Malumfashi Post

Malumfashi Post Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Malumfashi Post, Newspaper, Malumfashi.

Malumfashi-Post, sabon shafin Jarida ne da aka kirkira dan tallata hajar yan, kasuwa yan,siyasa, ko tofa albarkacin baki, tare da kawo muku sabbin rahotanni na labaran duniya a cikin harshen Hausa kyauta, idan kun kasance masu yin Like & Follow din shafin

DWI Ta Yi Allah-wadai da Zarge-zargen Banza Marasa Tushe Na Abubakar Malami Kan ’Yan Majalisar Jihar KebbiKungiyar Democ...
19/09/2025

DWI Ta Yi Allah-wadai da Zarge-zargen Banza Marasa Tushe Na Abubakar Malami Kan ’Yan Majalisar Jihar Kebbi

Kungiyar Democracy Watch Initiative (DWI) ta bayyana takaici da ƙin amincewa da ƙorafin da tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami (SAN), ya shigar a kan ’yan majalisar jihar Kebbi da ke kira da a k**a shi tare da gurfanar da shi gaban doka.

A cewar kungiyar, zarge-zargen Malami cewa Gwamna Nasir Idris da shugabannin jam’iyyar APC suna shirin shigo da ’yan daba da mak**ai cikin jihar, ba su da tushe kuma manufarsu kawai ita ce tada hankalin jama’a da kawo fitina.

Kungiyar ta kuma yi nuni da cewa Malami da kansa ana zarginsa da shigo da ’yan daba daga jihohin makwabta, abin da ya haddasa rikici a Birnin Kebbi da kai hari ga ofishin APC na jihar. Wannan, a cewar DWI, ya nuna cewa maimakon ya zama mutum mai kare doka da adalci, Malami ya zamo wanda ke yada fitina da kawo rikici.

DWI ta yi kira da gaggawa ga hukumomin tsaro da Majalisar Ɗinkin Tarayya da su k**a Malami tare da gurfanar da shi domin kare zaman lafiya da mutuncin dimokuraɗiyya.

Kungiyar ta kammala da tabbatar da goyon bayanta ga ’yan majalisar Kebbi da al’ummar jihar wajen neman adalci da tabbatar da siyasa mai lumana da gaskiya.

Kisan Hakimin Dogon Daji A Zamfara Barazana Ce Ga Tsaron Ƙasa – In Ji Shugaban Arewa Media Writer’s, Comr. Haidar H. Has...
18/09/2025

Kisan Hakimin Dogon Daji A Zamfara Barazana Ce Ga Tsaron Ƙasa – In Ji Shugaban Arewa Media Writer’s, Comr. Haidar H. Hasheem

Shugaban ƙungiyar Arewa Media Writer’s, na ƙasa ya bayyana matuƙar takaici da bacin rai kan kisan gilla da ‘yan bindiga s**a yi wa Hakimin Dogon Daji a ƙaramar hukumar Tsafe ta jihar Zamfara, inda s**a yi masa yankan rago har lahira. Wannan lamari abin kunya ne ga ƙasa baki ɗaya kuma babban ƙalubale ne ga gwamnati da hukumomin tsaro k**ar yadda rahotan BBC Hausa da Leadership s**a kawo rahotan.

Wannan mummunan hari ya sake tabbatar da cewa lamarin tsaro a Arewacin Najeriya na ta ƙara tabarbarewa, inda ake ci gaba da kai hare-hare a ƙauyuka, sace jama’a, kona gidaje da gonaki, tare da hallaka shugabannin al’umma ba tare da tsoro ba. Wannan yanayi ya jefa dubban mutane cikin fargaba, gudun hijira, da rasa amincewa ga gwamnati.

Ya k**ata gwamnati ta gane cewa tsaro ba abu ne da za a siyasantar da shi ba. Tsaro shi ne ginshiƙin kowace al’umma, kuma kariya ga rayuka da dukiyoyi wajibi ne na gwamnati. Rashin ɗaukar mataki mai tsauri na iya ƙara dagula rayuwar jama’a da kuma barazana ga makomar ƙasa baki ɗaya.

