05/02/2025
MATSALAR TSARO A MALUMFASHI
Yau Kimanin Wata Ɗaya Kenan Kusan Kullum Sai Ƴan ta'adda Sunci Karen,su Ba Babbaka A Ƙaramar Hukumar Malumfashi Dake Jihar Katsina.
Koda yanzu ban fiye yawan zama a cikin yankin gari na ba ƙaramar hukumar Malumfashi dake jihar Katsina amman ina bibiyar lamarin dake gudana acikin garin, kuma ina takaicin samun rahotannin yanda ƴan ta'adda ke yawaita kai hare-harekullum babu dare babu rana a yankunan dake cikin karamar hukumar ta Malumfashi.
A wannan rubutu saƙon da ni Kamalancy nake son isarwa zuwa ga gomnatin tarayya shine tasan cewar fa maganar gaskiya wannan aikin na yaƙin ƙawar da waɗan nan miyagun mutane a doran ƙasa ba ƙaramin aiki bane da zata zurawa mutanan gari ido, ko ace za'a barmu da ƙoƙarin gommatin jiha kadai bare na ƙaramar hukuma.
Domin matsalar ta munana tayanda dole saida ƙoƙari da taimakon gomnatin tarayya, tunda itace ke da iko da mallaki ga jiragen yaki da hafsanonin tsaro, amman Malumfashi bamu taba ganin ko da Helkoftan yaƙi ɗaya yazo nan kawo ɗauki ba, ya kamata muga ƙoƙarin ta a zahirance indai har daman da gaske take wajen ƙoƙarin ta na yaki da wadan nan miyagun mutane a cikin al,ummah.
Jami'an tsaron ƙasar mu Nigeria mun san nagarta da ingancin su a fannin yaƙi, suna da kwarewa ta nunawa da duk duniya tana alfahari dasu, dan haka muna kyautata zaton zasu iya aikin kawar da waɗan,nan tsirarun ƴan ta'adda cikin dan lokaci ƙalilan a duk inda suke indai gomnati ta basu dama da kayan aikin yin hakan da gasken gaske.
Bayaga harin da s**a kai gidan shugaban ƙaramar hukumar garin, Harin da har s**a kashe ɗaya acikin ƴan sanda masu tsaron gidan kuma s**a tafi da ƙaramin ɗan sa ɗaya, a daren Litinin ɗin nan ma sun kuma ƙara shiga Hayin gada Unguwar dake kusan cikin gari, nanma sun kwashi mutane duk da an nasarar ceto wasu, amma har yanzu akwai wasu nacen tsare a hannayen su.
Akwai kuma wani gari Unguwar Kire, da shima duk yana a ƙarkashin ƙaramar hukumar ta Malumfashi ƴan ta'addan sun kai harere har sau 4 cikin sati ɗaya, amma harin da yan ta'addan s**a kai na ranar Litinin, yafi muni sosai, sbd ƴan ta'addar sunbi har gida gida a garin suna karbe kudade mashina da wayoyi tare da kore kimanin dabbobi guda Dari ukku da hamsin.
Sannan a jiya Talata ma da safe sun kuma sake komawa garin sunyi garkuwa da mutum shidda tare da kore awaki da zasu iya kaiwa akalla 150 zuwa 200, da daddare kuma s**aje garin Marabar Ƙanƙara, nanma s**a kashe wani mutum daya kuma sauka tafi da direban motar, duk a jiyan.
Yanzu haka dai Al'ummar garin na Kire, na ta kwashe kayayyakin su wasu kuma na nan sun fito mata da maza hadi da ƙananan yara ɗauke da kayayyakin nasu sun tsaya zube a bakin t**i
tare da dan abinda ya rage masu na dukiyar su, suna shirin barin garin dan su samu su tsira da rayukansu, koda basu san inda zasu dosa ba.
Haka ma a rahotan,nin da nake yawan samu yankin Malumfashi ta gabas musamman garin Na'alma nan ma waɗan nan ƴan ta'addan kusan kullum suna fitowa kai musu hare-hare dan ko a cikin satin nan da muke ciki al,ummar garin sunce daren jiya ne kaɗai basu jiyo ɗuriyar fitowar su ba.
Cikin hare-haren da suke kaiwa yankin akwai harin da s**a kaiwa garin daren lahadin nan da ta gabata misalin karfe 11:30 Pm duk da dai daga ƙarshe mutanan gari sun samu taimakon C-W wajen korar ƴan ta'addan, amma harin ya munana, sbd sun kashe mutum ɗaya kuma sun tafi da matan aure 2 da wataƙ ƙaramar yarinya ɗaya yar shekara 9.
A ƙarshe ina mai kara yin kira da rogo gommatin da hukumomin tsaro da su taimakawa rayuwar al,ummar da ke a ƙarƙashin kulawar su, dan Allah su kara zage damtsin ƙoƙari da tashi tsaye sosai akan wanda s**ai, dan ganin an kawo ƙarshen waɗan,nan azzaluman mutane a cikin Al,ummah.
Allah ubangiji ya dawo mana da zaman lafiya dawwamamme yankin gari na, na Malumfashi da jiha ta Katsina da dukka Arewa har dama ƙasar mu Najeriya baki ɗaya da bamu da inda ya fita.
Daga| It'z Kamalancy
05| Feb| 2025