
19/09/2025
DWI Ta Yi Allah-wadai da Zarge-zargen Banza Marasa Tushe Na Abubakar Malami Kan ’Yan Majalisar Jihar Kebbi
Kungiyar Democracy Watch Initiative (DWI) ta bayyana takaici da ƙin amincewa da ƙorafin da tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami (SAN), ya shigar a kan ’yan majalisar jihar Kebbi da ke kira da a k**a shi tare da gurfanar da shi gaban doka.
A cewar kungiyar, zarge-zargen Malami cewa Gwamna Nasir Idris da shugabannin jam’iyyar APC suna shirin shigo da ’yan daba da mak**ai cikin jihar, ba su da tushe kuma manufarsu kawai ita ce tada hankalin jama’a da kawo fitina.
Kungiyar ta kuma yi nuni da cewa Malami da kansa ana zarginsa da shigo da ’yan daba daga jihohin makwabta, abin da ya haddasa rikici a Birnin Kebbi da kai hari ga ofishin APC na jihar. Wannan, a cewar DWI, ya nuna cewa maimakon ya zama mutum mai kare doka da adalci, Malami ya zamo wanda ke yada fitina da kawo rikici.
DWI ta yi kira da gaggawa ga hukumomin tsaro da Majalisar Ɗinkin Tarayya da su k**a Malami tare da gurfanar da shi domin kare zaman lafiya da mutuncin dimokuraɗiyya.
Kungiyar ta kammala da tabbatar da goyon bayanta ga ’yan majalisar Kebbi da al’ummar jihar wajen neman adalci da tabbatar da siyasa mai lumana da gaskiya.