A wannan yanayi, muna kira da:

1. Gwamnati ta tashi tsaye da gaggawa wajen murkushe ‘yan bindiga da duk wata ƙungiya ta ta’addanci a Arewa.

2. A samar da kayan aiki na zamani ga jami’an tsaro, tare da horo da ƙarfafawa domin su iya gudanar da ayyukansu yadda ya k**ata.

3. A shimfiɗa tsare-tsare na dindindin don tabbatar da tsaro a ƙauyuka da birane.

A madadin al’ummar Arewa da ƙungiyar Arewa Media Writer’s, ina kira da a ɗauki wannan kisan da aka yi wa hakimin Dogon Daji a matsayin kira na musamman ga shugabanni a dukkan matakai, domin lokaci ya yi da za a kawo ƙarshen wannan masifar tsaro da ta addabi yankinmu.

A ƙarshe, ina addu’a ga Allah Madaukakin Sarki Ya jikan hakimin da aka kashe, Ya ba iyalansa da al’ummarsa juriya, Ya kuma dawo da zaman lafiya mai ɗorewa ga Najeriya baki ɗaya.

✍️ Rubutawa:
Comr. Haidar H. Hasheem
National Chairman, Arewa Media Writer’s

Hotunan Yadda Ƙaramar hukumar Malumfashi ta gudanar da taron rantsar da mutum 85 masu bada shawara da mataimaka na musam...
15/09/2025

Hotunan Yadda Ƙaramar hukumar Malumfashi ta gudanar da taron rantsar da mutum 85 masu bada shawara da mataimaka na musamman a gomnatin ƙaramar hukumar ta Malumfashi

YANZU-YANZU: An Cimma Yarjejeniyar Sulhu Tsakanin Al’umma Da Ƴan Bindiga A Faskari, Jihar KatsinaRahotanni daga ƙaramar ...
14/09/2025

YANZU-YANZU: An Cimma Yarjejeniyar Sulhu Tsakanin Al’umma Da Ƴan Bindiga A Faskari, Jihar Katsina

Rahotanni daga ƙaramar hukumar Faskari da ke Jihar Katsina sun tabbatar da cewa an kulla zaman sasanci tsakanin al’ummar yankin da wasu daga cikin ƴan bindiga da ke addabar yankin tsawon lokaci.

Wannan yarjejeniya ta samu ne a yayin wani zama na musamman da aka gudanar, inda aka cimma matsaya cewa ƴan bindigar za su daina kai hare-hare ko cutar da al’umma, amma za su rika shigowa gari don gudanar da rayuwar yau da kullum cikin lumana.

Wannan mataki ya zo ne bayan dogon lokaci na tashin hankali da kashe-kashe da garkuwa da mutane da aka sha fama da su a yankin, wanda hakan ya tilasta wasu al’umma barin muhallansu.

Yayin da wasu ke kallon wannan mataki a matsayin nasara da ci gaba wajen dawo da zaman lafiya, wasu na nuna damuwa kan amincewa da ’yan bindiga su shiga gari ba tare da an hukunta su ba.

Ana sa ran hukumomi za su ci gaba da sa ido kan yarjejeniyar tare da daukar matakin da ya dace don tabbatar da dorewar zaman lafiya a yankin.

Al'umma A Jihar Imo Sun Yiwa El'rufai Tofin Alatsine, Sun Yi Watsi Da Shi Tare Da Nuna Ƙyma Da Irin SiyasarsaDaga Abdul-...
09/09/2025

Al'umma A Jihar Imo Sun Yiwa El'rufai Tofin Alatsine, Sun Yi Watsi Da Shi Tare Da Nuna Ƙyma Da Irin Siyasarsa

Daga Abdul-Azeez Suleiman

Nasir El-Rufai, tsohon gwamnan Kaduna, ya gamu da zanga-zangar ƙin karɓarsa a Owerri, Jihar Imo, lokacin da ya halarci Taron Odenigbo 2025 a Assumpta Cathedral. Jama’a sun fito da kwalaye da ƙorafe-ƙorafe, suna zarginsa da kalaman wariya kan kabilar Igbo a baya.

