Kamalancy

Kamalancy Kamalancy sabon shafin jarida ne da aka kirkira dan kokarin kawo maku sabbin kayatat'tun labaran Dun

An Jaddada Jagoranci Nagari Da Yaƙi Da Shan Miyagun Ƙwayoyi a Babban Taron Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya "CNG" a...
16/01/2026

An Jaddada Jagoranci Nagari Da Yaƙi Da Shan Miyagun Ƙwayoyi a Babban Taron Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya "CNG" a Sakkwato

Ƙungiyar Coalition of Northern Groups (CNG) ɓangaren ɗalibai ta samu gagarumar nasara wajen shirya laccar bai ɗaya da aka gudanar a Kwalejin Ilimi ta Shehu Shagari da ke Sakkwato.

An gudanar da laccar ne ƙarƙashin jagorancin Mai Martaba HRH Farfesa Sambo Wali Junaid (Wazirin Sakkwato), inda manyan masu jawabi s**a yi jawabai masu armashi kan batutuwa masu muhimmanci da s**a shafi kyakkyawan jagoranci nagari, illolin shan miyagun kwayoyi, da kuma mummunan tasirin "Hate speech" a makarantun gaba da sakandare da ma al’umma baki ɗaya.

Taron ya samu halartar ɗalibai masu yawa daga fannoni daban-daban, abin da ke nuna yadda matasa ke da ƙwazo da sha’awar rungumar kyawawan ɗabi’u, haɗin kai da jagoranci nagari.

Hakika, laccar ta ilmantarwa ta kuma yi tasiri sosai, inda ta haɗa zukatan matasa masu burin gina kyakkyawar makoma mai ɗorewa da ci gaban al’umma.

Masu Yaɗa Ƙarya Akan Gwamnan Bauchi Ba Za Ku Yi Nasara Ba!Muna jan hankalin jama’a game da wani labari na ƙarya da ake y...
07/01/2026

Masu Yaɗa Ƙarya Akan Gwamnan Bauchi Ba Za Ku Yi Nasara Ba!

Muna jan hankalin jama’a game da wani labari na ƙarya da ake yaɗawa a kafafen sada zumunta, wanda ake zargin cewa an bai wa wata ƙungiya da ake alaƙantawa da ta’addanci kuɗi daga Gwamnatin Jihar Bauchi. Wannan labari ba shi da tushe, b***e Malama, babu hujja, kuma ƙarya ce tsagwaronta.

Babu wani lokaci da Gwamnatin Jihar Bauchi, ko Mai Girma Gwamna Sanata Bala Abdulkadir Mohammed, ya amince ko ya ba da umarnin bai wa kowace ƙungiya da ke da alaƙa da ta’addanci kuɗi, ko ta kowace hanya. Wannan zargi an ƙirƙire shi ne kawai domin ɓata suna, yaudarar jama’a, da tayar da fitina.

Muna kira ga jama’a da su yi watsi da irin waɗannan labaran ƙarya, su kuma guji yaɗa bayanan da ba su tantance ba. Gwamnatin Jihar Bauchi ta himmatu wajen tabbatar da tsaro, zaman lafiya, da bin doka da oda, tare da haɗin gwiwa da hukumomin tsaro na ƙasa.

Duk wanda ke yaɗa wannan labari na ƙarya, yana da niyyar ɓata sunan shugabanci da ya samu amanar jama’a, kuma hakan ba zai hana gwamnati ci gaba da ayyukan alheri da ci gaban jihar Bauchi ba.

Gaskiya ce za ta yi nasara a kowane lokaci.

Kungiyar Arewa Media Writers Ta Yi Kira Ga Shugaba Tinubu Da Ya Gaggauta Sauke Ministan Abuja, Nyesom Wike…Kungiyar ta c...
06/01/2026

Kungiyar Arewa Media Writers Ta Yi Kira Ga Shugaba Tinubu Da Ya Gaggauta Sauke Ministan Abuja, Nyesom Wike

…Kungiyar ta ce dole ne a dakatar da duk wani yunkuri da ke barazana ga dimokaradiyya, zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.

Daga Kungiyar “Arewa Media Writers”

Kungiyar Marubutan Arewa "Arewa Media Writers" ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙungiyar na Ƙasa, Comr. Haidar H. Hasheem (Kano), ta nuna matuƙar damuwa tare da yin Allah-wadai da abin da ta bayyana a matsayin k**a-karya, nuna wariya da cin zarafin ‘yan ƙasa, da ake zargin Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, na aikatawa.

