Muna masu addu,a da rokon Allah ubangiji ya karbi shahadar Shamsu Lawal, tare da duk sauran musulmi, Allah ya kawo mana karshen matsalar tsaro a jihar Katsina dama Arewa baki ɗaya.

Daga| Kamalancy
28| Jan| 2025

22/01/2025

Qur'anic Festival; Wazirin Katsina yayi kira na musamman ga malamai akan wannan taron.

Idan kuka ce dole sai kun yi Qur'anic Festival, to tarihi zai iya maimaita kansa ~ Farfesa Sani Lugga Wazirin Katsina

Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya Ɓanagaren Mata Reshan Jihar Kano (CNG-WOMENS WING) Ta Yi Watsi Da Sabuwar Dokar Gy...
21/01/2025

Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya Ɓanagaren Mata Reshan Jihar Kano (CNG-WOMENS WING) Ta Yi Watsi Da Sabuwar Dokar Gyaran Haraji

Daga Comr Haidar H Hasheem

Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya (CNG) reshen mata ta gudanar da wani babban taro a jiya a birnin Kano, wanda ya maida hankali kan batutuwan da s**a shafi mata, shugabanci, da tasirin dokar gyaran haraji da ake shirin zartarwa a Najeriya. Taron ya samu halartar fitattun masu magana, ciki har da Shugaban Kwamitin Amintattu na CNG, Dakta Nastura Ashir Shariff, da kuma wasu mataimakiya ta musamman kan harkokin mata ga Gwamnan Jihar Kano Haj. Fatima tare da fitaccen Malamin Addini na Kano Sheikh Ibrahim Khalil.

Kin Amincewa da Sabuwar Dokar Gyaran Haraji
Ƙungiyar matan ta bayyana rashin amincewarta da sabuwar dokar gyaran haraji, tana mai jaddada cewa dokar na da tasirin da zai iya shafar gajiyayyu, musamman mata da yara. A cikin wata sanarwa da aka fitar bayan taron, mahalarta sun yi kira ga gwamnati da ta tabbatar da tattaunawa mai fadi kafin ta zartar da wannan doka.

Sanarwar ta bayyana cewa gyaran harajin ya rasa adalci da la’akari da yanayin tattalin arziki na yankuna daban-daban a Najeriya. Hakan ya sa s**a nemi a haɗa kungiyoyin al’umma, makarantu, da kananan hukumomi a cikin shawarwarin, domin tabbatar da tsarin da zai dace da kowa.

Tasirin Tattalin Arziki Ga Mata da Iyali
Mahalarta taron sun nuna damuwa kan yadda wannan doka za ta iya jefa nauyin haraji kan talakawa, musamman a irin wannan lokaci da ‘yan Najeriya ke fuskantar tasirin cire tallafi, hauhawar farashin kayayyaki, da darajar Naira.

Kungiyar ta jaddada cewa mata, wadanda ke matsayin kula da iyali da kuma masu tasiri a bangaren kasuwanci na ƙananan hukumomi, za su fuskanci mafi tsananin tasirin wannan gyara. Hakan zai iya rage musu damar samun ababen more rayuwa da kuma hana su samun ‘yancin tattalin arziki.

Masu jawabi sun jaddada muhimmancin samun shugabanci mai adalci da kuma tsarin tattalin arziki wanda zai amfani kowa. Sun gargadi cewa rashin tsarin da zai dace zai iya janyo rashin gamsuwa daga jama’a, tare da haifar da matsalolin zamantakewa. Tarihin Najeriya ya nuna cewa duk wani tsarin tattalin arziki mai wuyar karɓuwa yakan janyo rashin zaman lafiya da ci gaba a al’umma.

Karfafa Gwiwar Hukumomin Ci Gaba
Kungiyar ta kuma yi kira ga gwamnati da ta ci gaba da tallafawa hukumomi kamar TETFUND, NITDA, da NASENI, waɗanda ke taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa ilimi, fasaha, da masana’antu. Sun bayyana cewa bai kamata a rage kasafin kudinsu ko sauya musu fasali ba, maimakon haka, a ƙara musu ƙarfi domin su magance manyan kalubale a fannin bincike, kirkire-kirkire, da karfafa fasaha.

Kiran Gaggawa Ga Gwamnati

Taron ya ƙare da kira mai ƙarfi ga gwamnati da ta yi amfani da hanyoyi masu sauƙi da adalci wajen tsara manufofin tattalin arziki. Shugabannin mata sun tabbatar da jajircewarsu wajen ganin an samar da dokoki masu sauƙi kula da adalci, daidaito, da ci gaban mata da sauran marasa galihu a kasa.

Gamayyar kungiyoyin Arewacin Najeriya bangaren mata ta CNG ta nuna muhimmancin rawar da mata ke takawa wajen tsara al’amuran tattalin arziki da zamantakewa a Najeriya, tare da yin kira ga kowa da kowa ya taka rawa wajen gina ƙasa mai cike da adalci da ci gaba.

Innahlillahi Wainnah ilaihir'raji'un😭Daren jiya ƴan ta'adda masu garkuwa da mutane sun shiga garin Marabar Ƙanƙara, dake...
20/01/2025

Innahlillahi Wainnah ilaihir'raji'un😭

Daren jiya ƴan ta'adda masu garkuwa da mutane sun shiga garin Marabar Ƙanƙara, dake ƙaramar hukumar Malumfashi jihar Katsina.

A rahotan dana samu ƴan ta'addan sun kashe mutum biyu sannan kuma sun dauki mutane da har yanzun ba a kaiga tantance adadinsu ba

Amma dai kawo iyanzu wannan matashi da na sa muku Hotan,sa ƙasa mai suna Usman da'u shine kaɗai ake da tabbacin sun ɗauka.

Muna masu kara yin addu,a da rokon Ubangiji Allah shi kawo mana karshen wannan iftila'i

Daga| It'z Kamalancy
20| Jan| 2025

Address

Malumfashi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Malumfashi Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category