Wannan martani bai tsaya kan shi kaɗai ba, ya kuma fito da tsohuwar matsalar rashin haɗin kai, raunin Yaƙin Basasa, da kuma gajiyar jama’a ga shugabannin da ake ganin sun rabu da halin rayuwar talakawa.

Masu zanga-zangar har sun yi kira ga a tsawatar wa Peter Obi saboda kusancinsa da shi, abin da ya nuna cewa kowane ɗan siyasa na iya fuskantar tambaya muddin yana da alaƙa da mutanen da ake kallon masu raba kan ƙasa.

Zanga-zangar ta zama alamar cewa jama’a na da ƙarfi wajen kalubalantar manyan ‘yan siyasa, musamman a wannan zamani na kafafen sada zumunta. Darasin da ke ciki shi ne shugabanni su daina rarrabuwar kawuna, su rungumi tattaunawa, su girmama tarihi, domin kawai haka za a samu haɗin kan ƙasa mai bambance-bambance.

Jama’a Sun Yi Masa Watsi, Sun Nuna Ƙiyayya da Siyasar Rarrabuwar irin ta El'rufai, sun kuma shawarci Peter Obi da ya gaggauta nesanta kansa da El'rufai don tsira da mutuncinsa.

Rashin Tsaro: Lokaci Yayi Da Gwamnati Za Ta Ɗauki Matakan Gaggawa Kan Matsalar Tsaro A Arewa ~ Cewar Shugaban Kungiyar M...
30/08/2025

Rashin Tsaro: Lokaci Yayi Da Gwamnati Za Ta Ɗauki Matakan Gaggawa Kan Matsalar Tsaro A Arewa ~ Cewar Shugaban Kungiyar Marubutan Arewa

Shugaban ƙungiyar marubutan Arewa a kafafen sadarwar zamani Arewa Media Writer, Comr Haidar H. Hasheem, yayi kira da kakkausar murya ga gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro da gwamnatin jahohi da su dauki matakan gaggawa da na dindindin wajen kawo karshen matsalar tsaron da ta addabi al’ummar Arewa musamman a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da sauran sassa na Arewacin Najeriya.

Shugaban ya nuna matuƙar damuwa kan yadda yan ta’adda ke ci gaba da kai hare-hare cikin ƙauyuka, suna kashe mutane a masallatai, suna sace jama’a tare da ƙona gidaje da dukiyoyi. Wannan lamari ya jefa dubban mutane cikin tsananin fargaba, barin garuruwansu da kuma rasa amincewa ga gwamnati da hukumomin tsaro.

Ya k**ata gwamnati ta fahimci cewa tsaron ƙasa ba abu ne da za a siyasantar da shi ba. Tsaro shi ne ginshikin ci gaban kowane al’umma, don haka wajibi ne a ɗauki matakin gaggawa domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a. Rashin yin haka na iya sa al’umma su rasa kwarin gwiwar dogaro ga gwamnati.

Kare rayukan al'umma wajibi ne ga gwamnatin kasa, haka kuma ya k**ata ita gwamnati ta samarwa da jami'an tsaro kayan aiki na zamani tare da basu ƙarfin gwiwa wajen daƙile matsalolin tsaron da ake fama da su.

A madadin al’ummar Arewa baki ɗaya, da marubutan Arewa muna kira ga shugabanni a kowane mataki da su yi tsayuwar daka wajen ganin cewa an kawo karshen wannan matsalar tsaron da ta yi katutu a Arewa.

A ƙarshe, ina roƙon Allah Madaukakin Sarki Ya kawo ƙarshen wannan fitina, Ya ba Najeriya da Arewa zaman lafiya da tsaro nagari.