Kungiyar ta ce abin takaici ne yadda ake zargin Ministan da amfani da ƙarfin iko wajen cuzgunawa ‘yan Arewa da ‘yan adawa, musamman saboda banbancin ra’ayin siyasa, abin da hakan ke tauye ‘yancin ‘yan ƙasa tare da zama barazana ga tsarin dimokaradiyyar Najeriya.

A cewar ƙungiyar, ana zargin Wike da amfani da hukumar EFCC da jami’an tsaro wajen tsoratarwa da musgunawa abokan hamayya, lamarin da ke haifar da fargaba, rashin adalci da rashin amincewa ga hukumomin gwamnati.

Kungiyar Arewa Media Writers ta kuma nuna damuwa kan yadda Ministan ke yin furuci da ayyuka masu ɗauke da wariya ga al'ummar Hausawa/Fulani, inda ta jaddada zargin da Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad, ya yi a baya-bayan nan, wanda yace ya samu wata masaniya daga mai jiya mai tushe dake nuna cewa hatta hukumomin EFCC, Wike ke amfani da su wajen matsin lamba ga yan adawa, haka kuma ya tabbatar dasa hannun Ministan wajen ƙoƙarin bata masa suna ta hanyar jingina shi da zargin ɗaukar nauyin ta’addanci a kotu.

Kungiyar ta bayyana cewa irin waɗannan zarge-zarge ba komai ba ne illa kiyayya ta kabilanci da siyasar adawa, wanda hakan ya saba wa ruhin haɗin kan ƙasa. Idan baku manta ba tun a lokacin da Wike ke Gwamnan Jihar Rivers, an samu rahotannin rusa masallatai, rufe shaguna da gidajen ‘yan Arewa, tare da korar su daga jihar, abin da har yanzu ke ci wa zukatan al’umma tuwo a ƙwarya.

Haka kuma ƙungiyar ta yi tsokaci kan sauke Sakataren Ilimi na Abuja, Dr. Danlami, wanda ɗan Arewa ne, inda ta ce yadda aka yi hakan ya ƙara nuna amfani da iko ba bisa ƙa’ida ba, tare da mayar da shi aiki bisa wasu sharudda.

Ba wannan kaɗai ba, kungiyar ta kuma nuna damuwa kan zargin amfani da jami’an tsaro wajen tarwatsa rikici a helkwatar jam’iyyar PDP, inda aka ce har aka yi amfani da hayaki mai sa hawaye ga wasu gwamnoni ciki har da Seyi Makinde da Bala Muhammad, lamarin da bai dace ba ga shugabanni da kundin tsarin mulki ya tanadar musu da rigar kariya.

Kungiyar Arewa Media Writers ta jaddada cewa tsarin shugabancin Najeriya bai ginu kan kabilanci, wariya ko ramuwar siyasa ba, illa adalci, daidaito da mutunta ‘yancin kowa.

A ƙarshe, Kungiyar Arewa Media Writers tana kira ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya gaggauta dakatar da duk wani yunkuri da ke barazana ga dimokaradiyya Najeriya, taka wa Ministan Abuja burki, ko kuma a sauke shi daga mukaminsa, domin kare martabar dimokaradiyya, zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.

Arewa Media Writers za ta ci gaba da tsayawa kan gaskiya, adalci da kare haƙƙin al’umma.

✍️✍️
Comr Nura Siniya
Chairman Arewa Media Writer's Katsina Chapter

GWAMNAN JIHAR BAUCHI YA FALLASA ASIRIN MINISTAN ABUJA NYESOM WIKEMaigirma Gwamnan jihar mu na Bauchi Senator Bala Abdulk...
02/01/2026

GWAMNAN JIHAR BAUCHI YA FALLASA ASIRIN MINISTAN ABUJA NYESOM WIKE

Maigirma Gwamnan jihar mu na Bauchi Senator Bala Abdulkadir Mohammed (Kauran Daular Usmaniyyah) ya fallasa asiri na makircin da Ministan Abuja Nyesom Wike yake kulla masa da jihar Bauchi gaba daya

Maigirma Gwamna yayi wannan fallasa ne a cikin shirin Sunrise Daily na Channels TV dazu da safe, yace akwai wanda yake shirya min makirci, kuma na san shi, shine Ministan Abuja na yanzu Nyesom Wike, ya fada wa duniya cewa zai kunna wuta a jihata na Bauchi