Rubutawa ✍️
Comr Haidar H. Hasheem
National Chairman, Arewa Media Writer's

ALHAMDULILLAH YANZU-YANZU: Jami'an tsaron ƴan sanda dake Malumfashi sunyi nasarar kwato dukka mutane 3 da ƴan ta'adda s*...
30/08/2025

ALHAMDULILLAH

YANZU-YANZU: Jami'an tsaron ƴan sanda dake Malumfashi sunyi nasarar kwato dukka mutane 3 da ƴan ta'adda s**a ɗauka a garin Marabar Ƙanƙara daren jiya.

Jinjina ga jami'an tsaron haƙiƙa wannan ba karamar nasara bace, muna masu kara maku addu'a da fatan Allah Ubangiji ya ƙara baku sa'ar kawar da duk wani ɗan ta'addan dake a lungu da saƙon ƙaramar hukumar Malumfashi.

~ Kamala Bala Kamalancy

25/08/2025

Daga bakin mutana gidan mantau dake ƙaramar hukumar Malumfashi jihar Katsina.

Yanzu-Yanzu: An Hango Ƴan Majalisar Tarayya Dana Wakilai Na Jihar Katsina Sun Nufi Shalkwatar Tsaro Ta Ƙasa Dake Abuja.....
22/08/2025

Yanzu-Yanzu: An Hango Ƴan Majalisar Tarayya Dana Wakilai Na Jihar Katsina Sun Nufi Shalkwatar Tsaro Ta Ƙasa Dake Abuja....

Duk Sati Uku Sai An Yi Man Allurar Naira 250,000 - Malam Nata'ala na Daɗin Kowa Jarumin Kannywood  Mato-na-mato, wanda a...
17/08/2025

Duk Sati Uku Sai An Yi Man Allurar Naira 250,000 - Malam Nata'ala na Daɗin Kowa

Jarumin Kannywood Mato-na-mato, wanda aka fi sani da Malam Nata'ala na shirin Daɗin Kowa yana fama da rashin lafiyar ciwon Daji (Cancer), wanda ya kwashe sama da shekara yana fama da wannan cutar.

Sai dai yau an hango wani bidiyo da yake bayyana yadda lalurar ke ci gaba da ƙara ta'azzara, inda ya ce duk Sati uku sai an yi masa allurar Naira 250,000, kuma zai kwashe kimanin watanni 6 yana karɓar kulawa.

Hakazalika ya roƙi al'umma da su taimaka masa, sak**akon ƙarfinsa ya ƙare, sannan ya gode wa masu taimakonsa, da kuma neman yafiya ga duk wanda ya yi wa laifi.

Matashi Ɗan Garin Malumfashi Mubarak Aminu M**s Ya Yi sujjadar Godiya Ga Allah, Bayan Ya Kammala Karatu Da Sak**ako Mafi...
16/08/2025

Matashi Ɗan Garin Malumfashi Mubarak Aminu M**s Ya Yi sujjadar Godiya Ga Allah, Bayan Ya Kammala Karatu Da Sak**ako Mafi Daraja (First Class) A Jami'ar Bayero Dake Kano

Matashi Mubarak Aminu, shine dalibi na farko da ya fara fita da sak**akon First Class a bangaren kimiyyar gine-gine.

Daga Kamala Bala Kamalancy

Sarakuna Ku Girmama Matsayinku: Ku Fice Daga Rikicin Jam’iyyar ADC, Ku Bar Malam Nafi’u Bala Gombe Ya Cigaba Da Aikin Gy...
02/08/2025

Sarakuna Ku Girmama Matsayinku: Ku Fice Daga Rikicin Jam’iyyar ADC, Ku Bar Malam Nafi’u Bala Gombe Ya Cigaba Da Aikin Gyara Jam’iyya Cikin Gaskiya

Ofishinmu na Shugaban rikon kwarya na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) yana bayyana damuwarsa matuka kan yadda wasu sarakunan gargajiya ke kiran waya da nufin matsin lamba ga Shugaban rikon kwarya na jam’iyyar, Alhaji Nafiu Bala Gombe, domin ya sauya matsayinsa na kare tsarin dimokuradiyya da doka na jam’iyyar.