Kauran Daular Usmaniyyah yaci gaba da cewa; na fahimci Wike ne yake bada umarni wa hukuma irin na EFCC wajen batani, yana bawa mutane cin hanci, yana sayar da filayen Abuja yana amfani dasu wajen cimma burinsa, ba sabon abu bane a gareni saboda na taba rike mukamin Ministan Abuja na shekaru 6 na san komai

Gwamnan Bauchi yaci gaba da cewa; yana da hujjoji daga majiyarsa na sirri dake EFCC wanda s**a tabbatar masa da cewa Wike ne yake tsara duk abinda yake faruwa da ‘yan adawar siyasa a Nigeria

Kaura yace tsohon Accountant General dinsa na jihar Bauchi yaci amanata, ni na kaishi Kotu da kaina domin a masa hukunci, daga bisani Kotu ta bada belinsa, to a yanzu Wike ne yake aiki dashi a Kotu wajen bada shaida na karya akan mukarrabaina da aka k**a

A matsayina na Gwamna wanda na rike manyan muk**ai tun daga Sanata har Minista, ina shugaban al'ummah ta ya zai kasance ina daukar nauyin ta'addanci, ana min wannan sharri ne saboda ina cikin manyan 'yan adawa

Zan bi duk matakan da s**a dace domin na kare kaina, na rubuta wa Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya takardan korafi, tare da sanar da hukumomin tsaro, kuma zan kai korafina zuwa ga hukumonin Majalisar dinkin duniya, inji Maigirma Gwamna

Sannan Gwamna Bala yace Shugaban Kasa Tinubu yana kewaye da 'yan daba, 'yan damfara wadanda suke son ha||akashi a siyasance irinsu Wike

Muna rokon Allah Ya kare jihar Bauchi daga wadanda suke neman jingina mana ta'addanci, Allah Ya sa mugun nufinsu ya kare a kansu da iyalansu kadai.

DA ƊUMI-ƊUMI: An Kaddamar Da Kungiyar 'TAFIDA YOUTH ORG FOR DIKKO 2X' a Karamar hukumar Dandume.Ranar Juma'a 26/12/2025 ...
27/12/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: An Kaddamar Da Kungiyar 'TAFIDA YOUTH ORG FOR DIKKO 2X' a Karamar hukumar Dandume.

Ranar Juma'a 26/12/2025 Aka Kaddamar Da Shuwagabannin Ƙungiyar 'TAFIDA YOUTH ORG FOR DIKKO 2X' reshen Karamar hukumar Dandume jihar Katsina Karkarshin jagorancin Alhaji Ibrahim Shuaibu (Tafidan Dandume), Kuma Shugaban Kamfanin (SHIAGRO Nigeria Limited) Fitaccen Matashi, Dan Kasuwa Dan Asalin jihar Katsina.

Manufar Kungiya shine Tallata Manufofi da ayyukan maigirma Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD. CON. (Gwagwaren Katsina) a lungu da saqon Jihar katsina, Domin wayarda kan alumma akan abubuwan alkhairi da maigirma Gwamna yakeyi ma alummar jihar katsina daga nan harzuwa lokacinda za'a sake rantsardashi a matsayin Gwamna karo na biyu insha Allah.

A cewar shuwagabannin kungiyar 'Kamar yadda s**ara qaddamarwa a Karamar Hukumar Dandume Haka zasu cigaba dayi a dukkan kananan Hukumomin jihar katsina Talatin da Hudu 34LGAs cikin wadannan lokutan In Shaa Allah, Domin tabbatar da nasarar gwamna Radda a shekara 2027"

Taron Ya samu halartar wakilan kungiyar daga gundumimi 11 dake karamar hukumar Dandume da matasa maza da mata yan gwagwarmaya siyasa.

~Karaduwa Post

Wani Ɗan majalisa a jihar Kaduna ya sha dakyar yayin da al,ummar da yake wakilta s**a tarfa shi da bugu sak**akon ya sha...
25/12/2025

Wani Ɗan majalisa a jihar Kaduna ya sha dakyar yayin da al,ummar da yake wakilta s**a tarfa shi da bugu sak**akon ya shafe wata 9 rabon da yaje yankin nasa.

Wajen gudun tsira daga hannun al,ummar mazabar tasa ne dai dan majalissar har ya bar hula da takalmin sa da rana tsaka k**ar yanda kuke gani a cikin hotuna.

Me zaku ce ?

‎RAYUWA BA TABBAS: Kwana 2 Ya Rage Aurenta Rai Yayi Halinsa.😭😭‎‎Wata Budurwa Mai Suna Hajara Umar Lumus Daga Jihar Nassa...
25/12/2025

‎RAYUWA BA TABBAS: Kwana 2 Ya Rage Aurenta Rai Yayi Halinsa.😭😭

‎Wata Budurwa Mai Suna Hajara Umar Lumus Daga Jihar Nassarawa, Ta Rasu Yau Sak**akon Hatsarin Mota, Bayan Da Ake Ta Shirin Aurenta A Ranar Asabar Ɗinnan Ta 27 Ga Watan Disamba,

~ Kamala Bala Kamalancy

Matasa Daga Arewacin Najeriya Sun Bukaci Tinubu Ya Sallami Ministan Tsaro Bello MatawalleƘungiyar Northern Christian You...
19/12/2025

Matasa Daga Arewacin Najeriya Sun Bukaci Tinubu Ya Sallami Ministan Tsaro Bello Matawalle

Ƙungiyar Northern Christian Youth Coalition (NCYC) ta bukaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya sallami Ministan Ƙasa na Tsaro, Dr. Bello Muhammed Matawalle, sak**akon zarge-zargen da suke nuna cewa yana da alaƙa da ta'addanci wanda tsohon hadiminsa Musa Kamarawa yayi ikirari.

A cikin wata sanarwa da Babban Kwamishinan ƙungiyar, Jeremaid Hudso Bako, ya fitar, ƙungiyar ta ce kira da take yi na nufin ƙarfafa gaskiya, riƙon amana, da dawo da amincewar jama’a ga gwamnati, musamman a bangaren tsaro.

Ƙungiyar ta yaba wa Shugaba Tinubu kan tsige tsohon Shugaban Hukumar NMDPRA, Farouk Ahmed, tana mai cewa hakan alama ce ta ƙoƙarin gwamnati wajen yaƙi da cin hanci da rashawa. Sai dai ta ce ya dace a yi adalci iri ɗaya ga kowa, ciki har da Matawalle.

NCYC ta jaddada cewa zarge-zargen da ake yi wa Matawalle suna da nauyi sosai, musamman ganin cewa suna da alaƙa da tsaron ƙasa da rayukan al’umma, don haka bai dace a yi shiru a kansu ba.

Ƙungiyar ta ce idan har gwamnatin Tinubu na son a san ta da gaskiya, adalci da shugabanci nagari, to ya zama dole ta ɗauki mataki cikin gaggawa kan duk wani jami’i da ake zargi da aikata abubuwan da za su iya lalata amincin ƙasa tare da sauke ƙaramin ministan da kuma gudanar da binciken gaggawa a kansa.

Odua People’s Assembly Ta Nemi Gwamnati Ta Gudanar Da Bincike Gaggawa Kan Matawalle....Zargin alaƙa da ‘yan bindiga bara...
16/12/2025

Odua People’s Assembly Ta Nemi Gwamnati Ta Gudanar Da Bincike Gaggawa Kan Matawalle
....Zargin alaƙa da ‘yan bindiga barazana ce ga tsaron Najeriya.

Ƙungiyar Odua People’s Assembly (OPA) ta nuna damuwa matuƙa kan zargin da ake yi wa Ministan Tsaron Ƙasa (State), Bello Matawalle, dangane da alaƙa da ‘yan bindiga. Ƙungiyar ta ce zargin yana da hatsari ga tsaron ƙasa da amincewar jama’a.

OPA ta buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta gudanar da bincike mai zaman kansa, tare da sanya gaskiya kuma ba tare da son kai ba, domin fayyace gaskiyar lamarin. Ta ce rashin daukar mataki zai ƙara raunana amincewar jama’a da hukumomin gwamnati, musamman a lokacin da Najeriya ke fama da matsanancin matsalar tsaro.

Ƙungiyar ta ce bayyanar wani bidiyo da ke nuna Bello Turji, shugaban ‘yan bindiga, yana kare Matawalle abin tayar da hankali ne, domin yana nuna yiyuwar haɗin kai tsakanin jami’an gwamnati da masu laifi.

OPA ta bayyana cewa duk wata alaƙa, kai tsaye ko a kaikaice, tsakanin jami’an gwamnati da ‘yan bindiga cin amanar ‘yan Najeriya ne, musamman waɗanda s**a sha wahala sak**akon rashin tsaro.