Wannan barazana da kuma kiran da ake yi ga wasu mambobin Kwamitin Zartaswa na Kasa (NWC) domin su ja da baya daga goyon bayan shugabansu, abin takaici ne kwarai, musamman ganin cewa sarakuna sun bar turbarsu ta raya al’adu da zaman lafiya, sun rungumi muradin wasu 'yan siyasa masu son karbe jam’iyya ta kowane hali.

MAKIRCI NA BAYA-BAYAN NAN

Bayanan sirri daga majiya mai karfi na nuni da cewa wasu manyan ’yan siyasa da s**a hada da Janar David Mark da Mallam Nasir El-Rufai da wasu gungun mutane sun hada wata kungiya da ke shirin tura dattawa su je Gombe domin matsawa mahaifiyar Shugaban rikon kwarya da nufin tilasta masa mika jam’iyyar da nufin cinma burinsu na siyasa a shekarar 2027.

Wannan yunkuri na ziyarar mahaifiyar Shugaban jam’iyyar abu ne da ba za mu lamunta da shi ba. Hakan na nuna cewa wasu sun sadaukar da dimokuradiyya ga son zuciya da yin coge don biyan muradinsu na 2027.

1. Muna da tabbaci daga bayanen sirri masu inganci cewa wadannan sarakuna na kokarin tilasta Alhaji Nafiu Bala Gombe ya mika jam’iyya ga 'yan siyasa masu matasanancin kwadayin mulki ta hanyar matsa masa da kiraye-kiraye a wayarsa tare da shisshigi a boye. Wadannan sarakuna ba su kyauta ba, saboda suna neman rage kima da martabar al'adunmu masu nagarta ta hanyar neman zama 'yan koren masu mayatar son mulkin siyasa a shekarar 2027. Wannan abin jimami ne ga dukkan mai kishin martabar masarautinmu.

2. Wannan kuskure ne mai muni daga bangaren sarakuna, wadanda ya k**ata su tsaya a gefe su kasance iyayen kasa masu kima.

3. Mu na kara fayyacewa: Sarakuna ba su da hurumin shiga harkokin jam’iyyar ADC ko zama 'yan gada-gadar 'yan siyasa. Wannan ba shekarar 1983 ba ce; yanzu idon kowa a bude yake. ADC ba ta sayarwa ba ce!

4. Alhaji Nafiu Bala Gombe ba zai ja da baya ba, yana da cikakken goyon bayan dokokin jam’iyya da mambobinta masu kishin kasa.

5. Wadanda suke fakewa da cewa suna hidimar “sasantawa”, yaudarar jama'a suke, da nufin biyan muradin 'yan cogen Hadaka ta Zaben 2027. Su sani cewa za mu bayyana sunayensu da cikakken bayani game da boyayyiyar manufarsu, in bukatar yin hakan ta taso.

6. Ga wadanda suke matsayin sarakuna amma s**a tsunduma siyasa da goyon bayan hargitsi, muna ba ku shawara: ku koma ku kula da masarautunku. Kada ku sayar da martabarku da al'adunmu masu nagarta don biyan bukatun 'yan siyasan da s**a shahara wajen yaudarar al'umma shekara da shekaru.

MATSAYARMU A KAN WANNAN KATSALANDAN:

Jam’iyyar ADC ba ta sayarwa ba ce. Ba za mu bar makircin wasu mayaudaran 'yan siyasa ya kassara mulkin dimokuradiyyan kasar nan ba, ko ya lalata alkiblar jam’iyyar ADC ba. Kuma za mu fallasa kowane mai hannu a ciki — ko saraki ne shi ko dan bangar siyasa.

In kunne ya ji, jiki ya tsira.

Sanya hannu:
Dr. Aminu Sani Alhassan
Mai Baiwa Shugaban Rikon Kwarya Shawara kan Harkokin Jama’a
Jam'iyyar African Democratic Congress (ADC)
Abuja

Address

Malumfashi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Malumfashi Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category