A matsayin mataki na dawo da amincewar jama’a, OPA ta buƙaci a sauke Matawalle daga muƙaminsa nan take, tare da kafa cikakken tsari na bincike mai zaman kansa. Ta kuma gargadi cewa rashin daukar mataki mai tsauri zai ƙarfafa ‘yan bindiga tare da ƙara ta’azzara rashin tsaro.

Ƙungiyar ta bukaci ‘yan Najeriya su kasance masu faɗakarwa, su kuma riƙa kira ga alhakin shugabanni, tana jaddada cewa yaƙi da ‘yan bindiga ya zama na bai ɗaya, ba tare da la’akari da siyasa ko yanki ba.

Sa Hannun
Sunday Daniel
Mai magana da yawun Odua People’s Assembly

Yak**ata Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Kwamitin Bincike Na Gaggawa Kan Zargin Alaƙa Da Yan Bindiga Da Musa Kamarawa Yayi Ga ...
15/12/2025

Yak**ata Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Kwamitin Bincike Na Gaggawa Kan Zargin Alaƙa Da Yan Bindiga Da Musa Kamarawa Yayi Ga Bello Matawalle
.... Dole a gaggauta binciken Musa Kamarawa da kuma Ƙaramin Ministan Tsaron kan alaƙa da yan bindiga domin tabbatar da tsaron al'ummar Arewacin Najeriya.

Ni, Comr. Haidar H. Hasheem, ɗan Arewa kuma mai kishin zaman lafiya da tsaron ƙasa, ina bayyana damuwa mai tsanani kan manyan zarge-zargen da ke yawo a fili, musamman ikirarin da tsohon mataimaki na musamman ga tsohon Gwamnan Zamfara, Musa Kamarawa, ya yi a faifan bidiyo dangane da Ministan Tsaron Ƙasa na yanzu, Bello Matawalle.

Waɗannan zarge-zarge sun haɗa da alaƙa da ’yan bindiga, zargin tura kuɗaɗe ga fitaccen shugaban ’yan bindiga Bello Turji, sayen motocin Hilux ga yan ta'adda, da kuma tallafawa da dukiya k**ar gidaje, saya musu dusa da sauran kayan more rayuwa, tare da zargin cewa wasu ’yan siyasa daga Zamfara da maƙwabtanta sun taka rawa a hakan.

Waɗannan ba ƙananan maganganu ba ne. Zarge-zarge ne masu nauyi da ke nuna yiwuwar alaƙa mai zurfi tsakanin wasu masu rike da madafun iko da ’yan bindiga, abin da ke iya rushe ƙoƙarin jami’an tsaro tare da ƙara jefa rayukan al’umma cikin haɗari.

Ina da cikakken ra’ayi cewa musantawa kawai ba za ta wadatar ba. Idan ba a yi cikakken bincike ba, shakku zai ci gaba da ƙaruwa, kuma amincewar jama’a ga gwamnati da hukumomin tsaro za ta ƙara raguwa.

Haka kuma, matakin kai ƙara kan Sheikh Murtala Asada yana iya fassaruwa a idon jama’a a matsayin yunƙurin tsoratarwa da hana faɗin gaskiya, maimakon kare mutunci. Ina kira ga Sheikh Asada da ya fito da duk wata hujja da ke hannunsa, domin gaskiya ita ce ginshiƙin adalci, haka kuma bayyana dukkan gaskiyarsa gaban kotu zai taimaka don tabbatar da kare tsaron ƙasa.

A bayyane yake cewa babu wanda ya fi ƙarfin doka, kuma duk wani yunƙurin kare masu hannu a ta’addanci yana raunana tsaro tare da cin zarafin mutanen Arewa da Najeriya baki ɗaya.

Saboda haka, ina kira da a gaggauta kafa bincike mai zaman kansa, marar son zuciya, wanda Majalisar Ƙasa, hukumomin tsaro, da Ofishin Babban Lauyan Ƙasa za su jagoranta, domin binciken kuɗaɗe, kayan aiki, sadarwa da duk wata hulɗa da ka iya taimaka wa ’yan bindiga.

Dole ne a kare masu fallasa gaskiya, kuma duk jami’in gwamnati da aka samu da laifi ya fuskanci hukunci ba tare da la’akari da matsayinsa ko ƙarfin ikonsa ba.

Arewa ta sha wahala ƙwarai sak**akon ’yan bindiga. Wannan lokaci ne na fuskantar gaskiya, ba na ɓoyewa ba. Lokacin shiru ya wuce. Lokacin gaskiya, adalci da ɗaukar mataki ya yi.

Ɗan'uwanku
Comr. Haidar H. Hasheem
Ɗan Arewa Mai Kishin Tsaro Da Tabbatar Da Adalci

Dole A Gaggauta Binciken Ƙaramin Ministan Tsaro Kan Zargin Alaƙa Da Yan Bindiga ~ Cewar CNG..... Gamayyar Kungiyoyin Are...
14/12/2025

Dole A Gaggauta Binciken Ƙaramin Ministan Tsaro Kan Zargin Alaƙa Da Yan Bindiga ~ Cewar CNG
..... Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya Ta Buƙaci A Gaggauta Bincike Mai Zurfi Kan Zargin Da Ake Yiwa Matawalle Da Alaƙa Da Yan Bindiga

Ƙungiyar Coalition of Northern Groups (CNG) ta bayyana damuwa mai tsanani kan ikirarin da Musa Kamarawa, tsohon mataimaki na musamman ga tsohon Gwamnan Zamfara kuma Ministan Tsaron Ƙasa na yanzu, Bello Matawalle, ya yi a wani faifan bidiyon da yake nuna Matawallen na da alaƙa da tallafawa yan bindiga.

CNG ta ce zargin ya shafi tura kuɗi kai tsaye ga fitaccen shugaban ‘yan bindiga Bello Turji, sayen motocin Hilux da dama ga ƙungiyoyin ta’addanci, da kuma bayar da tallafin kayan aiki k**ar gidaje, shanu da sauran dukiya, wanda ake zargin ‘yan siyasa daga Zamfara da maƙwabtanta s**a taimaka wajen aiwatarwa.

A cewar CNG, waɗannan ikirari suna nuna yiwuwar alaƙa mai zurfi tsakanin wasu manyan jami’an gwamnati da ‘yan bindiga, lamarin da ka iya rusa ƙoƙarin sojoji tare da ƙara jefa al’umma cikin haɗari.

Ƙungiyar ta ce irin waɗannan zarge-zarge ba za a iya watsi da su ta hanyar musantawa kawai ba, domin hakan na ƙara haifar da shakku cewa ana ɓoye gaskiya.

CNG ta kuma soki matakin Ministan na kai ƙara kan Sheikh Murtala Asada, tana mai cewa hakan na iya zama yunƙurin hana faɗin gaskiya, maimakon kare mutunci. Ta bukaci Sheikh Asada da ya fito da dukkan hujjojin da ke hannunsa ba tare da tsoro ba.

Ƙungiyar ta jaddada cewa babu wanda ya isa ya fi karfin doka, kuma ɓoye masu hannu a ta’addanci na raunana tsaro da amincewar jama’a.

Saboda haka, CNG ta nemi bincike mai zaman kansa, binciken da babu son zuciya, wanda Majalisar Ƙasa, hukumomin tsaro da Ofishin Babban Lauyan Ƙasa za su jagoranta, domin binciken kuɗaɗe, kayan aiki, sadarwa da duk wata shawara da ka iya taimaka wa ‘yan bindiga.

Ta ce dole a kare masu fallasa gaskiya, kuma duk jami’in gwamnati da aka samu da laifi ya fuskanci hukunci ba tare da la’akari da matsayinsa ko ƙarfin ikonsa ba.

CNG ta jaddada cewa Arewa ta sha wahala matuƙa sak**akon ‘yan bindiga, kuma wannan lokaci wata dama ce ta fuskantar tushen matsalar. Kare masu aikata laifi zai lalata makomar tsaro da amincewar jama’a. Lokacin ɓoyewa ya wuce, lokacin gaskiya da adalci ya yi.

Sa Hannun
Comr Jamilu Aliyu Charanchi
National Coordinator CNG

YANZU-YANZU: Sojojin Nigeria sun kashe ‘yan bindiga 4, Sannan sun k**a ɗan sanda da ke aiki da kungiyar 'Yan Bindigar A ...
30/11/2025

YANZU-YANZU: Sojojin Nigeria sun kashe ‘yan bindiga 4, Sannan sun k**a ɗan sanda da ke aiki da kungiyar 'Yan Bindigar A Jihar Taraba.

Me zaku che?

Address

Malumfashi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kamalancy posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Kamalancy:

Share

Category